Skip to content

Chapter 67

Chapter 67

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,245 words 0 views Progress saved
Download Book

zauna a nutse ta had'a dai-dai cikinta tayi bissimilah ta fara ci, duk abunda take yana kallonta ta k'asan idonsa dake mutum ne shi mai yalwar gashin ido shiyasa in ya lumshe idonsa sai kayi tunanin a rufe yake. Mama ce ta futo daga wani d'aki cikin shiri tana sanye da wata lafiyyar lifaya wacce tayi mata kyau sosai, had'a ido sukayi da Balaraba tayi saurin yin k'asa da kanta, Mama Fulani tayi murmushi kunyar yarinyar tana burgeta sosai,tace" Yawwa ko kefa ai gwara da kika fito amma kin zauna cikin d'aki babu ci babu sha" Sunkuyar da kai tayi cikin jin nauyi. Ta kalli su Sadiya sun sake suna wasa,Usuman ta kira tace"Zo muje ka rakani wani guri" Da sauri yaron ya tafi gurinta.Mama ta kalli Balaraba tace"Zamu shiga shashen Hajiya Kattime yanzu" "To Mama a futo lafiya" Balaraba tafad'a cikin girmamawa. Har ta nufi k'ofa sai ta dakata ta juyo tana kallon Balaraba tace "Ki kula da Almustafa,in ya tashi daga baccin ki bashi abunci, na lura kwana biyu yana wasa da cikinsa,duk ya rame" Balaraba tace"Insha Allahu Zanyi Mama,Agaida Hajiya. "Zataji insha Allahu" Mama tafad'a lokacin da take k'okarin futa. Shiru yayi duk yana jin zantukan da sukeyi,har yanzu idonsa a lumshe yake yana kallonta duk abunda take, cin abinci take a nutse har ta kammala,ta goge bakinta, shiru tayi tana tunanin ta yaya za'ayi ta tasheshi daga bacci har ta bashi abunci, dole ne ta cika umarnin da aka bata. Mik'ewa tayi ta nufi inda yake, ganin ta nufo gurinsa yasa ya rufe idon gaba d'aya ta k'araso tayi tsaye kansa tana kallon fuskarsa, tsigar jikinta taji tana tashi ganin wani zallah kyau da annuri da yake futa a fuskarsa, mai d'auke da zara-zaran gashin idon had'e da sanjensa Wanda ya kewaye d'an mitsitsin bakinsa, tsabar hutu da jin dad'i yasa tafarshi tayi wata irin kala, ita ba fara ba ita ba b'aka, hakika Allah yayi hallita a gurin, ko da take farar mace, tayi shawa'ar fatarshi ji take ina ma itace take da Irin fatar. Hannusa ta kalla mai d'auke da zararan zaran yatsu ya d'ora kan cikinsa, tayi saurin kauda kanta tana tunanin ya zatayi ta tashe shi, cikin sa'a d'aya daga cikin wayoyinsa tafara k'ara, yanaji yayi shiru, kallon fuskar wayar tayi, Matata,sunan da tagani yana yawo kan screen ni d'in, katsewa tayi wani kiran ya k'ara shigowa wata zuciyar tace d'auki kiyi magana, kiji wacece,tunda dai ita iya saninta dashi tasan bashi da wata mata, sun kuya tayi zata d'auki wayar yayi saurin dafe wayar da hannusa, hannuwansu suka had'u guri guda. Yarrrrr!! Ya ji a jikinsa sai ya d'amke wayar a hannusa tare da hannuta,ya bud'e idonsa tarr! A kanta sukayi ido hud'u Abunda yasa ya hanata d'aukar wayar shine gudun rigimar Halisa yasan itace saboda ringing din da yasa mata daban ne, yasan taji muryar mace, tashin hankali zasuyi Zare hannuta take k'okarin yi ya rik'e ya had'a da nashi da wayar ya kara a kunne, cikin wani kasalalliyar murya yayi sallama. Tana jiyo muryar Halisa tana fad'in Habibi ganinan shigowa Shashen Mama yanzu na futo shashanka Buba yace baka shigo ba tun da safe, da ka futa" Kamar baya so yace "Sai kin shigo " Kashe wayar yayi yana me kallon hannun Balaraba dake had'e da nashi, babu zato taji yace mene kika tsaya min aka, tun d'azu" _*TSANTSAR BUTULCI*_ *_NA_* _BINTA UMAR ABBALE_ *BINTUBATULA*👄 _Littifi mai dauke da darusa gami da cin amana da iri-iri, kar ku bari a Baku labari_ https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ ________________________ _*We are here to educate,motivate and entertain aur readers*_ ________________________ _*DIDEGATED*_ _*TO*_ ```RAHAMA ALIYU``` _*BISMILLAHI-RAHAMANI-RAHIM*_ *🅿77* Daburcewa tayi, tana k'okarin cire hannuta daga nasa, tace"Mama ce tace ka tashi kaci abunci yanzu" Kallonta yake cikin nutsuwa yace"Mama batace ki tashe ni daga bacci ba, cewa tayi in dan na tashi ki bani,ai duk inajin abunda kuke fad'a" Shiru tayi na minti biyu tace"Hakane, ko da yake dama hakkin ciyar da kai abunci ba akaina yake ba, ga matarka nan sai ta baka" Tana gama fad'ar maganar takama hanya zata wuce,ya rik'e hannuta, yace"Ba ita aka umarta da ta bani abunci ba,ke a ka umarta da ki bani saboda haka,sai ki tsaya ki bani" Cikin sanyi jiki tace"Wai me yasa kake son rik'e min hannu ne, nifa ba muharramar ka bace,abunda kake babu kyau,nasan ka sani kuma kana takewa" Cikin d'an b'acin rai tayi masa maganar. Hannunta ya saki,yana d'an sosa kansa irin na sabo, shi bada wata manufa yake tab'a jikinta,illa kawai irin sabon da Halisa tayi masa,n yawan kusantarsa,duk da yake itama baya wani zak'ewa iya kacinsa da ita ya rik'e mata hannu, ko kuma in zai mata magana ya d'an zungureta daga haka baya k'arawa,itace me zak'ewa da yawa yana tsawatar mata. Ganin ya sakar mata hannu yasa ta wuce can inda kayan abuncin suke ta fara had'a masa lafiyayyan towon shinkafa miyar taushe me d'auke da wadattacen nama,da man shanu, cikin wani had'addan plate ta had'a ta rufe da irinsa ta nufu in da yake zaune. K'asa ya sauko ya jingina jikinsa jikin kujera, tazo ta aje masa ta koma ta d'auko lemo jus ta da ruwan roba nan ta aje kusa dashi, ta mik'e zata bar gurin,gyaran murya yayi a tsanake yace"Dawo ki zauna ki bani kamar yadda aka umarce ki" Cikin Mamaki Balaraba ta juyo tana kallonsa, a dake tace"Ban gane abunda kake nufi ba"? "Ai baki gama aikin ki ba, yafad'a yana kallon k'ofa jin kamar za'a shigo,kafin tayi wani tunani Halisa ta shigo da siririyar sallama taci uwar kwalliya tamkar wata sarauniya, turusss!! Tayi ganin Balaraba kan Habibinta, shi kuma yana kallonta, k'okarin dane abunda taji a zuciyarta tayi ta k'arasa kuda dashi, cikin wata irin tafiyar k'asaita Balaraba kuwa saurin kauda kanta tayi, cikin zuciyarta tana wani irin jin haushin Halisa haka kawai. Ta k'araso ta zauna kusa dashi har kafad'arsu tana gugar juna,cikin tsabar kwarkwasa ta gaishe ya amsa babu yabo babu fallasa, yace" Wannan kwaliyyar da kikayi ni kika yiwa ko kuwa" Cikin jin dad'in yaba kwaliyyarta da yayi tace" Kai nayiwa gwarzon zuciyata me mulkin zuciyata" Wani k'asaitaccan murmushi yayi yana kashe mata ido yace "Nawa ne kud'inta in siya" Fari da ido Halisa tayi tace" Bana buk'atar komai sai so da k'aunarka" Ganin yanda suke hira ta soyyaya sun shareta yasa Balaraba barin gurin da rai a b'ace! Kallo ya bita dashi har ta shige d'akin da take. Ita kuwa Halisa bud'e a abunci tayi ta fara bashi abaki sunayi suna hirar soyyaya ko da wasa bata yi masa zancan Balaraba ba saboda in gargad'in da yayi mata, kwanaki,a zuciyarta tace,kowa tasa ta fisheshi,ita k'okarinta taga ta mallake zuciyarsa ita kad'ai,don haka sai ta k'ara zage damtse tana ta shirya masa hira masu dad'i, sosai ya saki cikinsa yaci abuncin saboda dama neman me d'ebe masa kewa yake,bai samu ba. ******** To Sallau dai da k'yar ya koma gida tare da taimakon Mai gari da d'anshi Walidi,saboda tun a hanya ya jigata sai haki!yake tun lokacin da me Martaba ya fad'a masa cewar Balaraba zatayi aure a gidan shikkenan yaji zuciyarsa

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108