Skip to content

Chapter 14

Chapter 14

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,252 words 0 views Progress saved
Download Book

kai in ci da "yayanka" Bai ce mata komai ba ,ya fizge rigarshi gami da gyara wuyanta in da ta yaga masa,ya sakai ya fice daga gidan babu abinda ya dameshi,can mahadarsu ya nufa,abokanshi na Zane suna ta faman karta! (Caca) nan ya zauna cikinsu a ka fara yi dashi. _ina so Ku fahimci ko wane marubuci da nasa salon,gaskiya ni babu yadda za'ayi in yi rubutu batare da na fadi jogon labari ba ,domin shine ginshin fara karatu, So dan Allah kuyi hakuri kuci gaba da bina a yadda nake za azo in da kuke so_ *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* [04/05, 03:17] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? 🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀ *By* _BINTA UMAR_ *Maman Abdul Wahabu* _ZAMANI WRITES ASSOCIATION_ *🅿23* _Bissimillahi_ To haka rayuwa take, Ayuba ya yi ta fafutukar naman abinda zai rufawa kanshi,asiri ,yayin da "yan uwanshi suka tasa shi a gaba har sai dai suka ga ya kwanta, ba ya iyayin komai da kanshi sai dai ayi masa,gashi lokacin nauyi yayi masa yawa dalili kuwa yayarshi Atika mijinta ya rasu,sai ta dawo gidan ta zauna dakinsu na gado ita da "yan uwanta ,da suke can garinsu ,suna aure,a lokacin Balaraba na da shekara goma sha uku, sai kanwar ta ,wato sadiya, tana da shekara tara,sai qaramin kaninsu Usuman dan shekara bakwai. Sosai Ayuba yake ciwo an rasa gane kan ciwon anyi na asibitin har an hakura ,sai aka dawo yin na hausa,sabida yadda kafarsa guda ta kumbura take fitar da ruwa abin babu dadi , wani mai maganin hausa da yazo ya dubashi ,yace jifansa a kai (Asiri) sabida haka kar a kara yin maganin asibiti domin zai kara rikita ciwon,cikin ikon Allah ya hada magani ya bashi nasha da wanka gami da shafawa, a kafar,sai a ka fara samun saukin abun, domin wani lokacin yakan tashi da kan shi yafito waje yana dafa bango, Tunda yafara wannan ciwon tsakanin Sallau da Lantana da Uwa babu wanda yazo ya duba shi ballan tana yace dashi sannu ,gwara Mamman shi yazo dalilin tursasawar matarshi Halimatu, Lantana tace yadda uwarka ta tafi tabarka haka kai ma zaka tafi kabar naka "yayan gyyar tsiya arna a idi, kullum in zata fita yawon tallanta sai ta tsaya a tsakar gida tayi surutai ,sannan take tafiya ,tana fatan Allah yasa kafin ta dawo ta tarar ya mutu kowa ya huta Allah mai yadda yaso a sanda yaso ,an kwanta da Ayuba lafiya daran alamis ,domin kafin yayi bacci ma sun dade da matarshi da yayarshi Atika ,gami da "yayanshi suna hira,ashe ta bankwana ce, da asubah Hafsatu ta rika tashin sa taji shiru ,sabida ta saba duk asubar fari shi yake riga kowa tashi a gidan,shiyasa ta gigice ta fice daga dakin da sauri,tayi dakin Iya Atika,ta daga labulen ta ce"Iya fito kiga babansu Sadiya yaki tashi, Da sauri Iya ta mike daga kan dadduma ta fito tana salati a zuciyar ta domin dama jikinta ya bata ,tunda ta kwanta take munanan mafarkai, Ta shiga dakin gami da zama kusa da qanin nata ,tana kallon yadda idon shi suka kakkafe tasan lallai Ayuba ya amsa kiran Ubangiji, salati take tana sallallami ,Hafsatu tace "Iya ya mutu ko"? Iya Atika tarasa mai zata ce mata sai kawai ta kama hanya zata fita daga dakin tana sharar hawaye, Kafin ta daga labule,taji abu ya fadi, rigif!! wanda yayi dai-dai da farkawar *Balaraba* daga bacci a furgice! Iya ta dawo dakin da sauri tana Salati ganin yadda Hafsatu tafadi kan Ayuba dake kwance, Tana daga ta taga ta kwanta yaraf! alamun babu rai! a jikinta, *INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN* Abinda Iya tafada kenan, Balaraba ta mike tsaye a zabure tana kallon iyayen ta biyu a kwance ,dukkaninsu babu rai! tace"Iya mai nene Iya kar kice min babana ya mutu,! Iya ki tashi Umma na kin ga tafadi, a kasa, sai ta fita waje da gudu bata saurari abinda Iya take fada mata ba, *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* 08089965176 [04/05, 03:17] +234 808 996 5176: 🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀ *GIMBIYA BALARABA* 🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀🧝🏻‍♀ *By* _BINTA UMAR_ *MAMAN ABDUL WAHABU* _BISIMILLAHIR RAHAMANIR-RAHIM_ *Page* *24* Lantana dake tsugune bakin rijiya tana daura alwala,ta juyo da sauri ganin Balaraba ta fito da gudu daga dakinsu tana ihu,sai ta mike tsaye gami da sakin botar hannuta,tace"ke Balaraba kina hauka ne,dan ubanki ko Ayuba ne ya mutu abinda zakiyi kenan,shashasha mara hankal.... Kafin Lantana ta karasa maganar ,Iya ta tare ta ,da cewar "to ai zan ce ya kare Ayuba da Hafsatu ,sun koma ga Allah,wanda yake ganin zai zauna jiran duniyar gashinan ga tanan. Lantana ta zabura ,cikin rawar jiki tace "me kika ce Atika, kina nufin Ayuba ya mutu"? Iya tafashe da kukan da yake cin zuciyarta tun dazu,tace "ai ba'a wasa da mutuwa Lantana ,leqa ki gani, Jikinta na rawa ta nufi dakinsu Ayuba, Ai kuwa abinda ta gani ya daga mata hankali sosai ,babu Ayuba babu Hafsatu, Lantana ta furgita sosai ,sai ta fito da sauri,ta fasa wani ihu! da ya ta da mutan gidan gaba dayansu har da makota, Kankace kwabo gida ya cika da jama'a ana ta kokawa da wannan mutuwar mai abin mamaki. Balaraba kuwa ta dai na kuka sai dai na zuci idanun ta sunyi mici mici kallon kowa kawai take,takama kanne ta da ke kuka ta rungume itama tana kukan zucci. Uwa da Lantana kai har da Sallau , mutuwar nan ta gigitasu ta firgitasu,sosai jikinsu yayi sanyi,amma abin mamaki ana yin sadaqar uku ,shikkenan ,suka watsar,mussaman ,yanda suka ga irin mutanan Ayuba ,suna kawo taimako, sai Sallau yayi uwa yayi makarbiya yace"ai shine wakilin yaran, sai Iya tayi da gaske sannan yake barinta ta karbi sadakar,komai idonshi na kai,ita ko Balaraba ,in an bata ,sai ta mikawa Iya,Ashe Sallau duk yana lura,sai yaga babu idon Iya sai yayi ta zuga Balaraba wai ta karbi kudin ta tabashi ,ya aje mata sabida in tazo yin aure shi zai yi Mata kayan gado, Kwata kwata Balaraba bata sauraronshi,sabida tasan ko ta bashi kudin zuwa zai yi yayi caca dasu kamar yadda yayi ,da wa"yanda ya karba ,yamma nayi ya lura,an dai na zuwa sai ya yayi tafiyarshi,mahadarsu,ta "yan caca Rayuwa kenan Balaraba ,ita ce tazama uwa da uban Sadiya da Usuman ,tun bayan rasuwar iyayensu,ita ce cinsu ita ce shansu, kudin makarantarsu,da nata, Bayan rasuwar iyayensu da kwana arba'in ,Balaraba ta hada "yan kudin da suka samu ita da "yan uwanta, ta shiga kasuwa ,ta siyo kuloli da farantai ,hade da manyan tukwane, tazo ta dira abincin siyarwa, a lokacin shekarun ta basu wuce sha shida ba, dake yarinya ce mai girman jiki ,shiyasa in ka kalle ta zakayi tunanin ta zarta haka, Balaraba tana da kyau sosai ,tana da diri na jiki, fara ce tas! Dan idan tayi kwalliya ta fita baza ka taba cewa a wannan gidan take rayuwa ba,tana da kirki sosai abin ta bai rufe mata ido ba domin ko abinci tayi kafin ta fita dashi duk wanda ya kwana ya tashi a gidan takan zuba masa ,sannan yaran da suke fitar mata dashi su dauka a kura, su kai mata bakin kasuwar,(sha tambaya) anan take siyar da abincin ta,wanda da an fita dashi yake karewa,wani

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108