Skip to content

Chapter 79

Chapter 79

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,209 words 0 views Progress saved
Download Book

yake nuna mata ta kalla, ita fa bataso tana had'a ido dashi domin. Idanunsa suna mutukar kashe mata jiki. Dakewa tayi tace"Duk maganar da zamuyi muyi ta anan da can da nan duk d'aya ne" Shiru yayi na minti biyu, yace"Na fi so ina kallon fuskarki maganar zata fi armashi" Tab'e baki tayi tana d'an hararsa, minti biyu da maganar tasa ta mike a nutse taje ta zauna kujerar da ya nuna mata, zama tayi irin Wanda ake Dora kafa d'aya kai d'aya. Kallonta yayi yana mamakin zaman k'asaitar da tayi, babu Wanda ya isa yayi irin Wannan zaman a gabansa, ba tare da ya karb'i hukunci ba, amma da yake ya san halinta sai ya share kawai ya gyara fuskarsa sosai idanunsa ya zuba mata babu wasa yace"Inaso ki yi min bayanin Asalinki dana mahaifiyar ki, domin inajin a jikina akwai wani al'amari a game dake, bazan b'oye miki ba, nafi k'arfin shekara goma shabiyar ina mafarki dake tare da wata mata da alama mahaifiyar ki CE,tunda kullum tare nake ganinku kuna zuwan min cikin mafarkina, wannan mafarkin babu Wanda yasan dashi sai ni sai ke, yanzu Dana fad'a miki" ****** ****** ****** A kori kura guda biyu aka cika da kayan masarufi, su Shatima suka nufi gidan su Balaraba inda suka samu rakiyar daga Bubu direba tunda shi kadai ne yasan gidan. Sosai Shahid yayi mamakin inda mahaifar Balaraba take,ashe dama 'yar talakawa ce tilis, Lallai so babu ruwanshi ko a mafarki bai tab'a tunanin zai iya zuwa irin wannan gurin ba, Soyayar da Moddibo yakewa Balaraba ta gaske CE. Tabbas yayi mamaki da ya kalli yanayin jikinta da fatar ta, idan zata kwana tana rantsuwar babu Wanda zai CE a cikin irin wannan guri take rayuwa. Yara ne suka fara taruwa a gurin suna tsale suna d'ane mota sai su ruga da gudu, hankalin Samar in dake can tsallake ya dawo Kansu da sauri suka k'araso gurin, Buba Direba ya bud'e mota da sauri ya futo ya bud'e wa su Shahid suka futo, ganinsu cikin kayan sarauta yasa yara zurawa da gudu zuwa gidajansu suna ihu! Suna fad'in ga sarki! Sarki ga sarki! Mutane suka fara lekowa daga gidajansu. Da sauri Shahid ya umarci matasan nan dake tsaye a gurin yace su fara d'ibar kayan nan suna shiga dashi, lungun su Balaraba, Buba yayi gaba, sukuma suka koma cikin motar saboda hayaniyar jama'a, yuuuuuu!! Jama'ar dake gurin yara da manya suka rufa musu baya domin ganin ina za a shiga da wannan uban kayan masarufi. Lantana ta sawo Kai kenan zata futo daga cikin gidan suka buga karo da Sauri ta koma da baya tana masifa! Abokin Walidi yace"Lantana ina zakije ne"? D'ago kai tayi a fusace za tayi masa masifa"Aik.. Idonta ya sauka kan k'aton buhun shinkafar dake kansa ta bud'e baki kenan za tayi magana, sai ta hango matasa hud'u kowanne kansa da buhun shinkafa irin na kan Abokin Walidi kuma da alama suma gidan zasu kaita,, Zanin jikinta ne ya sabule garin sauri ta buge da kyaure bata damu ba, da sauri ta tsugans ta dauki zaninta da ya fad'i k'asa tana tafiya tana d'aura wa gami da k'walawa Maburuka kira. ************ ************ ************* A nutse take kallonsa tace"Bangane kullum kana mafarkina ba, a ina kasan ni ka san uwata da har zaka dunga mafarkin mu"? Ta karashe maganar cikin mamaki. "Duk ba wannan na tambaye ki ba,duk wata maganar ki ki aje ta gefe guda ki fara bani amsa ta tunda nine na tambaye ki" Tab'e baki tayi yana wani murmushi irin na gefan baki nan, girgiza kai tayi ta dago kai tana kallonsa tace"Ni ba wata aba b'ace kamar yadda kake tunani hakanan kuma ni ba "yar kowa bace, Tunda nake da Moddibo bai tab'a turke ni yana tuhumata da dole sai ya San asalina ba,saboda yasan inda yaje ya d'auko ni" Hararata yayi k'asa-k'asa cikin muskilanci yace"Ni daban Moddibo daban, in zaki fad'a min ki fad'a min banason, bata lokaci" Ganin fuskarsa babu wasa yasa itama ta gyara tata fuskar ta fara magana kamar haka. *Sunana Balaraba Ayuba Tanko* Dago kansa yayi yana kallonta sai ya tuna da lokacin saukar al'kuranin ta. Basarwa yayi yace"B'angaran uwa fa"? Ranta ya soma b'aci, dakewa tayi tace"Sunan babata Hafasatu, kakata kuma Kaka Suwaiba gurin haihuwar babana ta mutu" "Allah sarki, Ubangiji Allah ya jikinta da rahama" Ya fad'a cikin jimami! "Uhumm"! Ina sauraron ki"? Yafad'a yana tsatsare ta da ido. Wasu hawaye ne suke k'okarin biyo kumatun ta, à kufule tace" Wai kai dolene sai kasan Asalina in baka aure na a haka ka fasa ai babu dole. Ni ban san asalin mahaifiya ta ba. Shikkenan Malam" mik'ewa tayi zata bar gurin tazo ta giftashi, kamar kububuwa Dan haushi sai nishi. Take, tana tuno Moddibon ta, duk tsawon lokacin da suka dauka suna soyaya dashi bai tab'a turke ta ba, sai wannan Dan rainin hankalin ai babu dole idan bazai aure ta ba sai ya fasa. Hannu ya rik'e sosai yana murzawa ta sha kunu! Tana fad'in 'sakar min hannuna" K'i yayi yanai mata wani irin kallo, me tattare da abubuwa kala-kala a zuciyarsa yace"Ashe dama wannan zafin kan nata yana nan. Ajiyar zuciya kawai take saukewa idan da tasan tambayar da zai mata kenan babu abunda zai sata ta tsaya ta saurare shi. Mintuna kusan biyar suna a haka bai sake ta ba. Hannusa a cikin nasa , muryarshi bata futa sosai yace"Naji na janye wancan maganar ta baya, tunda ba kyaso amma wannan dole ne ki amsa min ita, lokacin da kina sai da abunci cikin kasuwar sha tambaya maza nawa kika kula"? ************* ************** *************** Mabaruka ta futo daga cikin d'akinsu a sukwane jin irin kiran da Lantana take k'uga mata, fad'i take 'wannan tsohuwa da jaraba take wallahi. Lantana ta shigo gidan tana fad'in "Mabaruka kece me mutanan arzki masu kudi da naira, yau wani Dan sutturar daga cikin mutanen ki ya rufa mana asiri ga kayan arzkiki na......Kafun Lantana ta rufe bakinta Zaratan samari suka dunga shigowa da kayan masa rufi buhu-buhu. Uwa! Ta futo daga ita sai d'aurin kirji da wata daud'addiyar biriziya duk Tasha d'auri hannuta duk ya saki, kanta inda kasan kan jaka fuskar ta sai maiko takeyi,, wata irin gud'a ta rafka Ayurrrrrrrrrr!!! *Muje zuwa* 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*GIMBIYA BALARABA*_ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* ```MARUBUCIYAR``` *NANA KHADIJA* *YARO DA KUD'I* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* _*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_ _________________________ ```We are here to educate, motivate and entertain aur Reades``` _________________________ _*DEDIGATED*_ _*TO*_ _RAHAMA ALIYU_ _*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR RAHIM*_ *🅿92* Uwa! sai zabga gud'a takeyi babu ji babu gani, sai da tayi me isarta sannan, ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya tace"Yau "yan bak'in ciki zasu mutu, nima lokacina yayi, haihuwa tayi min rana, Mabaruka farar aniya farar haihuwa,nasan wannan alkairin kece silar shi" Ta k'arashe maganar tata tana dafa kafad'ar Mabarukan. Ita kuwa tunani takeyi waye ya kawo mata wannan shatara ta arzkin domin basuyi da wani daga cikin samarin ta ba, wata zuciyar tace mata ko dai Alhaji Saminu ne, mutum da yake so yayi luwad'i da ita. Nan take ta yardar ma kanta cewa shi d'in ne. Bak'in ciki kamar ya kashe Shamsiyya domin suma a junansu hassada suke ma junansu. Shigo da kaya abunci

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108