Chapter 54
Chapter 54
Magajin Sarki ni kad'ai nasan abuda yake damun raina fa, jiya kwana nayi ina murk'ususu ciwon cikina ya tashi, kasan yadda yake min in ya motsa min" Da sauri ya kalli fuskarsa yaga duk tayi zuru-zuru, tabbas da gaske yake, yace"kayiwa girman Allah ka rage k'ulafun yarinyar nan, kar kaje ka tayar mana da hankali, kafi kowa sanin in ciwon ka ya tashi, babu me zaman lafiya, da kwanciyar hankali, ba kai kad'ai ne kake shan wahala ba harda mu gaba daya " Girgiza kai Moddibo yayi yace"sam ba soyyayar da nakewa Balaraba bace zata tayar min da ciwon na ba sai dai rashin fahimtar dake tsakaninku da ita, Balaraba ba ta da kowa,a yanxu sai Ina so ka tayani sonta da kula da ita" "Shikkenan zanyi yadda kace, amma don Allah kar ka jawo mana tashin hankali, Indin saboda bana sakin jiki da Balaraba ne, yasa kake wannan tunanin na dai na daga yau insha Allah" Farin ciki ne ya kama Moddibo fuskarshi a sake suka shiga shashen Sarki! d'in zama yayi cikin kujera shi kuma Moddibo ya hau sama,d'akinsu Balaraba, tana zaune ta zanga tagumi cikin damuwa Sadiya da Usuman na zaune gefe-da gefen ta, yayi sallama ya shiga, dak'in dago kanta tayi cikin nutsuwa ta sauke a kansa har ya k'araso kusa da ita ya zauna da murmushi a fuskarshi, yace"barka da asubah sarauniyar zuciyar Yusuf Moddibo, zuciyata tana azabtuwa da so da k'aunarki Ina fatan kin tashi lafiya"? Fuskarta d'auke da k'ayataccan murmushi ta sauko k'asa gami da sunkuyar da kai, tace " lafiya kalau na tashi Ina fatan kai ma ka tashi lafiya"? "lafiya k'alau, ya kwanan bak'unta kuma"? Shuru tayi kawai har yanzu da murmushi a fuskarta, yace" sakko muje k'asa Ku gaisa da mutumin ki" B'ata fuska tayi, tace"ba Kaine kake gaba dashi ba,ai shine ya kamata yazo ya gaishe ni" "Duk da nine nake gaba dashi amma girman shi yafi nawa, kuma a matsayin ki na matata uwar " yayana ya kamata ki d'aukeshi a matsayan magaji na tunda shak'ik'ina neshi, duk ranar da bana nan,shine zai mar miki uwa uba" K'walla ce ta taro a idonta tace" wannan wace irin magana ce kake Yusufu ni dai ka daina min don Allah" Kamar zata fashe da kuka ta k'arashe maganar. Rarrashin ta ya fara yi cikin taushin murya har sai da yaga ta mayar da k'wallar sannan hankalinsa ya kwanta ya kalli su Sadiya gami da shafa kan Usuman yace"kun tashi lafiya"? Kai a sunkuye Sadiya tace"Yaya Yusuf Ina kwana"? Amsa yayi fuskarsa a sake, Usuman ma ya agaidashi a nutse ya amsa, Balaraba tace"Sadiya ai da zazzab'i ta kwana mybe ko b'akonta ne" Hankalin sa a tashe ya jawo yarinyar yana tambayar ta, jikin nata, tace" Yaya Yusuf naji sauk'i abokinka wannan me kyau d'in yana da kirki shine ya bani magani nasha cikin dare" Moddibo yace"sunanshi Sark! Ko ce masa Magajin Sarki! nasan zaiyi fiye da haka ma, saboda yana tausayi" Kicin-kicin da fuska Balaraba tayi tace"ka gafarce ni Yusuf, ko maganar da zanyi maka zata b'ata maka rai, gaskiya kayi masa magana jiya cikin dare ya shigo d'akin nan, gaskiya ni ban yadda ba" Wani iri yaji a zuciyar sa, jin abunda tace"me ya kawo Sarki! d'akin, ya san halin d'an uwanshi ba mane min mata bane,kuma bazai ci amanarsa ba, Sadiya tayi Sauri tace"A'a Yayarmu ya ganni a wajan d'akine shine ya bani magani nasha ya rakoni na kwanta yace kuma in daina futowa cikin dare" Moddibo yace"yanzu naji,zance, kiyi hakuri Gimbiya babu abunda zai faru sai alkairi ba halin Sarki! bane abunda kike nufi" d'an tab'e baki tayi kawai tayi shiru yace"Ku tashi mu sauka k'asa Ku gaisa sai Ku karya" M'ikewa sukayi duka suka nufi k'ofa. Karo sukaci dashi zai hau saman shima, ratse masa sukayi a baranda har ya k'arasa hawowa Mariya baiwarsa ce take bayansa da'alama gyare-gyare zatai masa Wanda takeyi kusan kullum duk safiya, murmushi ya sakarwa Sadiya, sam ! baki kalli inda Balaraba take tsaye ba, ciki-ciki tace"Ina kwana"? yaci albarkacin Yusuf Moddibo. A dak'ile ya amsa, ya mik'awa Sadiya hannu, yarinya mai sauk'in kai da wayewa sai ta sanya hannuta cikin nasa tana yar dariya tace" Magajin Sarki ina kwana"? Cikin mamaki yake kallonta sai kuma ya kalli Moddibo cikin tuhuma yasan shine zai fad'a mata wannan sunan, saboda ba kowa ne ya ke kiransa dashi ba, Murmushi Moddibo yayi, shi kuma ya tab'e baki kawai yaja hannun Sadiya suka nufi d'akinsa, Sakin baki Balaraba tayi kawai tana kallon ikon Allah, shi kuma yana sane ya sakarwa yarinyar fuska duk Dan ya muzgunawa zuciyarta, saboda yana bala'in jin ciwon zargin da take masa a kan yarinyar,baya ga haka ma, yarinyar ta kwanta masa,tana da hankali da nutsuwa ba kamar yayar ta ba. *Comments Vote and Share* 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ _*DEDIGATED*_ *_TO_* ```RAHAMA ALIYU``` ```BISIMILLAHIR- RAHAMANIR-RAHIM``` *🅿62* K'asa suka sauka zuciyarta tana mata sak'e-sak'e kan zak'ewar da taga mutumin nata yayi kan Sadiya,sam bata yadda dashi ba, ganin yadda yake wa mutane wani irin kallo, kullum ido a lumshe kamar munafuki. Ko da suka sauka k'asa hadimai ne su wajan biyar maza biyu mata biyu suna aikin gyara falon,kowa da inda yake gyarawa, jikinsu sanye da wasu kaya iri d'aya masu kamar Uniform, wani k'amshi ne mai dad'i ya cika hancinta, wani ku-ku ne ya futo daga kchin hannusa dauke da wani tank'asheshan faranti cike da abubuwan ci, Balaraba tayi saurin kauda kanta domin bata so tayi k'auyanci irin na jiya, hannun Usuman ta kama suka ni bayan Moddibo,inda ya nufi Wani k'ebantaccan guri a falon, yace da Usuman ya zauna, yaron ya zauna cikin wata k'aramar kujera mai taushi, zama tayi itama tana bin gurin da kallo gaskiya k'ayatuwar gurin ya burgeta sosai dagani gurin hutawa ne, D'aya daga cikin hadiman dake aiki a gurin ne ya k'araso ya zube gaban Moddibo yace"ranka ya dad'e a kwai abunda za'ayi ne"? A nutse Moddibo yace"ka kawo abun kari na mutum hud'u" Cikin bin umarni ya mik'e daga gurin. Cikin nutsuwa ta kalli Moddibo tace"ya kamata fa ka kira Sadiya haka" " Yanzu zai sauko ai wanka ya hau yayi" Shiru tayi kawai tana d'an ya mutse fuskar ta, tace"tsarin gurin nan ya burgeni Yusuf ina so abu White coulor" Murmushi yayi yace"lallai tsarin ku d'aya da mutum min in kin lura ai duk adon falon nasa white ne" Shiru tayi tana da tasanin fad'ar maganar, minti biyu tsakani yace"zan shirya miki falon ki da wannan colour" "Nagode" Abunda tace kenan,tayi shiru kanta a kasa tana wasa da hannuta Tsura mata ido yayi,kurum yana kallo, ta d'ago kai tana kallonsa suka sakarwa juna murmushi, tace"wannan kallon fa,Yusuf"? Da murmushi a fuskar sa yace"kallon soyyaya ne Gimbiya zuciyata tana fad'a min akwai wani babban al'amari da zai faru a tsakanina dake" Itama Murmushin take,tace"babban al'amari ai bai wuce na aure na da kai ba, dama ina so in tambaye ka a wace matsaya muka tsaya,nifa zama anan kamar a kan k'aya nake" " Karki damu insha Allahu yanxu in na tashi daga nan gurin me Martaba zan wuce, za'ayi komai a gama cikin kwanciyar hankali"
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108