Skip to content

Chapter 82

Chapter 82

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,222 words 0 views Progress saved
Download Book

sai aikinsu suke, k'amshi suke ko ta ina Sarki yana cikin wata d'anyar Shadda gezner me mugun tsada anyi masa wani irin dinki babbar Riga da " yar ciki ita kanta hular dake kansa da da yankin shaddar aka had'a ta kafarshi sanye da wani takalmi rufaffe mai mugun kyau kalar kayan jikinsa sky blue yayi masifar kyau fysakarsa sai futar da annuri take, sajensa ya kwanta lif-lif a fuskarsa hannusa wani irin agogo ne, na zallahr azurfa, kana ganinshi kasan yana cikin farin ciki da annushuwa, sai gaisawa yake da manyan mutane gwamnoni da "yan majslisa sanatoci da sauransu, " yan abokan arziki duk murna sukeyi da farin ciki. Wata kujera ya nufa wacce a ka k'wata ta da shimfud'u na alfarma yana tafe su Shatima na take masa baya, zama yayi cike da k'asaita, wasu nayi dake tsaye suna jiran zuwansa suka hau yimasa firfita, Shahid da Shatima suka zauna gefe da gefan sa. K'irari kawai kakeji da busa marok'a sun rud'e kowa da irin nashi rok'on kowa naso ace nashi yafi na d'an uwanshi. "Masha Sarki! Ya futo fasa taro Jimana na gaban Giwa, baka iya ba Allah ne zai yi maka, yaro me Halin dattako! Fari mai farar anya! Hak'ika matayen ka sun dace da samun nagartaccan miji jarumin jarumai,, Duk zaka iya dasu har da k'warl'wara ma, Sarki! Almasur kujerar mulki takace Allah ya yataka ruk'o jamuje Gami sha sassaka duk wani mak'iyinka sai da ya mutu!!!!!! faaaa!! Gurin d'aurin aure ya kai ya kawo jama'a d'aurin auran mataye uku ba wasa ba ne, Waziri Zayyanu na gefe guda shi da tawagar shi duk ransa a b'ace yake shi ba abun ya koma gida, wata zuciyar tana ce masa ya zauna kawai a k'arasa dashi, dole shine Waliyyin Ango kuma yayi rantsuwar bazai masa waliyi ba, Yana kallon Shige da fucen da Galadima yake shida Wambai, sam sunk'i su zauna kusa dashi,sun karkata gurin Sarki,yasan duk kalar munafurci ne, kujerar mulki sukewa yaga kuma yadda za'ayi a karb'eta a hannusa. Gaisawa kawai yake da jama'a ba dan ransa ya so ba, mutane sai zind'ansa suke suna nuna shi a matsayinsa na Sarki me rik'on k'warya. Sai da aka fara d'aura auranshi da Halisa kan sadaki dubu d'ari sannan aka d'aura da Azima itama sadaki dubu d'ari, sai Balaraba itama haka, Liman ne ya karb'i wakilcin Balaraba,saboda babu wakili Sallau ne kuma bai zo ba saboda tsabar bak'in ciki,shi kuma Maman baya gari yana can tafiya tafiyensa dake babbar motar d'aukar kaya yake ja,,, Kowa ce aka damk'awa Wakilinta sadakin ta, Liman ya rik'e na Balaraba a hannusa yace shi zai bata da hannusa. Bayan d'aurin. Aure guri ya hargitse da ciye-ciye na abunci nau'i nau'i ana futo dashi daga gida,, Masha Allah kowa yaci kuma yayi guziri guri bai watse ba sai dab da sallahr azahur sannan kowa ya nufi gida domin yin sallah. Mahaifin Azima ne suke keb'e da Waziri suna maganganu k'asa-k'asa karku manta da cewar dama tuntuni abokai ne Tun daga nesa Sarki! Ya Fahimci akwai maganganu da suke tattaunawa. Kuma da alama basu da gaskiya, suna ganin sun k'araso gurin Mahaifin Azima ya saki fuskarsa sosai yana fad'in "Dama ina cewa azo a nemo min kai muyi sallama yau zamu koma ni da tawaga ta, inai maka fatan alkairi da d'or ewar zaman lafiya kai da iyalinka, ga Azima nan nabaka amana,yanzu ma abunda nake kara jaddadawa abokina kenan gashi nan a tsaye" Fuskarsa babu yabo babu fallasa ya mik'a masa hannu yana fad'in "Insha Allah karkadamu mungode sosai A sauka lafiya" Cire hannusa yayi ya mik'awa Waziri Zayyanu, kauda kai yayi ba tare da ya bashi hannusa ba, yace"Ka rik'e gaisuwarka ni bana buk'atarta, na fad'a maka tun wuri tsalle d'aya mutum yake ya fad'a rijiya, amma sai yayi dubu bai futo ba" Yana gama maganarsa ya wuce ya barsu tsaye a gurin, Sarki! Shahid Shatima Duk suka bishi da kallon mamaki. 👸🏻👸🏻👸🏻 _*GIMBIYA BALARABA*_ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* ```MARUBUCIYAR``` *NANA KHADIJA* *YARO DA KUD'I* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* _*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_ _________________________ ```We are here to educate, motivate and entertain aur Reades``` _________________________ _*DEDIGATED*_ _*TO*_ _RAHAMA ALIYU_ _*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR RAHIM*_ *🅿94* Sanin Hali yafi sanin kama,Sarki fuska yayi kawai ya wuce ba tare da ya tsaya ya k'ara sauraron wata magana daga bakin Mahaifin Azima ba wato me Martaba sarkin Yalwa, ganin ya wuce ne yasa su Shahid suma suka rufa masa baya suna cike da mamakin abunda Waziri Zayyanu ya aikata. Suna tafe suke maganar har suka isa shashen nasa Shatima ya zauna kan kujera yana fad'in "Sai yanzu gajiya ta fara damuna kuma" Shahid yace"Duk ba wannan ba, abunda wannan mutumin ya fad'a fa abun dubawa ne, Tsalle d'aya mutum yake ya fad'a rijiya,Wannan Kalmar a hausance meye ma'anarta"? Wani k'asaitaccan murmushi Sarki! Yayi yace"Ku rabu dashi don Allah inajin shine zai fad'a rijiyar ya kasa futowa" Shatima yace"magana ce me harshen damo kuma da gani akwai wani k'ulli Shahid yace"Nima na lura da haka wallahi tunda muka doso inda suke, suna magana k'asa-k'asa" Tab'e baki Sarki yayi yana kici-kicin cire babbar rigar dake jikinsa yace"Mugun k'ullinsa zai koma k'ansa ni ina tare da Allah" "Wannan magana haka take,duk mutumin da yake tare da Allah kuwa to babu abunda wani mutum zai masa ba tare da Allah ya tsare shi" Su Shatima ne suka fad'i wannan maganar. Zama yayi kusa da Shahid da gashi sai Singelt da dogwan wando na shaddar dake jikinsa, yana fad'in zafi nake ji wallahi ga yunwa kasan tun jiya da yamma rabona da cin abunci" Shahid yasa dariya yana fad'in ai zama da yunwa ya k'are me mata hud'u rigis" Gabansa ne ya fad'i kad'an shi kansa yana tunanin yarda za'ayi ya zauna dasu lokaci guda. Shatima yace"Mutumina ai jarumi ne, zai iya rik'e su, ni dai INA ja maka kunne da kayi adalci a tsakaninsu" Shatima ya k'arshe maganar yana dariya Hararasa yayi yana fad'in "Ank'i ayi adalci me yasa su baza ka fad'a musu suyi min adalci ba sai ni zaku ta damu da maganar adalci, duk wacce tafi kyauta ta min itace Gimbiya ta" Dariya suke masa,Shahid yace"Maganar haka take duk macan da take kaytata ma kafi jin ta aranka. Ammafa kowa ce mace da irin nata salon wata akwai iya salo da jawo hankalin me gida da iya kwanciya wata kuma iya girki da iya hira wata kuma iya kwalliya da tarairaya duk dai gasu man, idan Allah ya hore maka mace me ibadah fa duk wannan abubuwan Dana fad'a to kayi sa'a a rayuwarka" Shatima yace"Wannan maganar haka take" Shiru yayi musu suna ta zubah, mik'ewa yayi ya je ya k'aro k'arfin AC sosai yake jin zafi abunka da wanda be saba ba,ya shiga cikin jama'a ga rana da cukurkud'u kowa naso ya gaisa dashi, shiyasa ya daure ya dunga gaisawa da jama'a domin futa hakkinsu Shahid ne ya kalle shi yaga yana lumshe ido, yace"Ko a sa a kawo abunci ne" Bud'e ido yayi yana kallon daining, babu komai a kai, d'aga kai yayi ya mayar da idonsa ya lumshe. Shahid ya mike yana k'okarin futa, bud'e idonsa yayi a karo na biyu yace"Kasan me"? Shahid ya tsaya yana kallonsa, shi kuma yace"tea nake so

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108