Skip to content

Chapter 25

Chapter 25

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,249 words 0 views Progress saved
Download Book

kunyar yarinya kwanakin baya, da sukayi saukar al'kurani,makarantar tasu ta kawo saukar gaban sarki, Sunanta Balaraba, bazan taba mantawa da kallon banzan da tayi min ba, kai in ka gani sai kayi mamaki, lokacin kana can Swiziland, abun ya bani mamaki, sosai" Murmushi Maddibo yayi yace"nafada maka duk me wannan sunan ba karamar mace bace, mybe ka nuna mata halinka ne shiyasa ta nuna maka nasu halin" Tabe baki yayi yana dan sosa sumar kanshi wanda hakan ya zame masa jiki in dai zai yi magana sai yw sosa kanshi yace"me ya dameni da ita,kasan ni mata basa gabana,wallahi, kai ni fa zan iya kare rayuwata batare da wata mace ba" "Wannan kuma mahaukaci zaka fadawa wanda bai san wanene kai ba" Dariya yasa ya dan sosa kai yace"Wallahi nake gaya maka yarinyar nan wai a na cewa gani na fito, ita ta riga kowa tashi domin ta ganni ina lure da ita, daga baya kuma ta fara yimin kallon banza,sai kace wani sa'an ta" "Maddibo ya ce" ka ishemu da zan wata yarinya ko ka na ciki ne, dan ban taba ganin ka ka zauna zance wata ba,ko Halisa bata da wannan matsayin" "Kai me zanyi da wannan yarinyar" yafada yana gyara fuska ya cigaba da cewa"kawai dai inai maka kwatance da ita ne, Allah yasa taka Balarabar ba irin halinsu daya da waccan din ba" "Zamuje ka ganta ne ai sam tawa daban take da kowa" "Ok Shikkenan, Allah yasa" Nan suka cigaba da hira har suka karasa Unguwarsu Balaraba, Maddibo ya kalli Haladu Direba yace"yi parking dai-dai can" da sauri Haladu yayi parking din motar inda a ka umarce shi, A nutse ya dago kanshi yana bin unguwar da kallo, Kallon Maddibi yayi yace"wannan wace irin unguwa ce ka kawo mu, guri duk tarkace da kazanta, ko ina kango,da kwatoci, kasan bazan fito ba wallahi,kaje kasa a kira maka ita" Ajiyar zuciya Maddibo ya sauke domin yasan dole za suyi haka dashi, yace"kake maganar kango duk gidajan jama'a ne, duk babu wani kango a cikin nan unguwar, wannan tarkacen kuma da kake gani yaran unguwar ne suke sana'ar gwan-gwan" Ya mutse fuska yayi yace"gaskiya Maddibo baka da kirki, yanzu da kasan a irin wannan unguwar budurwar taka take ka gayyoto ni,kamar baka san halayyata ba, kai yanzu ya dace"kazo ka nemi matar aure a irin wannan guri"? "Kaga bana son ka bata min rai dan Allah, kafito mu shiga ga lukon gidansu can,yanzu duhun dare ne babu wanda zai gane ka" "Billahillazi, babu inda zanje nayi iya yi na, in ka damu kai ka futa ka kurawo ta sai mu gaisa,amma bazan fita daga motar nan ba,haka kawai kwalabe su fasa min kafafu,kan wata shashashar budurwar ka wai ita Balaraba" ya karashe maganar yana gyara kwanciya cikin motar babu abunda ya dame shi. Sanin halin taurin kai irin na Sarki! yasa Maddibo jan tsaki ya bude motar ya fita sabuda yasab duk nacin da zai masa bazai fito ba kamar yadda ya fada Dariya Sarki! yasa bayan fitar Maddibo daga cikin motar yace"duk Abinda zakayi kayi amma bazan fita in cuci kai na ba" Haladu Direba ya fito ya tsaya a bakin motar yana kalle-kalle, ganin fitowar Maddibo, yasa ya karaso Maddibo yace"ka tsaya kawai zan fito zan shiga gurin can" "A fito lafiya yallabai" Haladu ya koma bakin mota ya tsaya, Ganin motar gidan Sarauta yasa yara suka fara, taruwa *Comment* *Vote and Share* [02/07, 14:47] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† _*GIMBIYA BALARABA*_ βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» _*Na*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` Zamani Writes Association🀝🏻 ```Bisimillahir rahamanir rahim``` *πŸ…Ώ36* Kasancewar babu wutar nepa a unguwar shiyasa yara basu ankara ba sosai, dabi'ar yaran cikin gari kenan in suka ga bak'o cikin mota zasu zo su tsaitsaya suna kallo wasunsu kuwa har zuwa suke su dinga taba motar suna dariya suna rugawa gida da gudu,Sarki!yana kwance cikin motar yana bin unguwar da kallo, cikin zuciyarsa yace"yanzu haka jama'ar dake cikinta suke rayuwa, wasu gidajan gasu nan duk babu kofofi, wasunsu an sanya musu buhu an kare sabuda kar a gano cikin gidan, a fili yace"da gani gurin zai yi sauro sabuda tarin shirgi da datti da kazanta, dole a kawowa unguwar a gaji, Shi kadai yake wannan sake-saken cikin zuciyarsa, gefe guda kuma ya zaku yaga wannan yarinya da Maddibo ya makance a kanta. A nutse Maddibo ya kutsa kansa cikin lungun su Balaraba wanda yake dauke da tarkace iri-iri haka ya dinga tsallake kananun langa-langa da robibi har ya karasa kofar gidansu Balaraba,inda yara da matasa suke tsaye kan Shamsiyya wacce take ta faman soya awara da kwai, Gefe guda ya ja ya tsaya ya kira wani yaro wanda yake tsaye kan Shamsiyya yana jira ta sallame shi, "Kai Salmanu ungo awarar taka, in sallame ka in huta" Shamsiyya ce ta dago tana wa Salmanu magana,kawai sai ta ganshi ya nufi gurin wani mutum can gefe, fitilar wayarta ta kunna ta haske fuskar Maddibo tana wani ya mutse fuska tace"wancan wanene a tsaye a can ne" Da Sauri Walidi dake tsugune kusa da ita yana zukar wani abu a tsumma ya mike yana wani ciccije baki yace"yana ina ne yanzu in farde masa ciki"! "Gashi can naga ya kira Salmanu ko uban me zai yi masa oho! je ka gani" Walidi na tafiya yana hada hanya ya nufi inda Maddibo ke tsaye tare da Salmanu Matasan dake tsaye a gurin ne suka rufa masa baya suma cikin rashin tarbiya suke cewa"bari muje muga wane dan iska ne,yanzu mu kaddamar masa"! Maddibo yana hangen zuwansu gurinsa sai ya gyara tsayuwarsa, har suka karaso gurin,suka tare Salmanu, cikin tsageranci Walidi yace"kai ina zaka ne? me wancan guy yace maka"? Jiki na rawa Salmanu yace"Cewa yayi in kira masa Gimbiya ta gidanku" "Kai!! dan uwarka wacece Gimbiya a gidanmu"? Walidi yafada yana dukan kafadar yaron. " Balaraba fa yake nufi" Salmanu yafada jikinsa na rawa domin wani irin tsoran Walidi yake ji Cikin tsawa!Walidi yace "kai! kauce daga nan dan uwarka ko in yaga ka, yanzunan" Da gudu Salmanu ya bar gurin, Cikin wata irin tafiya Walidi ya karasa kusa da maddibo ya tsaya yana masa wani irin kallo, duk da cewa a kwai duhu a gurin bai hana shi ganin irin kallon da yake masa ba. "Kai waye ya baka izinin shigo mana lungu ehe,! mufa duk inda mukaga bakuwar fuska babu yadda, gurin wace Gimbiya kazo a lungun nan" Dariya ce taso takama Maddibo ganin yadda yaron yake wani ciccije baki yana wani tangadi tamkar zai kai masa duka, gashi sai warin ganye suke dukkaninsu, girgiza kai yayi gami da gyara tsayuwa yace"Sannuku "yan samari, ni bak'on alkairi ku kwantar da hankalin ku, Gurin Balaraba nazo" Walidi ya gyara tsayuwar gami da zira hannu cikin aljuhun wandonsa ya fito da wata wayarsa wacce duk ta sha dauri ka da kyaure sabuda tsabar ganin duniya,ya kunna fitar wayar cikin sigar rashin mutumci ya dallare fuskar Maddibo da ita, Sai wayar ta kusa faduwa sabuda razana da yayi, ganin Fuskar Sarki!Almansor da yayi, sabuda Maddibo suna dan yanayin kama da Sarki!amma ba sosai ba, sai dai duk inda jininka yake za'a ga kama ko yaya ne" Bakinshi na rawa yace"ranka ya dade, kace Balaraba kake

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108