Chapter 18
Chapter 18
zan fita muka hadu da cinkoso a titi haka ma yanzu abinda ya tsai dani kenan, ga mariba ta wuce ban yi sallah ba" "Ai kuwa sai ki yi harama yin sallah sabida kin san sallahr magariba lokacin ta kurarre ne" Iya tafada ta kokarin daura Alwala Lantana ta hau surutai na ha baici, tanayi tana tauna goro babu abinda ya dameta, Iya da Balaraba suna jinta babu wanda ya tanka mata a tsakaninsu Uwa tace"ke ma dai Lantana da wata magana kike wanda a ka rai na shi za'a fadawa haka ya yarda,mu babu abinda za'a rufe mana duk abinda mutum yakeyi muna da labarinshi, Sadiya matar Kawu Maman ce ta fito daga wurin ta, ta dan tsinci magan ganun da Uwa take a kan Balaraba, tace"ke dai Uwa kinyi a sara wallahi, ki tsaya kina shirme da "yar cikin ki, ki tsaya ki gama kashe wutar dake gabanki mana, amma kin bi kin sanya yarinuar nan a gaba kullum da irin sharrin da zaki kulla mata,kuma kullum kina cin arziqinta duk abinda kikeyi a na sani, haihuwa ce kema kinyi,duk abinda kasowa kanka to ka sowa dan uwanka, amma gaskiya abinda kikeyi ba kya kyautawa wallahi" Saura kadan Uwa ta kifar da kaskon tuyar awarar ta wanda yake cike da mai gefe ga uban a wara nan cikin roba ok Tayi kan Sadiya da masifa "ke kinga sarkin kinibibi da kankan ba, kwadayayya kawai, au! sabida in ta taje yawon iskancinta ta dawo tana kawo miki ajiyar kudi kuyi raba dai-dai shine kika fito zaki tare mata, iyi, to bari kiji babu ruwanki da ni da " yayana wallahi, bakinki ya sari dayan kashi,duk cikin zuri'ata ban haifi lalatattu ba ehe! ke da baki san ciwon haihuwa sai ki fadi haka, in kinyi zuciya yau ki haihu banza juya wacce bata haihuwa kawai" Uwa ta kare maganar tana buga cinya bakinta duk ya tara yawu sabida sabida tsabar jaraba da masifa Sadiya tayi wani murmushi mai ciwo ta kalli Uwa tace"Babu abinda yake damunki sai jahinci, wannan "yayan naki da kike magana a kansu,ni a gurina da haihuwarsu gwara babu,sabida zasu iya yi miki sanadin shiga wuta, sabida haka babu abinda zan ce yanzu sai dai in ce Allah ya shirye ki, kuma Balaraba da kike wanna tada jijiyar wuya a kanta tafi karfin ki daga ke har " yayan ki" da mara Uwa taci ta dinga cusawa Sadiya zagi gami da gore-gore tace "karya kike ki ce wancan mutsuyaciyat yarinyar tafi qarfina wallahi sai dai idan banga dama ba,ke dai kawai kice kina yi min bakin ciki kawai ganin ke baki haihu ba, Lantana na zaune tana jinsu uffan bata ce ba, dama in suna fadansu bata saka musu baki, Iya kuwa sauri takeyi ta idar da sallaha tafito, Balaraba ma sa taji abin yayi yawa tafito ta kama Matar Kawu da yake haka take kiranta dashi, tana bata hakuri da kyar ta mayar da ita gurunta, tafito ta daura alwala, kowa yayi shiru, sai Uwa ce kawai take zage-zage ga yara nan sunyi cirko-cirko suna kallonta taqi tazo ta sallamesu, Walidi ne ya shigo gidan kafadar sa rataye da wani katon buhu cike da robobi da gwangwanaye da kwalebe gami buhun-buhuna, ya tadda Uwarshi tana ta sirfa asahar sai kace ba magujiya Ya na wani ciccije baki yace" ke kuma Uwa wai menene? tun daga waje a ke jiyu masifarki ke dawa ye ne ehee!! Ya karashe maganar yana cije baki Tana kokarin zama kan kujerat suyar a warar ta tace"yo ni da waye ne in ba wacan "yar iskar yarinyar ba, ita kuma waccan juyar mai zaman kashe wando ta fito tana min maganar banza, sabida bata san darajar haihuwa ba take fadin wai da hai huwarku gwara babu, shine nake ci mata mutunci,domin ina raye babu mahalukin da ya isa ya tabaku in kyaleshi ko da ko sarkin garinan ne Almusfah" Bai tsaya ya gama sauraran abinda take cewa ba, ya nufi gurin Sadiya gadan- gadan, yana wani irin zagi irin na marasa tarbiya, ya daki kofar gurin da karfi abinka da kofar da babu kwari sai ga ta tabude da kanta, kokari yake ya shiga gurin, Iya tana tareshi yace"dallah iya saurara mana, wannan matar har ta isa ta ai bata mu ko tafada mana magana dan Uwarta! yau sai na farke mata ciki da kwalaba wallahi,ki kyauce kawai na afka mata, sai na nuna mata waye ni, yawa kike Iya!!! "Walidi wato ni ban isa in fada maka kaji bako, yanzu Matar wan mahaifinkan naka zaka cakawa kwalaba,iyi yaushe ka zama haka" Iya tafada tana rirriqeshi Matar Kawu ce tafito jikinta sanye da hijabi hannunta rike da carbi da alama bata dade da idar da sallah ba Tace"Iya sake shi gani na fito yazo ya caka min kwalabar, in ya cika shi mara kunya ne, yau zasu ga gatana daga shi har Uwarshi" kafin Iya ta ankara Walidi ya kwace daga hannuta, ya nufi inda ya jibge buhun shi na gwan-gwan ya ciro kwalbar maltina guda ya basa ta a kasa yayi kan Sadiya cikin zafin zuciya! *YANZU A KA FARA*โ๐ป [22/06, 15:16] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation ๐ธ๐ป๐ธ๐ป๐ธ๐ป๐ธ๐ป โโโโโโ _*GIMBIYA BALARABA*_ โโโโโโ ๐ธ๐ป๐ธ๐ป๐ธ๐ป๐ธ๐ป _*Na*_ _ยฎBINTA UMAR ABBALE_ *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` Zamani Writes Association๐ค๐ป *๐ ฟ30* ______Da gudu Balaraba ta kara so gurin tace"wai kai Walidi me yake damunka ne,? wane irin zafin zuciya gare ka, kanaso ka aikata aikin da nasani a rayuwarka, ni in dai a kai na kuke wannan abin zan tafi in bar gidan sai ku sake a ciki, amma duk tsiya nan ne tushe na, kuma da nan nake gadara,ni wannan masifar ta ishe ni wallahi" Jin furucin da Balaraba tayi yasa Lantana ta mike a zabure ta nufi inda a ke rigimar tace" kai Walidi ka kiyaye ni wallahi, wato kanaso ka jawo mana musiba,ko bisimillah ka caka mata kwalba mugani,wato uwarka tana daure maka gindi ka yi abinda kaga dama,ai uban naka zai shigo ya same ni, ehee"! Ta kalli Balaraba dake tsaye tace"ke kuma da kike cewa zaki bar gidan,gidan ubanki zaki je, kinaso ki kara nunawa duniya dama zaman kanki kikeyi ko, kina min bakin cikin abinda kike bani kullum ta Allah to babu inda zaki je,kina nan kina cigaba da samo min kudi ehee!! Lantana ta karashe maganar tana gyara daurin zaninta Tsaki Balaraba taja kawai ta bar gurin domin cigaba da tsayuwarta a gurin zai ya janyowa ta zagi Lantana ko ta gaya mata magana,shi yasa tabar gurin ranta a bace Uwa kuwa jin abinda Lantana tace yasa ta dinga ga ya mata bakaken maganganu, tace"wallahi Lantana sai tau na kara tabbarwa cewar ke muguwar kwadayayyi yace, wato duk abinda nake miki ba kya gani, ai sai kije ki tayi" Shiru Lantana tayi mata sabida tasan masifar jarabarta, ta mike taje ta dauki buta ta shiga ban daki, batare da ta saurari cin mutucin da take mata ba, *Wannan kenan* *GIDAN SARKI* Yana zaune a lambu dake shashen shi, wasu dogarawa masu manya-manyan riguna da manyan rawani, su biyu suna tsaye a kanshi, daya da wani katon mafici daya kuma a tsaye yana bin gurin da kallo, daga yaji motsin abu zai duba, Shi kuma yana kishin gide kan wani
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108