Skip to content

Chapter 8

Chapter 8

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,232 words 0 views Progress saved
Download Book

ta sanya Suwaibah a gaba tana ta yi mata fada tace"duk Abinda lantana zatayi babu ruwanki da'ita idan mijinku ya fita kine mi izinin zuwa nan gudun fitinar laraba ,sai miyi zamanmu idan ya dawo sai ki koma, Kinji ko? Suwaibah ta daga kai tana zubar da hawaye gami da tuno Dan ginta da "yan Uwanta ,Rayuwa kenan Kafin su watse sai da shatu takara yi mata fada sosai San nan tafito ta tafi Lantana Na zaune tsakar gida tana jiran shigowar ,malam Tanko ,Domin yau ko me za'ayi sai dai ayi taci Alwaashin bazai kwana da Amaryarsa ba tunda ya munafurce ta, Sallau ya shigo fudun! Fudun! Dashi kayan jikinsa duk datti tsabar kazanta jikinshi in banda tsami babu Abinda yake yi Ya zauna kusa da Babarta sa gami da cewa"lantana me kikeyi har yanzu baki je kin kwanta ba ,goma fa ta wuce yanzu" Tace"INA jiran babanku ya shi go Ayi wacce za'ayi" Yace"to Ina Abinci Na"? Lantana tace "kaga sallau !!wane irin Abinci kuma ,zan baka? Da girmanka da komai ,ni yau ban yi girki ba,ka kyale ni inji da Abinda ,ya dame ni" "Gaskiya dole in yi Aure nima nagaji da wannan Abin da a ke mana a gidan nan Abinci ma sai a hanaka" Dubi Yunusa dake shi Ubanshi yana sonshi ai yayi masa Aure ya bashi Abin yi da gurin zama,Amma mu muna zaune, gaskiya da sake ,bari Baban ya shigo yasan wacce zaiyi, shikkenan sai mu zauna muna kallonshi yana Aure Aure ,duk kudinshi su kare ta nan gurin. Sai bayan ya mutu mu tashi a tutar babu" Lantana ta gyara zama tace"Yo dama ai tuntuni nake fada muku Ku San Abin yi wallahi domin Malam baya tataku ,kaima kaje ka nemo matar Aure ,ihe! Duk in da kudi suke yafito dasu yai maka kuma dole ya baka jari da gurin Zama" Sallau yace "ai Abinda zan yi keanan kuma zan fara binkicen a dakarsa ta waccan dakin nasa da baya son Abude nasan da a kwai Abubuwansa a ciki masu Amfani ,zan bi dare Na sacesu ,a kan ya Qarar dasu a banza ba mu mori ko kwabo ba" Wata dariya Lantana ta fara yi cike da Farin ciki tace"shiyasa nake son ka Sallau ,ai kai ne maganainsa wallahi" Sallau tace"wai har an kawo masa Amaryar ne"? Dakin Suwaiba lantana ta kalla tana zabgawa harara ,tamkar da mutum take tace"tana ciki tana jinka munafukar banza! *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š _in kana bukatar cigabansi ga numbar nan_ 08089965176 [04/05, 03:08] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *✍🏻writting by* _*BINTA UMAR*_ *Maman Abdul Wahabu* _RABBI SHARALI SADARI WAYYASIRLI AMRI WA'ALAL UQUDATUN MIN LISANI YAFQAHU KAULI_ *πŸ…Ώ13* Tashi sallau yayi yaje ya dinga buga kyauran dakin ,cikin sigar rashin mutumci ,yana zagin Suwaiba Matar mahaifinshi Lantana tace" kayi min daidai ni dama nasan zaku share min hawaye Na" Sallau yaciga ba da ciwa Suwaibah mutumci yace"Tsintacciya wace tafito yawon karuwanci ,Dole sai kin koma garinku ,Na gado mai sifar bararoji nan ba Nijar bace ,kin zo zaki lashe mu mayya kawai" Suwaiba Na ciki tana kukan wannan cin mutumchi da ,salau ya ke sirfa mata! Motsi yaji daga waje ,yayi saurin barin kofar ,Suwaibah yaje ya zauna kusa da lantana ,duk a zatonsa malam tanko ne, Maman ne ya shi go fudun! Fudun! Yadawo daga yawonshi Na gidan kallo Ya zauna bakin rijiya,yana hamma yace Lantana ina Abinci na? Ban dashi!! Lantana tafada a zafafe tacigaba da cewa"gantalalle gama yawon Na ka zaka tambaye ni Abinci ai ko ina dashi bazan bayar ba" Maman yace"to kar ki bayar mana ai nasan in da yake zanje in diba" Tace"zagina zakayi ne Maman" wato baza ka dai Na yi min rashin kunya ba ko kana gananin Abinda mahaifinku yayi min" "To me zan miki "yafada babu damuwa a fuskarsa yacigaba da cewa "karkari kawai duk abinda matarshi tayi min ko tayi miki in Zane ta ciki da waje" Lantana tayi dariya gami da gyara zama tace" yawwa Dan arziqi irin albarka ,dama haka nakeso nasan kuna sona ,sabida haka. Mutaro mu takura mata kamar yadda mukaiwa wa"yancan yaran suka gudu ,har sai tagaji itama ta gudu da kafarta. Sabida Azabar mu Tace "kai kuma Sallau kabi dare da rana ka kwashe duk wani Abu da yake taqama dashi mu boye, domin baza mu tashi a tutar babu ba" Sallau yace ai ba sai kin fada ba Lantana" Dariya Maman yayi yace"gaskiya Lantana kin San ta kan Mugunta" Ita ma dariyar ta sheqe da ita tana gyara zama tamkar wata sabuwar mahaukaciya tace" ai duk a gurina kuka koya" Tace"bara Na kawo muku Abinci "yayan Albarka" Ta mike tayi kchin tana sambatu kamar tababbiya Suwaibah Na makale jikin kofarta tana jinsu ,Da duk Abinda suke kullawa,tausayin Malam tanko ya kama ta,sai tace"in sha Allahu Allah bazai Baku iko ba" Goma da dara bi Tanko ya shi go gidansa,ya kulle gidan , Abin mamaki Su Sallau ya gani zaune sun kewaye uwarsu kamar masu Neman gafara Yayi sallama Suka Amsa ,ban da Lantana tana can tana kallon Abinda yake hannunsa! Sallau yace Barka da dare? "Barka kadai" Tanko yafada yana kokarin shiga dakin Amaryarshi Sai lantana ta mike taje ta tari hanya ,cikin Neman tashin hankali tace"Malam baka isa ba fa" Cikin nutsuwa Tanko yake kallonta ,Tamkar mahaukaciya yace"lafiyarki kalau kuwa lantana" Rasss!! Nake tafada gami da buga cinya! Tace "bani ledar hannunka ,tafada kamar wata Uwarsa! Abin yabawa Tanko mamaki ,da yake tanko ba ya son raini ko kadan yace"bazan baki ba Lantana ranki zai yi mummunan baci idan baki kauce kin bani hanya ba" Ta buga cinya! Cikin rashin mutumci da rashin kunya tace "bacin rai Na yaushe kuma ,Tanko kajima baka bata min ba,har kaje ka daura Aure batare da sanina ba sabida tsabar muna furci da Annamimanci kuma karasa wazaka Aura sai mayya kuma karuwa wacce ba'san daga in da take ba" To sai dai kazaba ko ni ko ita ihee!!!! Wani bacin rai ne ya turnike Tanko ,wai shi Lantana take zagi a gaban yaransa da matarsa,kawai sai ya fidda hannu ya tsinka mata mari ,ya hankade ta ,tafadi a gurin ya shige dakin Amaryarshi ya mai da kofa ya rufe gamma!! Kuka Lantana ta rusa tana dukan kofar dakin da kafarta gami da zagin suwaibah ta uwa ta uba,makota Na jinta, Sallau ya taso yana kokarin janye ta daga gurin tana fincikewa tace"sallau kaga yadda Malam ya fasa min hanci jini Na zuba ko" Da sauri sallau ya lalubi Cocilan din shi da yake yawo da ita a Aljihu yana haska fuskar Mahaifiyar tashi Ai kuwa ya sata habo gurin marin gashinan jini yana zuba a hancinta. Da sauri yace"Maman zo kaga n" Maman ya taso a fusace ya karaso gurin.yana dubawa Tabbas jini ne yake fita a hancin mahaifiyar tasu, Ganin yadda Maman yake huci yasa Lantana kara lanjarewa tana kuka sabida ta San halin Maman da bakar zuciya! Suka janye ta daga bakin kofar suna rarrashinta ,nan suka yi mata Alkwarin daukar mata fansa a kan Suwaibah tunda duk a dalilinta Malam tanko ya zubar mata da jini ,Abinda bai taba faruwa ba , To suma sun dauki Alkwarin sai

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108