Skip to content

Chapter 37

Chapter 37

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,241 words 0 views Progress saved
Download Book

yayi kad'an yace" ni narasa abunda yake damun wasu matan wallahi, kawai sai tace ka aure ta baka santa,baku taba mu'amala da ita ba, tayaya wannan abu zai faru" "Humm kai ne kake ganin haka, nasan yarinyar ciki da waje, domin waccan shekarar tare mukayi aikin hajji da ita, kuma wata uku da suka wuce da naje Umara mun had'u da ita, sosai ta nace min kullum tare muke tafiya masallaci, sai dare take kyaleni ta tafi ma saukin su, safiya nayi zata zo ta dame ni, shine dalilin da yasa ko sati daya ban cika ba na tattaro kaya na na gudo bata sani ba, sai dai ta shafa taji ba nanan, kai kanka kasan na tsani ta kura" Dariya Maddibo yasa yace"Wallahi baka da kirki "Yan mata suna sonka kai kana k'insu ko zaka fad'a min dalili" *Comment* *Vote and Share* [13/07, 20:43] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^° _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®{REAL BINTU BATULA}👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{RAHAMA ALIYU}``` _ZAMANI WRITES_ _ASSOCIATION_🤝🏻 ```Bisimillahir-rahamanir-rashim``` *🅿48* Maddibo ya cigaba da cewa "yanzu me kace kai akan al'amarin"? " Kai ma kasan halin Baba Waziri,cewa nayi na amunce kawai,ba kaga yadda yake murna ba" "Ya zakayi da rigimar Halisa"? Tsaki! yaja yace" Halisa ba tafi karfi na ba,ina ruwana da rigimar ta tayi, ta gaji, ka manta cewa ba ni ne nace,ina son ta ba, ita wannan din da a ka k'akaba min, sam! ba tai min ba, Siririya ce, babu wani cikar arziki, ka san ba nason mace, haka, dukkanin su babu wacce tai min gwara-gwara ma Halisa tana da wasu abubuwan" Dariya Maddibo yake sosai yace"kana kiran Tafida, da mayen mata,to kai da wane suna za'a kira ka"? Shan kunu! yayi kamar ba shi ba yace"ai gaskiya ce, ganganci ne ka auri mace, wacca baza ka more ta ba,sai dai kai ta fama da kashi da jijiya, wallahi nake fad'a maka,wata macan ko me zaka bata, baza ta yi k'iba ba" Cikin dariya Maddibo yace"kana daga zaune sai zaro magana kake, wallahi matan ka sun shiga uku, kai dai" Tab'e baki yayi ya mik'e tsaye tsaye, yace"babu ruwana dasu a cikin su duk wacce tafi kyautata min itace taurarowa ta" Mikewa Maddibo yayi yace" Zanje fada mu gaisa da Maimarta ba, idan naga da sukuni zan shigar da maganar Balaraba" "Allah ya bada sa'a" Sarki yafada ya cigaba da cewa"nima wanka zan shiga zan futo yanzu" Lokacin da Maddibo ya isa fada, bata cika sosai ba, daga Sarki sai Waziri da Wambai sai Wasu fadawa su hud'u , Maimarta ba yana zaune kan kujerar shi, suna magana da Waziri, duk dai a kan Sarki! ne, Waziri yace"d'azu munyi magana dashi yace ya amunce, yanzu abunda zamuyi shine, zamu aika da takkada gayyata gare ta kan tazo su gaisa dashi, muna bukatar ta zauna tare damu, domin ta koyi irin al'adunmu sabuda kasancewar kowane gari da irin tasu sarautar" Jin maganar da Waziri yake tasa Maddibo faduwar gaba! kalubale na farko kenan, Cikin nutsuwa da dattako yayi sallama fadar kanshi a sunkuye ya zube! yana kwasar gaisuwa Da murmushi a fuskar Maimarta ba yake amsa wa yace"da alamu akwai magana a bakin Ubana, Maddibo d'an Maddibo kuma Uban Maddibo" Murumushi Maddibo yayi ya karasa gaban Maimarta ba kanshi a sunkuye,yace"Allah shi taimake ka, nazo muku da wata magana me muhimanchi ina fatan zaku karb'eta hannu biyu" "Masha Allahu" Maimarta ba yafada ya cigaba da cewa"nasan ko wace irin magana zats futo daga bakin ka mai muhumanchi ce Ubana,ina sauraron ka, tare da sauran iyayen naka" Yafada yana kallonsu Waziri dake zaune duk sunyi shiru Da sauri Wambai yace"kwarai kuwa Allah shi taimake ka, muna sauraron ka" Shiru Waziri yayi irin na kara, amma ya k'agara Maddibo ya fad'i irin maganar da yazo da ita cikin fada wacce ya kasa fad'a masa ita a matsayin sa na wanda ya haife shi, Cikin nutsuwa Maddibo yace"Allah shi taimake ka na samu matar aure insha Allahu, ina so a aika gidan su domin a tsayar da magana" Kafin Maimarta ba yace komai, Waziri yace" "yar wane Sarki ce a fad'in duniyar nan, ina fata bakaje kayi mana jajibe-jajiben " yayan bayin mu, ba wato talakawa" Shiru fada tayi, sabuda Waziri ya karya dokar fada,bai bari Maimarta ba yace komai ba, ya fara magana, daga baya da yage b'arnan da yayi, sai ya d'an runk'ufar da kanshi yace"Afuwa a gafarce ni ranka ya dade" Minti biyar Maimarta ba bai ce komai ba, daga bisani ya d'ago kai a nutse yana kallon Maddibo yace"kaje ka cigaba da neman yarinyar zamu sa a je ayi bunkice, babu ruwan mu, da cewar "yar talaka ce,ko " yar mai kudi ce, ko "yar sarauta ce, duk wannan basa gaban mu, nagarta da kyawawan halaye shi zamu duba, Allah yasa za'ayi damu" daga fadin haka,sai yayi shiru, amma fa fuskar shi babu walwala dalili Waziri ya b'ata masa rai, sam! ya tsani halayen dan Uwan nashi kwata-kwata baya kaunar talakawa, tun jiya yake tunanin maganar da yayi masa akan Sarki! da d'iyar Sarkin Yalwa, yasan da akwai wani abu a b'oye wanda shi Wazirin yake son cika wa, amma koma meye ya barwa Allah domin ya fisu sanin abunda yake lullub'e. Cikin farin ciki Maddibo ya mik'e yana godiya, Maimarta ba ya dakatar dashi da hannu, yace"ka zauna a fada na lura tunda ka dawo baka zauna ba,kai ma ka koyi d'abi'un d'an uwanka, yau in ya zauna a fada gobe ba zai zauna ba" Komawa yayi ya zauna gami da tankwashe kaf'a yace"Allah ya taimake ka" "Ko kana da wani Uzirin ne"? Maimarta ba yafada yana kallon shi " A'a babu wani uziri a yanzu, ranka ya d'ade" Shiru Maimarta ba yayi yak'i sakin fuskar sa,sabuda abunda Waziri yayi ya bashi haushi, nan Wambai ya fahimta yace"Waziri ya na neman afuwa ranka ya dad'e" A nutse yace"Ai ya nuna min bani ne uban d'anshi ba,tunda har ya kasa hakura in fad'i magana sai da ya fad'i tashi" "Tuba nake, a busa kuskure ne,ranka ya dade a gafarce ni" Waziri, yafada yana jin wani mugun bak'in ciki, a zuciyar sa, dole ne ma yasan yadda zai yi ya kawai da mutumin nan daga karagar mulki,tunda ba danshi kad'ai a ka hallice ta ba, shima yana da gadon sarauta kamar yadda yake da ita, babu yadda za'ayi ya dunga nuna masa mulki, amma babban abunda yake bashi mamaki da d'aure kai shine duk sanda yayi niyar aiwatar da wani abu a kansa,daga ya had'a ido dashi sai ya kasa, ya rasa wane irin kwarjini yake masa. Haka fada tai ta tafiya, har lokacin sallahr la'asar, Maimartaba ya mike a nutse domin shiga masallaci, Suna dawo wa fada Maimarta ya aika ai masa kiran Sarki! Lokacin yana wani k'ayataccan lambu wanda yake hutawa, yana kishin gid'e kan wani lallausan kafet,da wani tumto mai kyau da taushi,anyi masa ado irin na sarauta, gefe ga kayan marmari nan burjik, amma ko daya bai dauka yaci ba, yau baya buk'atar kowa ya rab'eshi shi kad'ai ya ke zaune a gurin, wata irin iska na kad'awa mai dad'i, wayar shi ca hannu shi ya kura mata ido ko k'iftawa baya yi, *Niko da san

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108