Skip to content

Chapter 73

Chapter 73

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,261 words 0 views Progress saved
Download Book

kawo masa matsala fa, yayin da buk'atarsa ta kusa cika Sunyi mamakin abunda Waziri yayi,zahiri ya nuna mulki yake so,Sam mutuwar d'an uwansa ba itace a gabansa, wannan ya k'ara bawa Sarki! K'warin gwiwa da son sha'awar mulki abunda bai dame shi ba,a da yana so yanzu su fafata da Waziri, Allah yaba mai rabo sa'a. Sai bayan sallahr isha'i Sarki! Ya shiga gida kai tsaye shashen Mamansa ya nufa,yana tafiya cikin sanyi jiki, ji yake duk duniyar tayi masa zafi, Lallai d'an adamu ba abakin komai yake ba,dubi irin hukuncin ubangiji,wata guda yayi rashin mutane biyu da bazai tab'a mantawa dasu ba a tarin rayuwarsa. Balaraba da Mama Fulani da tare da Madabo,da Halisa,da Azima da wasu mata biyu, sai jakadiya Shafa'atu wacce take kusa da Mama Fulani tana b'are mata lemon zak'i,domin ta kasa cin komai, wani irin d'aci take ji a bakinta, da k'yar ta dunga shan lemon har tasha guda uku. Da sallama ya shigo, falon Suka fara rige-rigen gaishe shi,da yi masa gaisuwa,amsawa yayi sama-sama ya shige turakar mahaifinsa. Ko da ya shiga kwanciya yayi kan gadon me Martaba,ya d'auki rigarsa da ya rasu da ita a jikinsa,ya rungume ta,k'am wasu zafafan hawaye suka fara zubo masa. Shikkenan Moddibo ya tafi me Martaba ya tafi,sun barshi shi kad'ai hakika duniya abar tsoro ce,hakama abun jikinta Kuka Sarki! Yake sosai,kukan da bai tab'a yin irinsa ba, hak'ika yanzu yana buk'atar me rarrashinsa domin ji yake zuciyarsa zata iyayin bunduga, shi musulmi ne, dole ya yarda da mutawa da rayuwa yasan mutuwar wannan mutane biyu, babu wani mahaluki da ya isa ya tare ta sai,Allah domin shine ya hallice su, amma ya karb'i abunsa, shima kuma na hakane, yanzu kawai addu'arshi itace Allah ya sanya masa dauriya da jarumunta a zuciyarsa. Kamar a mafarki yaji muryarta a kansa,tana kiran sunan sa. Bud'e idonsa yayi dukansu ya sauke a kanta Wani irin yarrrr taji lokacin da suka had'a ido ganin yadda k'war idonsa ta koma wata kala,tayi jazur kamar Jan gauta. Wani irin tausayinsa ne ya tsirga mata,itama sai taji hawaye yana k'okarin zubo mata,daurewa tayi kawai,a zuciyarta tace"Maraici babu k'arya a cikinsa,komai girma komai dukiyarka, ka rasa iyaye kayi babban rashi,yanzu zai fara jin irin ciwon da take ji a zuciyarta na rashin iyaye. Lumshe idonsa yayi yana jin tamkar ya kamo ta ya rungume a jikinsa ko ya samu sassaucin abunda yake ji a zuciyarsa,hak'ik'anin gaskiya yanzu Wanda zai rarrashe shi yake nema. Cikin taushin Murya tace"Ka tashi inji Mama kaci abunci,tace inyi k'okari in baka kaci kafin ka kwanta" Yana jinta yayi shiru abunsa, wani sanyi irin na zazzab'i yana k'ara ziyartarsa. Ta kure jikinsa yake yana neman bargo domin ya lullub'e jikinsa. Duk tana kallon abunda yake yi, muryar ta na rawa tace"Don Allah ka tashi kaci abunci kaji ko, bana son abunda zai damu Mama,ina tausaya mata da halin da take ciki,kar ka k'ara sanya mata wata damuwar tunda kasan rashin cin abuncin ka zai d'aga mata hankali, ba kai kad'ai kayi rashi ba,har damu,ni ina ganin kamar ni akayiwa mutawar ma" Ta k'arshe maganar tana goge hawaye da suka zubo mata. Yana lullub'e cikin bargo yace"A k'oshe nake,ko na tashi babu abunda zan iya ci, kiyi tafiyar ki kawai nagode" Girgiza kai tayi kamar zatayi kuka ta zauna gefan gadon ba tare da wani tunani ba ta kama bargon tana k'okarin cirewa daga jikinsa, bargon ya rik'e ya had'a da hannunta, yana girgiza kai,alamar ta sakar masa Girgiza kanta tayi itama kamar yadda yayi mata, komawa yayi ya kwanta kawai ya rufe idonsa, Kallonsa tayi taga yadda kwarmin idonsa suka zurma ciki sai girman k'war idon,sai kace Wanda yayi wata yana lalura, ba tasan sanda hawaye ya fara zuba daga idonta ba,wannan tausayi ta rasa daga ina yake zuwa, babu komai a zuciyarta face tsagwaron tausayin Sarki!Almansor. Sheshshek'ar kukanta yaji yasa ya bud'e idonsa da Sauri, yana kallonta,tayi saurin kauda kanta,tana k'okarin mik'ewa daga kusa dashi, ya ruk'ota da Sauri ya rungumeta tsam-tsam yana wata zafaffafiyar ajiyar zuciya! https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*GIMBIYA BALARABA*_ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* ```MARUBUCIYAR``` *NANA KHADIJA* *YARO DA KUD'I* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* _*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_ _________________________ ```We are here to educate, motivate and entertain aur Reades``` _________________________ _*DEDIGATED*_ _*TO*_ _RAHAMA ALIYU_ _________________________ 🕺🏼🕺🏼🕺🏼 *NAMIJIN DUNIYA* 🙆🏿🙆🏿🙆🏿 *Story & writing* *By* *Aunty Mamie* _________________________ _Ina masoya wannan novel d'in, Aunty Mamie na gaida ku, kuma tana muku fatan alkairi, gaba d'ayan Ku, wannan novel d'in mai suna Namijin duniya ya koma na kud'i dan haka duk me buk'atar ci gaba da karanta shi sai ya tuntub'i wannan numbar_ 08166526167 _________________________ *🅿85* K'okarin k'wace kanta take daga jikinsa, ya rik'e ta tsam a k'irjinsa,sai sauke ajiyar zuciya yake,zuwa can taji d'igar wani abu me d'umi a bayanta, hannuta tasa ta shafo,taji ruwa, Wannan ya tabbatar mata da cewar hawaye ne, tunda take dashi bata tab'a ganin kukunsa ba sai yau, itama zuciyarta sai ta karye,babban mutum kamar Sarki! yana kuka lallai tashin hankalin ya kai inda ya kai. Sunfi minti biyar rungume da juna, sai da taji jikinsa yayi sanyi sannan ta zare jikinta daga nasa,tana kallon fuskarsa, lumshe idonsa yake amma ba bacci yake ba, tana kallon yadda yake cije bakinsa,kamar wanda yaji ciwo me zafi. Jikinta a sanyaye ta futa daga d'akin. Tana zama Mama Fulani tace"Ina fatan kin bashi abunci yaci ya k'oshi"? Balaraba bata iya k'arya ba,dan haka kawai sai ta girgiza kai alamar A'a. Tace"Mama nayi-nayi ya tashi yaci yace a k'oshe yake Wallahi" Mama Fulani tace"Nasan dama abunda zai ce kenan, sam baya son cin abunci, tun safe a ce mutum babu abunci a cikinka, sai damuwa Allah ya kyauta" Balaraba dai Shiru tayi tana tunanin abunda ya faru tsakaninta dashi. Halisa ce ta mik'e da sauri tana kallon Mama Fulani tace"Bari inje in gwada bashi ko zai ci" Mama tace"Aikuwa da kin kyauta" Madabo tayi murmushi, tace"Ai dama ko wace mace da irin hikimar ta,da kin sani tun farko ita kika tura ba waccan ba, ita har yaushe ma suka shak'u da shi" Mama ta gane magana Madabo ta fad'a mata, tabbas Madabo baza ta canza halinta ba, na fad'ar maganganu da habaici. Halisa ta shige d'akin da Sarki yake cikin gadara. Azima kuwa tana zaune tamkar ta d'ora hannu aka, ta lura babu Wanda yake sonta, Balaraba tana da fada,gurin Mama Fulani, Halisa kuma "yar uwarsa CE, ga uwarta a tsaye a kanta, itama dole ne ta zage damtse gurin ganin ta kafa gwamnatin ta. Mik'ewa tayi itama tana shan. k'amshi ta kalli Mama Fulani tace" Bari in shiga in duba jikin nasa" Mama Fulani tace"A fito lafiya, kuyi k'okarin bashi abunci dai" Azima tace"Insha Allah Mama" Wucewa tayi ko kallon inda Madobo take batayi ba. Balaraba kuwa a manakinsu take in taga suna wani rawar jiki a kansa,abunda baza ta tab'a iya wa ba kenan, shi kuma dasuke domin shi, baya wani damunsa gwara ma Halisa yana sauraranta. Halisa na zaune kusa da k'afafunsa, tana masa magana k'asa-k'asa,yana jinta yayi mata shiru, hannunsa ta rik'o tana fad'in "Yallabai ka tashi kaci abunci don Allah kar ka kwanta da yunwa" Ranshi a b'ace ya bud'e idonsa ya mik'e zaune yana hararata, saurin sakar masa hannu tayi, yace"Wai ni yaro k'arami

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108