Chapter 4
Chapter 4
sai ta ganshi. Gefe can taja ta tsaya domin yadda a ke bangajeta gashi Sam Sam bata son hayaniya da jira da tana da damar tafiya da tayi tafiyarta wallahi domin kwata kwata bata son batawa kanta lokaci sanin da tayi cewar kannanta nacan na jiranta a gida, To ganin yadda makarantar ta karramata a matsayinta na daliba ta farko yasa bataso ta watsa musu kasa a ido Duk a zaton ta Sulaiman Ahamad shine na farko ganin yadda yake da kokari domin ko musa bakace shine yake cinyewa Amma Abin Mamaki sai taji sunanta a farko ,Tabbas ta yadda da kanta tunda Ita kanta tasan tana da masifar kokari domin wani sa'in itakewa "yan ajinsu kari idan malami bai shigo ba ita dai kyaleta da rashin kunyarta da gadara gami da takama gashi ita kuma ba "yar gidan kowa ba! Da kyar bushira ta hangi Sarki! Daga can nesa sai ta riqa mamakin ganinshi jin Balaraba nace da ita ae yaro ne Lallai Balaraba da son girma take cikin zuciyarta tace gaskiya yana da kyau wai!! Dole yaji dakanshi duk da cewa bai fiye haske ba amma kalar fatarshi abin kwatance ce ga wani uban saje da yabi ya kewaye fuskarshi a tsare hade da mitsitsin bakinshi idonshi Manya farare tas dasu sun Dan risina kadan bazaka taba gane girmansu ba sai ya bude masu duka Amma idan ka kalli saman fatar idonshi zaka gane yana da Manyan idanuwa a sabila da dimun'da'iman idan nashi a lumshe yake ba yadda ya bude su sabida shi kanshi yasan Allah yayi masa baiwarsu . Tun kan ta karaso gurin Balaraba take zabga mata harara tace"wallahi Sam Sam ba kuyi ba kun zubar mana da qima kuna mata kuriqa rububin zuwa kallon wancan waishi Dan sarki Mtssss Wallahi babu da Namijin da zanyiwa wannan rawar jikin ba'a haifeshi ba tafada a zafafe tanaji tamkar taje ta gaggaurawa matan dake rububin zuwa ganin shi. Kallonta Bushira tayi tana Mamakin Balarabar da yadda ta dauki kanta ita ba "yar kowa ba I dillalin kashi. Tace"laifi ne Dan munje ke tunda bazaki ba ae shikkenan ,humm gaskiya ya hadu duk da banganshi sosai ba tabbas nasan yana da mugun kyau. Tsaki Balaraba taja tace kyawunshi din baza bai dameni ba ni nan Sam Sam kyauwun wani Namji bazai rude ni ba ko wata sarautarsa tafada tana girgiza jiki gami da ji da kanta Dariya Bushira tayi kadan tace" Wallahi wannan Abinda kekeyi yana mutukar bani Mamaki wai ko Dan kinga kina da kyau ne? Banza Balaraba tayi mata tana hura hanci! Bushira tacigaba dacewa Dan kinsan bazaki taba samun kamarshi bane a matsayin Miji shiyasa kike ta wannan Abin" "Wani kallon Tara shaura kwata Balaraba tayiwa bushira tana ya mutse Fuska tace " Billahillazi kika sake yimin wannan Furucin sai na fasa miki baki ae kin San zan iya ko"! *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* πππππ [04/05, 02:52] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? π§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββ *πΎGIMBIYA BALARABA*πΎ π§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββ *βπ»Written by* _*Binta Umar*_ ~*MAMAN ABDUL WAHABU*~ ~*MRS AHAMAD GWADABE*~ _*WANNAN BOOK DIN NA SIYARWA NE NAIRA DARI BIYU IN KANA BUKATAR CIGABANSHI GA NUMBAR NAN*_ 08089965176 *π Ώ6* Bushira tace"idan baki fasa basa min baki ba kya tsoran Allah Mtss ke daga anyi magana sai kiriqa nunawa mutane gadara Aikin kawai! Shiru Balaraba tayi mata ganin rantaya baci Sam bata son bacin ran Bushiran sabida ita kadai ce ta iya zama da ita take jure halinta ,tace"Ai sai ki shige mutafi ni wallahi nagaji da tsayuwar gurin nan wai sai yaushe za'a tashi tunda dai Maimartaba ya tafi ba shikkenan ba kowa sai ya yi nasa guri" Tafada tana wani daga kai! "Sai dai ke kiyi tafi Amma ni bazan biki ba ke kullum ba kya gudun Abin Magana duk da halinki Amma haka A ka karramaki gurin nan gashi kina nema ki watsawa mutane qasa a ido"Bushiran tafada tana dauke kai daga kanta Gaba tayi kawai ta kyaleta tsaye a gurin tace "Sai kin tawo ae wallahi bazan zauna ina bata lokaci Na ba kinsan su Sadiya nacan A takure babu Mai basu Abinc......kafin ta karasa Sallau ya tari gabanta Cikin yaqe yace"diyata yarinyar Albarka ina Alfahari dake" Gabanta ya fadi!! Sai ta dake tace"Kawu Ashe kazo gurin saukar banganka ba sai yanzu" Washe hakoransa yayi yace"ae nazu tuntuni a gaban idona Maimartaba ya fito duk ina kallonshi har ya koma cikin gida yafada yana ta dariya Mara dalili domin kana ganin yadda yakeyi kasan karfin hali kawai yake "Allah sarki Kawu wato kazo Ashe Amma kanajin lokacin da Maimartaba yake fadin ina waliyyina yake yafito domin ya karbar min kyautittika Na kayi shiro ko? Tana sane tayi mashi Magana domin taga Halin da zai shiga sanin da tayi basu da Makiyi sama dashi da iyalinshi duk da yana Amatsayin wan Mahaifinta. Duk sai ya diririce Sabida yasan yarinyar "yar zafin kai ce duk da cewar bata masa rashin kunya Amma yana shakkar ta yasan kallonsa kawai takeyi gashi shi kullum nuna mata yake Ubanta ne shi tunda ba ran Mahaifinta, Amma duk wani hakkinta yakasa daukewa Asali ma da hadin bakinsa A ke muzguna musu a gidan ita da "yan Uwanta. Sai ya hau dudduba jikinsa yace"dube ni fa Balaraba babu sutturar Arziqi kunya nakeji shiyasa ban fito ba"yafada bakinshi na rawa kai daganin yadda ya yi maganar kasan tsari ne kawai da Rashin gaskiya Bata ce komai ba kawai ta hau duba kayan jikinshi. Tace"Kawu kenan kowa ae da sandar hannunsa yake kai duka maye laifin tufafinka yanzu gaskiya banji dadi ba wallahi ni kai dai a guri kowa da "yan Uwanshi da iyayenshi ban dani duk su Kawu Habu da Kawu Maman da Kawu Salisu babu Wanda yazo gurin Harsu Safiya da Mabaruka ma haka ai shikkenan tafada tana daga kafada , Duk sai ya rasa Abin fada Sabida babu gaskiya yace"kin San wa "yan nan basa son Zumunchi kowane shege sai yace kasuwa zai tafi su kuma su Safiya da kike magana a kan su kin sansu da shegen son kudi kamar jaraba suna can suna Aikin A wara da kulelensu kamar ko da yaushe" "To Kawu ina Uwa da Iya su mai yasa basu zo ba? Tafada domin taji mai zai ce domin tasan bata bakinta takeyi sabida tasan bazuwa zasuyi ba Lokacin da sukaji Labarin saukar cewa suka dinga yi ae saukar zuqu ce wannan. Yace "ke ma dai Balaraba kin san wa"yannan tsinannun Matan baza su zo ba su Neman kudinsu ya fiye musu komai ki rabu da waddanan "yan hassadar ,yafada yana kokarin karbar Allon hannunta gami da kyautitikan hankalinshi na kan Mukkalan gidan da shagon sai faman washe baki yakeyi *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* ππππππ [04/05, 02:52] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? π§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββ *πΎGIMBIYA BALARABA*πΎ π§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββ *βπ»Written by* *Binta Umar* ~*MAMAN ABDUL WAHABU*~ *MRS AHAMAD GWADABE* _*WANNAN BOOK DIN NA SIYARWA NE NAIRA 200 IN KANA BUKATAR CIGABANSHI GA NUMBAR NAN*_ 08089965176 *π Ώ7* _Bissimillahi_ Sakar mishi tayi tana bin shi da kallo ganin yadda jikinshi yake rawa Humm Kawu kenan tariga ta Fahimchi Abinda yake wa Yace"Diyar Albarka gaskiya ina Alfahari dake da Dan Uwana Ayuba da ya hafeki Allah yajikanshi ya gafarta masa "Ameen
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108