Chapter 57
Chapter 57
yana taya ta,ita kuma Balaraba sai fad'a take mata. Ko da Sarki! suka sauka k'asa da Halisa, zamansa yayi a inda ya tashi,ta k'araci k'orafe-k'orafen ta,bai ce mata komai ba, haka ta mik'e tana niyyar tafiya ranta duk a b'ace! ya d'ago kai a tsanake yace"koma ki zauna zamuyi magana" Komawa tayi ta zauna, ya aje littafin dake hannusa,fuskarsa babu yabo babu fallasa yace"kin san Gimbiya Azima,"yar Sarkin Yalwa"? Gabanta ya fad'i! jin sunan wacce ya fad'a ita kuwa tasan Gimbiya Azima,domin abokiyar fad'anta ce, basa shiri ko k'adan dalili kowa yana ji da izza! gami da tak'ama. Bakinta na rawa tace"Eh nasanta" "Yawwa itace zata zama abokiyar zaman ki in Allah ya yarda" Wani irin yarrrr! ta ji ajikinta lokacin da taji abunda yace mak'ogaron ta ya bushe k'amas, tace"ban fahimci abunda kake nufi ba" Wani irin kallo yayi mata yace"kin San bana magana biyu, kije kiyi tunanin maganar dana fad'a miki" Kuka ta fashe! dashi kamar wacce a ka aiko mata cewar uwarta ta mutu, tace"yaushe har a k'ulla wannan al'amarin ban sani ba,kuma mahaifiyata bata sani ba,Dan anga cewar ita macace shiyasa har ake abu batare da saninta ba,wannan ai yaudara ce" Cikin kuka ta k'arashe maganar. Ransa a mugun b'ace ya d'ago Kansa ya zuba mata idonsa,masu kwarjini,tuni tayi k'asa da kanta tana sharar hawaye Yace"dukanin ku ke da ita Azimar babu zab'ina a ciki, ke kin kasance zab'in Mamana,ita ta kasance zab'in Waziri, duk zan aure ku ne ba dan inaso ba,sai dai n in cika umarnin magaba tana" Shiru yayi na minti biyu ya cigaba da cewa na fad'a miki ne saboda ki sani kuma ki shirya, saboda kin fi kowa sanin halina bani da munafurci kuma bana san hayaniya, da fitina,wanda na lura ke haka halin ki yake tada zaune tsaye, idan anjima zata zo nan domin ta kawo min ziyara zan tara Ku guri guda dake da ita,ku fahimci junanku, kar wata b'araka ta futo daga gare ki, nasan halinki, in xaki kwantar da hankalin ki ki kwantar domin ke da ita ba da ku kad'ai zan zauna ba,kin fi kowa sanin yaya tsarin masaraurmu yake" Kuka mara sauti Halisa take,lallai tana cikin tsaka mai wuya, yanzu ta tabbatar da cewar Baba Waziri baya k'aunarta tunda har ya had'a "yar abokinsa aure da masoyin ta, ita da take burin taci lokacinta ita dashi kafin ya kawo wata,tasan ta more kuma sunsha soyyaya, yanzu ko auran a kayi tilas su raba kwana ita da Azima. Tunda ya gama maganar shi,ya kishin gid'e kan kujerar ya lumshe idonsa Allah kad'ai yasan abunda yake damunwa, yana jin kukan Halisa yak'i k'arewa ya bud'e idonsa wanda suka d'an yi ja kad'an, yace" kin cika min kunne fa da gunjin kuka, kije ki tambayi Baba Waziri yadda a kai haka ta faru tunda na lura ke baki da kunya, har kina cewa an yaudare ku" Yadda ya fad'i maganar da yanayin b'acin rai! yasa ta gane tayi kuskure domin Sarki! mutum ne wanda baya saurin nuna b'acin ransa da wuri, in ransa ya b'aci a yanayin maganar sa zaka gane, mik'ewa tayi ta nufi kujerar da yake zaune, ta rab'a jikinta a jikinta harda langwab'e kai, ta rik'e hannusa guda, d'aya, tayi k'asa da murya ta sosai tace" Allah ya huci zuciyar Habibi na, zuciya tana azabtuwa da so da k'aunar ka, shiyasa na rasa tunani na,lokacin da naji wannan maganar,ina kishin ka,mutuk'a bana k'aunar ko wace mace ta rab'eka sai ni,amma ina ganin burina bazai cika ba, Habibi nasan Azima ciki da waje,zata aure ka ne da wata manufa,a zuciyarta, gaskiya banso Azima zata kasance matarka ba, amma tunda haka Allah ya hukunta mama zan cigaba da tayaka addu'a" Yanayin yadda tayi masa magana a nutse yasa yaji ta bashi tausayi, gyaran murya yayi gami da d'an gyara zaman sa,a nutse yace"ki koma inda kike mana, na hanaki irin wannan" Muryar shi bata futa sosai yayi maganar, Mik'ewa tsaye tayi tana gyara alkyabarta tace"tafiya ma zanyi,yanzu sai anjima zan shigo,da kamar k'arfe nawa zata zo"? Tafad'a cikin sigar tambaya. "Hud'u zuwa biyar na yamma" "Shikkenan to" Tafad'a a sab'ule jikinta babu kuzari ta futa daga falon To,can gidansu Balaraba kuwa,babu wanda ya damu da rashin dawowar ta gida da wuri har wajan k'arfe tara da rabi na dare bata shigo gida ba, Iya hankalinta ya tashi ta futo ta nufi d'akin Sadiya matar Kawu suna maganar,can sai ga Sallau nan ya shigo fud'un-fud'un yana sab'a babbar riga, Iya ta tare shi cikin damuwa tace"Sallau har yanzu Balaraba bata shigo ba,babu ita babu yaran" Da sauri ya kalli k'ofar d'akin nata, cikin mamaki yace"to ina ta tafi mutsiyaciyar yarinya,me shegen yawon tsiya,ai gwara in aurar da ita,kar ta jawo min masifa" Lantana ce ta bankad'a labulen d'akinta ta futo da futular k'awai a hannunta, tace"wai zancan me nakeji ne" "Wannan munafurkar ce bata shigo gida ba" Lantana tace"Oho! dai a banza, duk inda ta shiga ta dawo,dole ace da mijin iya baba mune dai tilas d'inta, ehee"!! Sallau yace"ai ko guduwa tayi bazan fasa abunda na shirya a kanta ba, sai na d'aura auranta da Iro" Lanatana tace"kayi min dai-dai, da taje ta jawo mana abun fad'a" Uwa! na daga cikin d'aki tana sako baki, bak'in ciki da b'acin rai yasa Matar Kawu komawa gurin ta, Iya ma d'akinta ta koma tana addu'ar Allah ya tsare mata su Balaraba duk inda suke. Lantana Sallau Uwa su Shamsiiya baccin su sukai babu abunda ya dame su. Sab'anin Iya da matar Kawu baccinsu rabi da rabi ne, saboda fargaba, Asubar fari suka dunga jin bugu, a gigice Sallau ya diro daga gado,babu salati babu komai yaje ya zare sakata, yana hamma! Idonsa duk kwantsa abun k'yamk'yami! d'an aiken gidan me gari ne yazo, Sallau gabansa ya fad'i yace"lafiya dai ko"? D'an aiken yace"me gari yace"kazo yanzu-yanzu me Martaba ya aiko yana neman ku" Saura kad'an ya fad'i saboda razana da yayi,baki na rawa yace"me nayi ni Sallau"? D'an aiken yace"Ai ba kai ka dai zakaje ba tare dashi zaku" Ihu! ne kawai sallau ba kurma ba,ya shige gida cikin tashin hankali! *Muje zuwa* [02/08, 18:14] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ _*DEDIGATED*_ *_TO_* ```RAHAMA ALIYU``` ```BISIMILLAHIR- RAHAMANIR-RAHIM``` *🅿65* Lantana ce ta futo daga d'aki hannunta rik'e da butar alola, taga Sallau ya shigo wurjajan, kafin tayi magana ya tare,ta yana cewa "Lantana masifa ta same ni ,yanzu aike ya same ni,cewar muzo ni da me gari wai me Martaba yana neman mu" Sakin butar tayi tafadi a gurin saura kad'an zaninta ya fad'i k'asa saboda tsorata da tayi,salati take tana sallalami, cikin tsora tace"Allah yasa ba wani laifin kayi ba" Yace"yanzu dai zanje in ji, d'aki ya shiga yana tashin Uwa,ya fad'a mata halin da ake ciki,ko a jikinta ta koma tai kwanciyar ta Wani kud'addan yadi ya d'auko ya sanya a jikinsa,ya d'auki wata daud'add'iyar hula ya kwafa a kansa ya futo da sauri,har yanzu Lantana na tsaye a tsakar gida,jikinta duk yayi sanyi, tarasa abunyi,ta kalli Sallau lokacin da ya futo,tace"Nifa inajin wannan shegiyar yarinyar nan ce ta ka k'arar ka gurin Sarki kasan ba kunya ce da ita
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108