Chapter 40
Chapter 40
ya rik'e hannunta yace"nagode Yaya Allah ya biya miki bukatun ki" "Ameen" Balaraba tace ta mayar da hankalin ta kan Iya, tace"Iya sannu da jiki" Kai kawai Iya ta iya d'agawa "Bari in d'auko miki hijab muje Chamis kinji" D'aga kai ta kuma yi a karo na biyu. da taimakon Balaraba Iya ta mike tasa mata hijab d'in ta rok'ota suka futo, Su Sadiya nan suka zauna jiran dawowar su Kasancewar Walidi ya futa daga gidan yasa Lantana yi musu wani kallo shek'ek'e tace"munafurcin banza da wofi, zaki lanjare kice baki da lafiya, duk kuje ku gama munafurcin naku ku dawo ku same ni nice dai Lantana ban can zaba Babu wanda ya kulata cikinsu Uwa! lokacin tana band'aki, sai ita kad'ai a zaune a tsakar gidan, suna futa suka ci karo da Sallau ya dawo,tun daga bakin lungu a kasanar dashi abunda ya faru a gidan, cikin tashin hankali ya shigo gidan, Yaji dad'in ganin ta a sabuda haka sai ya ja tsaya yana surfa mata ashar yace"bantab'a sanin ke "yar daba bace sai yau, duk ikirarin da mutane suke a kan " yayana cewa suna harkar Daba! a she ba haka bane, duk abunda ya faru d'azu ina da labarin sa, to bari kiji wani abu da baki sani ba, duk k'iyayyar da kike wa Iro shine dai mijin ki ko kink'i ko kinso sabuda haka dole ne zakije har d'akinshi ki bashi,hakuri idan kuma kink'i sai dai kije ki nemi wasu iyayan bamu ba, domin ni nan da kika ganni sharri na yafi kala dubu,wallahi duk inda kika shiga,sai naje na b'ata miki suna" Ya karashe maganar a zafafe! Da kyar! Iya ta bud'e baki tace" haba Sallau bai kamata kafad'i wannan maganar ba,kamata yayi kabi ba'asi kafin ka yanke hukunci, me Iro yayi mata har ta d'auki mataki a kanshi, ni duk da akwance nake a d'aki bana jin dad'i hakan bai hanani na jiyo abunda yake faruwa ba, da Iro da Balaraba duk naka ne, in dai adalci ake" "Ke Iya rufe min baki, bana son hauka, me zai yi mata kuwa? wanda har zata d'auki wuka ta cire masa d'an yatsa, wallahi sai kin biya kud'in magani yanzu-yanzu, domin yana can Chamis za'ai masa d'inki, duk abunda ya faru shi Iro da kanshi yaje ya fad'a min komai, ni sam banga wani laifi a nan ba, dan yayi yunkurin tab'a jikin ki sabuda shine mijinki, dama kuma addini ya hallata cewar namiji zai iya tab'a jikin matar da zai aura kafin auren domin ya san wace iri ce matar gudun abunda zai je ya dawo, sabuda haka bayan kin biya kud'in maganin shi zakije ki bashi hakuri har shagonshi, kamar yadda na fad'a a farko" Cikin mamaki Balaraba take kallonshi, jin abubuwan da yake fad'a bata tab'a yadda Kawu Sallau mugun jahili ne ba irin yau, a wace mazahabar a ka yadda namiji ya kusanci mace kafin auransu, itakam bata tab'a jin wannan k'aulin ba, Iya tace"to kayi hakuri mu dawo sai mu yi maganar in sha Allahu zata bi umarnin ka kamar yadda kake so" Kaucewa yayi ya basu hanya yace"kuje ku dawo ku taddani ina nan ina jiran ku" Suna futa shi kuma ya shige gidan yana zage-zage kamar wani mahaukaci, Lantana ta mik'e zaune tana taya shi zage-zage tace"ashe kaji abunda ya faru ko? "E naji ai shi Iron yaje ya fad'amin, duk abunda ya faru,kuma ina shigowa unguwar ake ta tarata ana fad'amin" "Hummm! kagani ai sai ka d'auki mataki akan ta in ba haka ba kuwa sai dai kazo ka tarar ta kashe mu,a gidan dan yarinyar ta zama abunda ta zama, a duniyar nan" Nan Sallau ya zauna kusa da mahaifiyar tashi suna k'ara maimaita maganar, Uwa!ce ta futo daga band'aki hannunta rik'e da buta, aje butar da sauri ganin d'akin Balaraba a bud'e tun dazu Walidi ya bud'e mata, lokacin da zata shigo,gidan sam ta manta bata kulle ba suka futa, kai tsaye d'akin ta nufa, Lantana ta mik'e da sauri tabi bayanta, shima Sallau d'in mikewa yayi ya rufa musu baya, Bunkice suke mata sosai a cikin d'akin sunyi mata filla-filla da kayan sawar ta sun jefo waje, Lantana tace" yawwa Uwa! d'aga katifar nan ko anan take b'oye k'udi ki kwasa maganin dukan d'anki da tayi, aikuwa kafin Lantana ta rufe baki, Sallau ya d'aga katifar da sauri, babu komai k'asan katifar, ya mayar da ita ya aje, dama Balaraba bata wani ajiyar k'udi duk in ta samu na b'ukata ne shiyasa basa taruwa, mafi a kasari ma tafi ajiya cikin jakarta,kuma tana jikinta a rataye, haka suka k'araci bunkucen su basu ga komai ba, suka futo suna ta zagin ta,kamar mahaukata Babu abunda yake damun Iya illa zazzab'i na maleria nan me chamis din ya had'a mata magani yace"dole za'ai mata allura ta kwana uku, Balaraba duk ta biya kud'in me chamis din yace"Iya kinci abunci in ce ko"? "Eh to ba sosai naci ba" Iya tafad'a da kyar! yace "babu damuwa dama illar guda d'aya ce ayi miki allura bakici abunci ba, tunda kinci ko yaya ne shikkenan, nan ya had'a allura yayi mata, suka kamo hanya suka tawo gida,gurin wani mai balango da gurasa suka tsaya Balaraba ta sai mata gurasa da balangu,suka wuce gida, suna shiga soran gidan suka dinga jin hayaniya tana tashi a gidan, Iya tace" wannan masifa ta gidan nan Allah kayi mana maganinta, "Humm Iya ki kyalesu suyi su gama insha Allahu na kusa barin gidan sai kowa ya huta tunda nice basa buk'ata, duk kuma wanda ya zalunce ni Allah zai saka min" Balaraba tafada lokacin da suke shiga gidan, kayanta tafara cin karo dasu a watse a tsakar gida wasu a gurin rijiya wasu a kusa da shara, Cikin mamaki ta tsaya tana binsu da kallo, dawowar Mabaruka kenan daga talla, tana tsaye ita da Shamsiyya tana wassafa mata abunda ya faru, tsalle ta buga tayo kan Balaraba tace"Allah nagode maka,kullum mu ake kira karuwai, yau gashi yau Allah ya nuna mana karuwa a gidanmu,,zatayi zina da d'an gida, Huuuuuuuuu!!! tir dake da halinki shegiya karuwa" tak'arashe maganar cikin ihu! dama hanya take nema wacce zata ci mutumcin Balaraba sabuda mak'ure ta da tayi a bango kwanaki, kayanta dake watse tabi tana tumurmusawa da k'afafunta, babu abunda Balaraba tace, takama hannun Iya ta shigar da ita d'akinta,sannan ta futo su Sadiya na biye da bayanta, suka shiga d'aki, zama tayi gefan katifa ta zabga tagumi hannu bibbuyu, tunani take yaya zatayi da rayuwar ta da ta k'annenta, sai yanzu tafara jin rad'adi a kafarta, kallon k'afar tayi taga ta kara tasawa alamun k'ona, ita ba wannan ne abund ya dame ta ba yadda za'ayi su futa daga wannan jarabar itada "yan uwanta, shawarar da ta yanke kawai shine ta nemi gidan haya su bar gidan, shine mafuta duk wanda zai yi zargin ta, ya dad'e bai yi ba,dama kuma a cikin zargin mutane take, kullum, tun tana jiyo motsin da hayaniyar su Lantana ta a tsakar gida, taji shiru da alama kowa ya shiga d'akinshi, buta ta dauka ta futo tsakar gidan domin ta daura alwala, suka ci karo da Sallau ya shigo gidan afujajan, gabanta ne ya fad'i sai tafara karanta innalillahi a zuciyar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108