Skip to content

Chapter 69

Chapter 69

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,288 words 0 views Progress saved
Download Book

babu abunda yake d'orewa a duniyar nan sai ikon Allah,duk sharrin ku gami da hassadar Ku a kan Balaraba,dukanin abunda Allah ya hukunta, a kanta na alkairi sai ya faru, babu makawa, sai dai Ku mutu da b'akin cik...... "Ke Sadiya rufe min baki munafuka" Uwa!ta fad'a a fusace!ta cigaba da cewa" Wato ke dan baki haihu ba,shine kike min bak'in ciki, a dukanin lamarina da "yayana, to bari kiji, yanzu na fara bin malamai akan " yayana, sai ki mutu,baki san bin malamai ma sai me kud'i ba, aikin banza kawai" Shamsiyya ta rik'e hannun Uwa!tana fad'in "Don Allah k'yaleta munafuka ce zo mu tafi tana b'ata mana lokaci" Futa sukayi suna zagin Sadiya, gami da kwashe mata albarka. Ita kuwa Sadiya bayan futarsu girgiza kai tayi kawai ta shige d'akinta tana nema musu shiriyar Allah. *Wannan kenan* ********* Sosai Sarki!ya sakarwa Halisa fuska sukaiyi hira ta fahimta, abunda yasa ya saki jiki da ita,shine ya fad'a mata maganar auransa da Balaraba yaga ta Saki jikinta, bata nuna kishi ba, yaji dadin hakan sosai,kuma suna tare Azima ta kirashi a Waya, nan ma bata nuna b'acin ranta ba, ta burgeshi sosai, har wajan magariba suna tare da juna. Balaraba na cikin d'aki shiru, zuciyarta duk babu dad'i gasu Sadiya masu d'ebe mata kewa suna can falo har yanzu basu shigo ba. Mik'ewa tayi a nutse ta futa daga d'akin. Can ta hango su, wani keb'antaccan guri suna wasa babu abunda ya dame su Kwata-kwata bata kalli inda suke zaune ba, ta nufi inda su Sadiya suke, tunda ta futo yake satar kallonta ta kasan idonsa, har Halisa ta fahimta,ranta ya b'aci amma ta danne, kawai bata nuna ba. Mik'ewa yayi shima ya d'an kalli a gogon hannunsa bakwai shaura, Yace"Lokacin sallah yayi ya kamata, kije kiyi sallah ko" Halisa ta mik'e tsaye tana gyara zaman rigarta, tace"Idan nayi sallah zan dawo mu cigaba da hira, yau naji dadin hiraramu,babu fad'a bare hantara" A kasalance yace"Baki da abunyi ne,shiyasa kike wannan maganar, hirar haka ta isa, gobe ma bance kizo ba, domin nasan halinki" Cikin shagwab'a tace"Me yasa"? "Ba ranar ki bace gobe,zan zauna da Azima kamar yanda na zauna dake yau" Tab'e baki tayi,amma bata yarda ya gani ba,tayi shiru da bakinta kawai bata sake magana ba. Tsakaninsa da Balaraba ido ne,ko da tazo ta wuce su bata ce masa komai ba shima haka haka suka shige d'aki ita dasu Sadiya, su kuma suka futa tare. https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» 。。。。。。。。。。。。。。。 _*GIMBIYA BALARABA*_ πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *BINTUBATULAπŸ‘„* _MARUBUCIAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* _*Zamani writers Association*_ ________________________ *We are her to educate motivate and entertain aur Reades* _________________________ *DIDEGATED* *to* RAHAMA ALIYU 🎯🎯🎯🎯🎯🎯🎯 _*Soyayyar gaskiya*_ 🎯🎯🎯🎯🎯🎯🎯 _Jin jina gare ki marubuciyar wannan littafin,( Mugirat Musa 66) Nagode da addu'ar ki a gare ni, Ina miki fatan alkairi a rayuwar ki,Ubangiji Allah ya biya miki buk'atanki na alkairi damu kanmu al'umar musulmi baki d'aya._ BISIMILLAHIR_RAHAMANIR RAHIM *πŸ…Ώ80* Sai bayan sallahr Magariba Mama ta shigo, sun sha hira da Hajiya Kattime sosai,taji dadin ziyarar da Mama ta kaima ta,domin ta d'ebe mata kewa sosai, ko da Waziri ya futo daga turakarsa ya ganta,shan kunu yayi ya fucewarsa ba tare da ya amsa mata gaisuwarta ba, inda akwai wacce ya tsana a duniya,bai wuce Mama Fulani, da d'anta ba,wato Sarki! Ko da ya futa babu inda ya nufa sai sashen Hajiya Kulu me d'akin kudu wato Uwar gidan me Martaba kenan. ***** Tana hakimce kan wata kujera me cin mutum d'aya k'afarta d'aya kan d'aya bayi ne zagaye da ita suna fadanci, ita kuma sai zuba mulki take, Waziri yayi sallama ya shiga d'akin. D'aya bayan d'ayan bayin da suka futa,bayan sun kwashi gaisuwa gurinsa. Guri ya nema ya zauna yana fuskantar Hajiya Kulu sosai, suka gaisa cikin barkwanci kamar yarda suka saba, yace magana ce, nake tafe da ita" Hajiya Kulu ta gyara zamanta tana kallonsa,tace"Ai tunda na ganka nasan akwai magana a bakin ka, kasan abokin kuka shi ake fad'awa mutuwa, nima dama ina neman ka" Girgiza kai yayi, yaja wata ajiyar zuciya me zafi, yace"Mijinki yana samun nasara akaina ta ko wane hali,to wannan karon nayi rantsuwar sai dai ayi mutuwar kasko, ko ni ko shi,wallahi tallahi, mulki sai ya dawo hannu na,domin inaji ina gani, bazai bawa d'anshi mulki ba,ni ina zaune ban hau kurarar naji yaya take ba, ajiyar zuciya ya sauke,ya cigaba da cewa"Ina me tabbatar miki da cewar wannan karon idan ya tsananta to zan kawar dashi, daga duniyar nan,sai dai yaga ana mulki a k'iyama,idan yaje can" Ya k'arashe maganar bakinsa na kumfa" Hajiya Kulu,tace"Wannan maganar da kake tafe da ita,nima a kanta nake,a kintse nake,a shirye nake,zan mara maka baya gurin ganin burinmu ya cika,akansa ko d'ansa,domin kwata-kwata bana sha'awar mulki ya koma hannun wancan d'an shegiyar,ina me tabbatar maka da cewa kashinmu ya bushe" "Bar wannan maganar Hajiya,domin in kina yin ta jikina har wani d'aukar zafi yake,yanzu ke wace shawarar kika yanke kan al'amarin domin inji shirinki,nasan kema dai ba daga baya ba gurin shirya mugunta" Hajiya Kulu ta gyara zams sosai,ta kwashe masa duk abunda ta tsara,har da zuwan d'an bori, me suna Tsito, Waziri ya girgiza kai, gami da cewa"In yazo nine zan bashi masauki ina fatan dai ya iya aiki" Hajiya Kulu tace"Idan kaji aiki ma d'aya kenan,Tsito k'arshe ne,duk wani aljani dakake ji da gani, yana aiki dashu,kuma in ka nemi kayi magana dasu zai kirasu kuyi magana, babu wata shirka da tsubbu da bai iya ba,mutuk'ar zaka'aje masa kayan aiki,zaka ga aiki da cikawa" Gyad'a kai Waziri yayi cikin jin d'adi yace"Hak'ika wannan shine irin Wanda nake so, na samu,na lura yanda kike k'warzanta shi,har kashe mutum zai iya yi ko"? Hajiya Kulu tayi dariya, har da dukan hannun kujerar da take kai, cikin annushuwa tace"K'aramin aiki kenan,ai nake fad'a maka,yanda nake jin labarinsa gurin Jakadiya tace,a rana in yasa kansa,zai iya bawa aljanunsa k'afa masu goma,su sha jini su k'oshi" Waziri yayi murmushi yana ji a jikinsa buk'atarsa ta kusa biya, yace"Yaushe kika ce zai zo ne"? "Gobe Jakadiya za taje ta d'aukoshi" "Allah ya kaimu" Waziri ya fad'a ya cigaba da cewa"Tabbas idan yayi mana aiki me kyau,zan yi masa muhimiyar kyauta,ta ban mamaki" Hajiya Kulu tace"Kai dai kaje ka kwantar da hankalin ka kawai,ai buk'atarmu kamar ta biya ne" Waziri ya mik'e tsaye, da niyyar tafiya, gaskiya yana cike da farin ciki, tabbas yasan Hajiya Kulu ba tun yau ba,makirar maca ce kuma muguwa ce,ta inna niha,duk hanyar mugunta,ta sani,sallama sukayi,ko wanne zuciyarsa fara tas, suna Allah-Allah gobe tayi D'an bori Tsito ya dura,a gidan, domin ya fara aiwatar da aikinsa. **** Bayan sallahr Isha'i Mama ta aika Jakadiya Shafa'atu domin ta kira mata, Balaraba a cewar ta zaman kad'acin da Balaraba take,zai iya haddasa mata wani ciwon, babu yadda ta iya, ta mik'e ta bi bayan Jakadiya,domin baza ta iya sab'awa umarnin Mama ba,lokacin su Sadiya sunyi bacci. Sosai Mama take hira da ita tana dan janta a jiki,duk domin ta sake,tasa Jakadajiya tana basu labarai na ban dariya,sai ga Balaraba,ta saki jiki sosai har tana dariya. duk abunda bata gane ba,a game da labarin da Jakadiya Shafa'atu take bayarwa sai ta tambaye ta,ita kuma ta fad'a mata, k'arshe dai

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108