Skip to content

Chapter 11

Chapter 11

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,231 words 0 views Progress saved
Download Book

duniya Allah ya dauki Ran Malam Tanko Sakamakon Rashin Lafiya tafarar daya, Ayuba ya shaqu da Mahaifinshi Sosai Shiyasa Yaji Dacin Mutuwarsa,inda Kiyyaya da tsana gami da tsangwama,ce Tsakaninsa da "Yan Uwansa don ko da a kazo rabon Gado Sallau da Lantana ,Cewa Sukayi Ayuba Bashi da gadon Ubansu Domin Ba Dan Halak! Bane ,Sai da Malam Liman ya tsaya tsayin Daka A kan Lamarin Sannan A ka fitarwa da Ayuba gadonsa a gidan Ubansa. Duk Rayuwarshi gidan Liman yake yin ta ,inda ya kasance *Yaro* mai zafin Nema,a wancan lokacin duk Abinda ya ta6a sai ya zama kudi. Sallau ya sakoshi a gaba Da bakin ciki da hassada ,duk inda yasan yana zuwa Nemansa sai ya je ya batashi. [04/05, 03:14] +234 808 996 5176: πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€ *✍🏻Writting by* _Binta Umar_ *MAMAN ABDUL WAHABU* _*ZAMANI WRITES ASSOCIATION*_🀝🏻 *πŸ…Ώ18* _Bissimillahi_ A lokacin Sallau yayi Aure inda ya Auri "Yar yayar Lantana Mai Suna Fatsima suna kiranta da (Uwa!) Yarinya ce Mara kunya inda bata ganin girman kowa ,babba da Yaro ,Har Mahaifiyarta fito Na fito take da ita,Bata da Aiki sai yawon tallace Tallace to har a kayi Auran Uwa Na fita kofar gida ta dasa kasko Na suyar Awara gefe ga gyada nan cikin Faratin A quq-qulle a leda marau da tubes! Haka take Tara matasa ai ta shirme ,idan har kan dillanci tazo nan ma tana tabawa A takaice ita ce take ciyar da Sallau domin shi ya zauna zuciyarsa A mace yaqi ya fita ya nema ,Gwara Maman shi ya kan fita yayi buge bugensa ya samu Na kashewa,ita ko Lantana Kasuwanni take bi tana tallan zogale da kuli ,Da wannan suke Samun Abinda zasu kai bakinsu. To shiyasa daga Lantana Har Sallau! Suka taso Ayuba a gaba da kyashi gami da hassada,Wanda hausawa sukance (Hassada ga mai rabo taki ce) Ayuba ya shaku da "Yar Uwarshi Atika ,domin duk wani Sirrin shi tasani ita da Gwaggo Shatu marikiyar shi , Haka ya cigaba da Rayuwa ,tare da Kiyyaya da tsangwama gurin "Yan Uwanshi,Amma duk da Haka shi bai fasa Zumunci da su ba, Hafsatu ita ce Ayuba ya Amince da tazama Uwar "Yayanshi, Domin ya yaba da tarbiyar ta gami da nutsuwa da kamun kai,"Yar Makotan Su Atika ce Yayarshi Ita ma haifinta ya rasu,to haka dai Malam Liman ya tsaya Masa tsayin daka ganin Tabbatuwar Auran Nan ta tare gidansu ,Bangaran shi Na gado,Uwa da Lantana suka ce dawa Allah ya hadasu,suka sanya ta a gaba Babu irin Muguntar da basai Mata,yarinyar duk ta kwar zane,kullum cikin Aikin Awarar Uwa take tamkar ita take Auranta,inda Allah ya tai maketa ma ,Lantana,bata yini a gida Sai Yamma take dawowa daga zarar ta dawo ,zatai ta kwala Mata kira tana zagi! Tai ta sanya ta Aikin Wahala ,ko da ta Samu ciki basu bar ta ta huta ba, Kullum idan Ayuba ya shi go gidan yaga irin wahalar da take sha,sai bakin ciki ya kamashi gashi bashi da Bakin Magana,Lantana ta tsigale shi, Kullum in sun shiga daki yai ta Rarrashin ta yace"tayi hakuri Shima ba yason Wannan Wahalar da take sha Da yana da Hali da sai ya kama mata Haya ko daki guda ne,to Babu Hali domin duk wasu hanyoyin Samunsa Sallau ya shiga ya fita ,ya rabashi dasu da Asiri da kuma Ziga ga Mutane ,cewar kar Wanda ta hada hurda dashi domin ko ba Dan gari ba ne,Zai cuce su ya gudu To Lokacin A kwai qarancin Ilimi gami da Wayewa Sai Jama'a suka dinga gudun Ayuba, Tunda ga Lokacin ya dai na sana'a sai dai ya fita tayi buge bugensa ya dawo gida A lokacin Uwa! Tana da Yara Biyu Namiji da Mace'Iro da Shamsiyya, To iro tun yana shekara Uku ya iya yawon Talla kusfa kusfa,haka zata kasa masa a faran ti tun Safe ,ba bu Maganar zuwa makaranta Haka ake Zaman doya da Manja a gidan Domin Maman ma ya yi Aure shima Matarshi Na gidan , Mai suna Halima inda ta kasance mace mai sauqi hali gami da Hankali ,kwata kwata bata kaunar Abinda Su Lantana sukewa Hafsatu Matar Ayuba ,sai ta riqa Jan ta a jiki tana tausar ta,nan ko Uwa!! Tace dawa Allah ya hada su ,shiga fita Dari sai ta Zubda musu Ha baici ta dauki gaba da Halima ,duk dai a kan tana kula Hafsatu,ita ko Lantana dama Macace mai mugun kwadayi kasan cewar Maman duk ya fisu Samu yasa bata son Laifin sa ko Na Matarshi shiyasa ta kyale ta take Kula Hafsatun Dan kar ta dai Na bata Abinci da kayan dadi in Maman ya siyo Domin ,shi kwata kwata ya Manta da wata Lantana ta Matarshi yake,in Anyi Magana yace ai tana fita Nema taci da Kan ta,shima yanzu Nauyi yayi masa yawa. *Allah ka azirtamu da "Yaya masu Albarka ,duk Dan da zai zame mana fitina a rayuwarmu Allah kar ka bamu,Allah ka sa mufi qarfin zuciyoyinmu* *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* 08089965176 [04/05, 03:14] +234 808 996 5176: πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA🐾* πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€ *✍🏻Writing by* _Binta Umar_ *MAMAN ABDUL WAHABU* _*ZAMANI WRITES ASSOCIATION*_🀝🏻 *πŸ…Ώ19* _Bissimillahi_ Cikin Hafsatu ya isa Haihuwa , Halima Matar ,Maman ce ta tsaya Mata a gidan Lokacin Gwaggo Shatu babu Lafiya Abinka da jikin girma, Iya" Atika ita ce ta karbi Haihuwar ,su Lokacin Domin Lantana ta tafi tallanta Hakanan Uwa! Na waje tana Soyar Awara Tamkar ba matan Aure ba Cikin ikon Allah ta haifi diyar ta Mace Sak! Mahaifinta Kamar an tsaga kara dashi Fara tas!! Ga hanci har baka, Ayuba ya ruqa Murna ,A take yayi wa jaririya huduba da Sunan Mahaifiyarshi, wato Suwaibah ,sai ya ke ce Mata Balaraba kasancewar An haifeta ranar Laraba Ko da Lantana ta dawo taga jaririya tace ,Haushi Kamar ya kashe ta ganin Baiwa da kyau da Allah yayi mata ga Hafsatu Lafiya lau,ita San samun ta Hafsatun ta mutu kamar yadda Suwaibah ma ta Mutu , A ranar kwana tayi tana zage-zage Kamar ba tsohuwa ba, Ita ko Uwa!! Tsabar kyashi bai bar ta ba ma ballan ta ta shi go ta ga Abinda Hafsatu ta Haifa ,ta dai tura Iro gulma! Domin yaje ya gano mata ,Aiko Yaron ya dawo Yana Fada mata kyawun "Yar jinjinyar ,Bakin ciki kamar ya kasheta,ta waiwaya ta kalli Yarinyar ta Shamsiyya,a zaune ,duqun duqun!! Daga ita sai karamin ,Wando ga Wani Uban zarni! Da take yi,Yarinyar Baqa ce Sosai gashi Mummuna Dan Har Iro yafi ta kyau tunda shi ya Dan dauko kammanin Mahaifinshi,ito ko Shamsiyya Kamarsu daya da Uwarta! Nan taci Alwashin Sake Haihuwa ,Domin tana Zaune Wata baza tazo tafi ta "Yaya a gidan Ba, kuma in sha Allah ita ma sai ta haifi Fari ,sabida Sallau yana da Haske dai-dai gwargwado *Ni ko nace kuji ni da Uwa! Da tsabar jahilci don Allah*🀣 Har a kayi Suna Uwa! Da Lantana basu leqa sun ga Abinda a ka Haifa ba,Balle Sallau" Wanda ya tsiri gaba! Da Ayuba babu gaira babu dalili ganin yadda yayi komai Na Haihuwa ,Hatta hakika, biyu ya yankawa Maijego,shine yake Bakin ciki ,yana tunanin a ina ya samu kudin da yayi wannan Hidimar **** Kafin Hafsatu tayi Ar'ba'in Uwa! Ta samu Ciki sai tun qaho take

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108