Skip to content

Chapter 12

Chapter 12

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,230 words 0 views Progress saved
Download Book

tana hora hanci ita zata haihu ,Shiga Dari fita Dari sai ta yadda Habaici tamkar Wacce bata taba Haihuwa ba ,Ita ko Hafsatu bata ce Mata komai ,in tagama Ai kace Aikacen ta ,sai ta tafi bangaran ,Suyi zamansu Har Magari ba *Balaraba* ta saba da Halima Sosai in Kusan Kullum tana Hannunta ,in ko bata gurinta tana can gidan ,Iya Atika, Haka jama'a suke Kaunar ta daga An fita da ita kowa son ta dauke ta yake,Sabida farin jinin ta, Uwa! Ko babu shiri ta bazama, Gurin Malamai a kan Yarinyar ,Wai a Sanya Mata Bakin jini a ida nun Jama'a kuma a saka Ta ta fandare ta zama ga gararriya, Malamin nata yaga Tsubbu bace Tsubbacan Sa ya yi Mata Baya nin Yadda zata yi da kayan Aikin da ya bata Mutukar ta kuskure to babu Makawa "Yayanta zasu Lalace domin Aikin kansu Zai kuma, Haka ta dawo gida tana Haki ga tsohon Ciki a jikinta, Sai da ta bari dare yayi Sosai kowa ya shige dakinshi ,sannan ta Fito ta daga Manyan dutsinan da suke girgi dashi ta tona Gurin da Wuqa yayi zurfi Sosai ,sannan ta saka Wasu Manya Manyan Layu! Guda biyu ,tayi Sauri ta Mayar da kasar gurin ta Binne ,sannan ta Dora dotsen a kai. Ashe tayi shuka a idon Makwarwa Domin dai tun lokacin da tafito ,Halima ta ganta ita ma ta ta shine domin Zuwa ban daki har ta fito sai ta Ja da baya ,ta labe jikin kofar ta ganin Uwa!! A Gurfa ne a gaban Murhu ta dage tana To na wa. *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* 08089965176 [04/05, 03:14] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€ *✍🏻Writting by* _Binta Umar_ *Maman Abdul Wahabu* _*ZAMANI WRITES ASSOCIATION*_ *πŸ…Ώ20* _Bissimillahi_ Uwa! Na gama binne Layun ta Mike ,tana karkade jikinta sai wai ge wai ge take Na rashin Gaskiya, tayi Sauri ta shige dakin ta Ita ko Halima sai ta bari ta dai najin Motsin Uwa! Daga dakin ta,Sannan ta fito a hankali,ta aje botar hannunta gefe ,ta Dauke katon dutsen ,sannan ta sa Wuqa tafara tone Abinda Uwa ta Binne! A gurin Can ta tonu Layu daure jikin Wani Jan yanki, tayi Bissilimih gami da sanya Hannunta ta dauke ta aje gefe ,ta fara mai da kasar gurun tana Rufewa,Tsaf ta Gyara gurin ,ta mike tana Addu'oi ta dauki Layun ,ta je ta aje a gurin ta,Sannan ta dawo tayi Uzirin ta dama Abinda ya tashe ta kenan, Jin Motsin bude kofar ban daki ne yasa Uwa futowa da Sauri ,Tana kallon Bakin Murhu,Ajiyar Zuciya ta Sauke ganin Babu Abinda ya faru yadda ta bar gurin haka yake, Kallon- kallo sukayi ita da Halima,Sai ta buga tsaki ,ta joya ta shige dakin ta ban ko kofa! Girgiza kai! Halima tayi kawai,tana Mamakin Zuciyar Uwa Tamkar ta kafurai, A fili tace Allah ya shirye ki Uwa!" Ta shige dakin ta ita ma Safiya nayi Uwa! Ta fito ta aza tukunyar Awara ,A wuta ta dinga Hura huta Sosai sabida Malam yace Mata ,In ta binne layun ta saka Wuta sosai a gurin yadda Aikin zai fi saurin kamawa, Ai kuwa haka tayi sai Faman Saka ice take, duk a kokarin ta Na taga *Balaraba* ta lalace, *Allah ka sa muda ce* Can Bangaran Halima kuwa ,babu Wanda ta fadawa Abinda ya faru ,kawai Safiya nayi ta boye Layun Cikin Hijab din ta ,ta fita daga gidan,kai tsaye gidansu ta nufa,dama kusa ne,ta sanya kannenta ,suka kwance Layun ,tare da yi musu futsari Sannan tace ,su jefa a Masai! Ai kuwa haka yaran sukayi Abinda ta Umar cesu, Nan ta rarraba musu Goma-Goma suka tafi suna Murna, Maihaifiyar ta take Tambayar ta Mai nene"? Nan ta warware mata komai Tace "Gaskiya Uwa! Bata da imani Wallahi narasa Abunda Hafsatu ta tsare mata,Bai wuce ita tayiwa Asiri ba" Halima tace"Tabbas ita za tayi wa ,in sha Allahu sai dai sharrin ta ya bi ta,tunda ita ba ta nufe ta da shi ba, ***** Wannan Shine sanadiyar Lalacewar Iro ,Uwa!Na zuba Ido taji an ce Balaraba tafara sace-sace sai Hakan tafaru kan Dan ta Iro, Kwatsam! Suna Zaune daf da Magariba dukkaninsu a tsakar gida har Lantana ,ta dawo daga yawon Tallanta, Tafito da ciniki tana lissafawa Sallau! Ma shigowar sa kenan ,yana gyara tsayuwar Kekensa, Ita Kuma Tana Aikin Awara Wacce Shamsiyya take Zama gidin bishiya tana Soyawa da daddare, Kawai! Suka ji ihu! Ana barawo barawo Kafin suyi Wani yunkuri! Iro yafado gidan Yana Haki! Gashi sai Warin ganye! Yake yi,idonshi yayi ja,da gudu ya shiga dakin Lantana ya kulle , Matasa ne suka shi go sun kai su goma ko wannesu riqe da Abin duka! Suka Zagin Iro ! Wai sai ya fito sun dake shi, Lantana ta Mike a zabure! Tana gyara daurin Zaninta bayan ta Kwashe kananun kudinta da ta baza a kasa tana qirgawa ta boye cikin ,Wani burgujejen Sket din ta Mai Aljihuna,Wanda take sanyashi a ciki kafin ta daura Zani, takarasa In da suke tsaye Suna Hayaniya! Sallau Sai Rarrashin su yake Sabida ,dama shi tuntuni yaji Labarin Abinda Dan shi yake Aikatawa. Tace"Ku tsinannu! "Yayan Mutsiya ta, Mai jika Na yayi muku ,kuka biyo shi da Abin duka sai kace ,Wanda kuka kama shi da kayan Wani! Daya daga cikinsu, Yace "ke! Tsohuwa Kar ki rainawa mutane Hankali mana! Eh! A kwai tsinanne irin Iro! barawo Mai kwatar Wayoyin Mutane, Kinga Wannan Yaron ya fizgewa Waya,yanzu An ai keshi ya kai chaji ,Sabida haka kushiga Ku fito dashi ,Billahillazi Ku mu balla kofar! Mu Saba masa Kammani,dama ya ishe mu da Sace-Sace' A Unguwa babu dama a Aiki Yara da kudi ,sai ya kwace. *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* 08089965176 [04/05, 03:15] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€πŸ§πŸ»β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 *✍🏻Writting By* _Binta Umar_ *MAMAN ABDUL WAHABU* _*ZAMANI WRITES ASSOCIATION*_ *πŸ…Ώ21* "Sai dai idan kune barayi To kaji"! Lantana tafadi Maganar Kamar zata kaiwa Yaron Duka! Taci gaba da Cewa "Nasan Halin jikana baya Sata ,haka Kawai zaku kala Masa Sharri, Mutsiya ta" Wani Yaro Da suke kira Umaruru Dan zafin Kai Ne ,Sosai Bai Saurari Kowa ba Yayi Hanyar Dakin da yake Hango iro tun dazu yana Leqo da kai ta taga, Ya daki Kofar dakin da kafarshi daya,ta bude wai sunan an San ya Mata Sakata , Ya kamo Iro suka fito ,Yana turjewa, Nan Mata San suka yo kansa ko wanne da Abin duka ,suka fara jibgarshi suna Tambayar inda ya kai Wayar da ya kwace Nan Uwa! Tafa sa ihu! Tayi kan su Tana tutturesu Wai kar su kashe Mata da! Su fadi ko nawa ne kudin Wayar Zata biya su Lantana ta rika dura Musu Ashar tana bangaje su Lallai sai ta shiga tsakiya ta Hanasu dukan iro Umaruru ya Sanya Hannu daya ta ture ta tafadi a gurin ,Amma duk da Haka bata dai Na Zaginsu ba gami da Yi Musu mugun Baki Shi ko Sallau Shiru yayi yana kallonsu yana tsaye jikin bango yasan ko yace Suyi Hakuri ba za su hakura ba ,Sabida yasan Dama sun Dade sunaso su kama iron, Shi tsoro yake Ma kar su hada dashi, Halima da Hafsatu

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108