Chapter 85
Chapter 85
Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *Wannan page din naki ne rahama lawal Umar ( ummu Farhan ) kiyi yanda kike so dashi ,alkhairin Allah ya isa gare ki a duk inda kike nagode da soyayyar gare ni Allah ya bar zumunci Ameen* *Sorry last page nayi mistake wajan saka number maimakon 54&55 , na saka 44 &45. *56&57* Baba gaba d'aya jikin shi a mace yake da jin bayanan Abdulbasit tabbas ya tafka kuskure ko Kuma yace yana cikin b'ata, son duniya da sharrin shaid'an ya kai shi ga aikata duk abinda yayi sai dai komai rubutattace ne a kundin kaddara wanda ba makawa sai ya samu mai shi, in da ya kasance mai kulawa da iyalin sa da duk haka bata faru ba. "Na san ba zan kai labari ba dan kashe ni zasuyi kuma nima hakan nake fata domin tunda na rabu da Zareefa ban tab'a jin dad'in rayuwata daidai na second d'aya ba, nayi jinya a boye ba tare da kowa ya sani ba da naje asbiti doctor yace na kamu da ciwon zuciya mai tsanani , shiyasa na kudiri aniyar ganin bayan Emaka kamin in karasa 'yan kwanaki da suka rage min" Abdulbasit ya karasa da fashewa da kuka da bai samu daman yi ba duk watanin nan. Hawaye da suka zubo mishi Baba ya share zaiyi magana Baban Hamis ya kashe system d'in shi ya juyo yana facing abokanen aikin shi da duk suma labarin ya girgiza su kaman yanda ya girgiza shi shima sai dai kowannen su ya shanye abin sa a rai ba zaka tab'a fahimtar komai akan fuskokin su ba. Gyaran murya yayi sannan ya fara magana" duk da komai ya bayyana Ina son shi wannan Abdulbasit d'in ya amsa laifin shi da bakin shi sannan yayi jagora inda za'a samu gang d'in nasu gaba d'aya" babu wani ja suka nuna gamsuwar su kan hukucin da ya yanke bayan dan tattaunawa da sukayi suka wuce offices d'in su. Zafar bai masu isowa gidan mu ba sai da ya tsaya yayi sallahn azahar ya tsaya a wani shopping mall yayi sayayyan kayan masurufi masu yawan gaske sannan ya karaso gida. A waje yanzun ma yayi parking din motan shi ya samu yara a kofar gidan suna jiran a gama abincin sadaka a raba musu yace su shigar da kayan cikin gida nan da nan ko suka fara shigowa da sayayyan da yayi zuwa tsakar gida suna ajiyewa, Inna da fitowar ta kenan daga wanka tana neman Ibrahim ya fara kiran masu karban sakadan tayi arba dasu suna ta shigowa da kaya suna jibgewa hayaniyar su duk ya cika gidan. Cike da mamaki tabi su da kallo kamin ta tambaya Ibrahim da shigowar shi kenan rungume da carton na indomie yace " Innan Zareefa mijin Zareefa ne yace mu shigo da kayan nan kuma yace wai ta fito su tafi". Cizon yatsa Gwaggo Aisha da take leke ta window tayi tana jin bakinciki da takaici ya kume ta dole ne tayi maganin Inna ta shiyasa take ta d'agawa mutane hanci a gidan ita wai 'yar ta na auran mai kudi, Hajara da shigowan ta kenan zata wuce ciki ta ga yanda take rike da labule tana kallon yaran fuskarta kuwa kaman anyi gobara sai cizon d'an yatsa take, kain ta girgiza kawai tayi wucewar ta ciki tana mata addu'an shiriya ta barta anan tsaye tana faman leke . Na fito daga bathroom d'in daki na kenan fuskata na d'igan ruwan alwala da nayi murmushi nake sosai ina jin kaman babu inda na tafi iya watanin nan kaman bacci nayi na tashi haka nake ji domin komai na dakina yana nan tsab ba abinda ya canza kaman lokacin da nake nan. Kara fad'ad'a murmushi na nayi ganin Inna zaune a bakin gadon tana jiran fitowa na kamin in samu daman yi mata magana tace " kina idar da sallah ki fito ku tafi yazo yana jiran ki a waje" a take farar dake fuskata ya kau na kwab'e shi kuwa kaman zanyi kuka saboda ko kad'an ban saka ran tafiya yanzu ba na zata sai dare zai dawo. "Bana son shashanci kiyi sallah ki fito nace sannan kada ki yarda in kara dawowa dakin nan baki fito ba kema kin san sauran" cewar Inna kenan tana barin d'akin, hawayen da suka zubo min na share tare da karasowa ciki na shimfid'a abin sallah na fara sanin halin Inna in ta shigo ba zatayi min da dad'i ba. Har na idar da sallah ban daina hawaye ba dan ko kad'an bana son tafiyan, dole na na fito parlorn Ina sharar kwalla na samu Inna zaune da wani babban leda kusa da ita tace in shiga d'akin ta muyi sallama dasu Maa, jiki ba kwari na shiga na same ta harda 'yan uwan Baba duk sun idar da sallah kowacce rike da carbi suna lazimi. Har kasa na zauna dan niyyan yi musu sallaman amma na kasa furta komai sai hawaye na da suka karu, dariya suka fara min wai Inna ta shagwab'ani dayawa daga baya kuma suka shiga yi min nasiha kan in kara hakuri domin zaman gidan miji saida hakuri, ba gidan miji ba duniyar kanta in kana son kaji dad'in ta toh sai da hakuri da kauda kai. Tun ina kuka har na daina saboda yanda suka kashe min jiki daga nan suka ce in tashi in tafi yana Jira na, tashi nayi na fito Inna tana nan a inda na barta, miko min ledan tayi tace to in tafi mu gaida gida maimakon in karb'a kuka na saka mata ina sai naci abinci domin nayi missing girkin ta. Kala bata ce min ba sai ganin ta nayi da wani madaidaicin warmer ta zubo min abincin sadaka da sukayi tace in naje gidana inci kuma in biya wajan sauran matan gidan inyi musu sallama, dole na karb'a na fito Inna Asabe ita na fara yiwa sallama sai maman Dije ban shiga wajan Gwaggo Aisha ba kasancewar Hajara tace min ta tafi anguwa, a kofar d'akin su na tsaya dan muyi sallama amma sai ta karb'i kayan hannu na ta fara taka min tare muka fito bakin gate. Ta window Gwaggo Aisha take leken mu har muka fita bakinciki kuwa kaman ta had'ye zuciya ta mutu take ji wato na shiga ko Ina nayi musu sallama ita da na raina shine ban shiga mata ba ? Koda yake ta san Inna ce ta kitsa min hakan , ita kuma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99