Skip to content

Chapter 27

Chapter 27

Ba Sonta Nake Ba Book One Complete Hausa Novel 1,295 words 0 views Progress saved
Download Book

yarda su had'u duk yanda Yaya na ya kai ga son su gana amma yaki yarda kowani lokaci akwai excuse da zai nemo ya bada dan kaurace had'uwan nasu. Dije anyi auren ta kusan wata biyar da suka wuce ta auri mijin ta mai suna Bala ba mai arziki bane amma akwai wadatar zuci da rufin asiri, ko bikin ma kowa sai son barka yake kasancewar anyi komai cikin tsari. Hajara tana gida an kawo ta wanka satin da ya wuce bayan ta haifi d'a ba rai sakamakon yawan dukan da take sha wajan mijin nata ga yunwa da yake barin ta dashi sai dai Gwaggo Aisha tayi musu aike na kayan abincin domin yanzu tana samu ko sana'a ta daina yi duka bukatun ta Jameela ta d'auke mata su sakamakon samari masu kud'i da ta samu amma fa a cewar Gwaggo Aisha kenan dan ni dai ban tab'a ganin wani yazo kofar gidan mu neman ta da sunan zance ba sai dai inga taci kwalliya cikin matsattsun kaya ta fita kan zata je gidan kawaye in anyi sa'a ta dawo cikin dare ta kwana a gida wata rana kuma sai tayi kwana biyu bata dawo gidan ba, ta goge ta kara haske da kyau duk da hasken na shago ne. Dawainiya kula da Yayar ta ma itace ta d'auka babu abinda ta rage ta dashi shi kuwa mijin tunda aka kawo ta gida bai kara bi ta kansu ba balle yazo ya duba ta ko yayi musu aike, wannan dalilin yasa Gwaggo Aisha d'aukan alwashin 'yar ta ta gama auren shi ko uban wa yayi mishi tsaye ta gama auren shi kenan. Hura hanci da d'aukan kai da Gwaggo Aisha take a cikin gida sai wanda ya gani Inna Asabe take kula ta wani lokacin suyi tayi dan Inna ta kam ko iskar daya d'ebo ta bai ishe kallo ba. Sosai take kokari na son ta burge Baban mu dan ta dawo da matsayin ta na da amma hakan ta bai cimma ruwa ba kasancewar Baban mu gaba d'aya hankalin shi ya dawo kan Inna ta domin ita komai zata yi mishi ko ta bashi bata yi mishi gori tsabanin Gwaggo Aisha da sai ta tsaya a tsakar gida take mishi terere kowa yana ji yana gani hakan yasa Baban fifita Inna fiye da kowa a gidan ita kuma Gwaggo Aisha wannan dalilin yasa tace asiri Inna tayi mishi kuma ko zata tafi tsirara sai ta karya shi. *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ *14* _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Addu'ar Mash'arul Haram* Jabir, Allah ya yarda da shi, ya ce: Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hau taguwarsa mai suna Al-Kaswa har ya zo Mash'arul haram, sai ya fuskanci alkibla ya yi addu'a ga Allah, ya yi kabbara, ya yi hailala, ya kadaita Allah. Bai gushe ba a tsaye yana addu'a har sai da gari ya waye sosai, sannan ya dauki hanya kafin rana ta fito. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *14* Gwaggo Aisha tana riƙe da ƙudirinta a zuciyarta na sai ta warware asirin da Inna tayi wa Baba ta maida hankalin shi kanta tayi mulkin ta a gidan son ranta saidai rashin kud'i shi yake kawo mata cikas dan Jameela ta kwana 2 bata dawo gida ba amma ta kudirta tana dawowa zata karb'a a hannunta taje ta gabatar. Bayan kwana 2 Jameela ta dawo daga yawonta ba b'ata lokaci ta same ta da zancen ta bata dubu ashirin zata je gwaza wajan wani gawurtaccen boka da kawarta lantana ta bata labari dan yayi mata maganin Inna. Ba musu balle bata lokaci Jameela ta cake mata dubu ashirin da biyar tace tasha ruwa da dubu biyar d'in,in so samu ne zata so ta had'a da ni a shafa min bakin jini ko d'an yankan kai daya makale min zai guje ni su ga ta tsiya . (hmmm wai Yayana take nufi.) "Jameela wallahi kaman kin shiga zuciyata daman ita da kinibabbiyar uwarta duk shine takamarsu, kin ga in ya rabu da ita shikenan kowa ya huta tabbas hakan zamuyi zan fad'awa bokan ya shafa mata bakin jini da ko wani namiji sai ya guje ta muga ta tsiya". Dariya Jameela ta kwashe da shi har suna tafawa da uwarta kaman wasu kawayen juna sannan tace"shiyasa nake son ki ummata". Gwaggo Aisha ta bud'i baki zatayi magana suka ji muryan Hajara tana cewa "haba Umma wannan wani irin rayuwa ce,wayan nan bayin Allah babu ruwan su damu suna zaune da kowa agidan nan da zuciya d'aya amma ku burin ku shine ku cutar dasu ya kamata mu d'auki darasi ko akan abinda ya faru dani ga Jameela ta saka yawon karuwanci a gaba kina gan............" Buge mata baki da akayi shi ya hana ta karasa maganan da tayi niyyan fad'a musu,hannu tasa ta dafe bakin ta daya fara mata zugi tana bin binsu da kallo idon ta cike da hawaye su kuma suna aikin aika mata muguwar harara "Hajara ni kike gayawa magana akan wata banza can, ni mahaifiyar ki?" Gwaggo Aisha ke yiwa Hajara tsawa tana nuna kan ta da yatsa. Gyad'a kai tayi kana tace "Ko da yake ba laifin ki bane ina ganin harda ke suka had'a suka tsafe dole sai na tashi tsaye ko kuma Bintu ta kaini ta baro,in banda aikin asiri tayaya zaki kira 'yar uwar ki wacce ta d'auki nauyin kulawa dake da wannan suna,. Kai jama'a kaji tsoron mutum Allah ya isa Bintu ki jira kiga yanda Allah zai wulakanta ki". Ta karasa cikin wani irin d'acin rai da tsantsan tsana. Jameela da har ta fara jin haushin 'yar uwar ta amma jin abinda mahaifiyar su ta fad'a yasa taji ta huce ashe ba yin ta bane itama asirce ta sukayi, haba abin da mamaki

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99