Chapter 82
Chapter 82
da alamu jikn shi ya fara sanyi. Kara sauke kan shi yayi ya cigaba " duk wani mugun aiki Emeka nayi kuma tun muna kanana ya bamu horo kan irin aiyuka da yake yi kasancewar muna dayawa Kuma dukan 'yan arewa ne babu kabilan shi ko d'aya a ciki, yana tura mu munayi mishi safaran kwayoyi cikin kasar nan sannan ga kidnapping na yara ana mishi safaran su kasashen waje Kuma muyi kidnapping na manyan mutane ko masu kudi muyi demanding kud'i masu uban yawa a wajan su daga baya in ya samu kud'in sai ya sake su su tafi amma wayan da suka mishi taurin kai kuma sawa yake a kashe su, a yanzu kam da Boko Haram suka yawaita yin b'arnan su shima sai ya saje dasu dan sai ya tura mutanen shi kauye guda a kashe iyayen ya kwashi yaran da yan matan ya tura su kasar da yake turawa a aiko mishi da kudin sa. Wasu hawaye masu zafi da suka zubo mishi yasa hannu ya d'auke tare da sauke ajiyar zuciya yace" duk cikin mu yaran shi Emeka yafi ji dani saboda kwazo na akan aiki dan babu aiki da zai bani a samu kuskure ko tangard'a a ciki sai dai kash had'uwa ta da ZAREEFA ya fara canza ni banida burin da ya wuce kyautata mata da saka ta farinciki tun tana karama , a lokacin da ta fara girma sai wannan tausayin da nake mata ya rikid'a ya koma so , I so much love her har Ina ji a jikina in ban aure ta ba rayuwa ta ba zai tab'a daidaita ba. A lokacin da na maida hankali na kan soyayya a lokacin kuma ya zama nayi sanyi a wajan aiki,duk aiki da Emeka zai bani sai an samu kuskure tun abin baya damun shi har ya fara damun sa kasancewar ya lura hankalin nawa ne sam baya tare dasu , a sirrance yasa aka fara bincike a kaina kan me yake d'auke min hankali har nake wasa da aikina haka, cikin kwana 2 aka kawo mishi rahoton soyayya nake da wata ta karbe min hankali har an saka mana rana auren ta zanyi. Sosai hankalin Emeka ya tashi dan ko shi baiyi aure ba saboda aikin namu hana bukatan sirri shiyasa ya jingine batun aure a gefe sai dai in ya bushi iska ya kan shigo cikin gari ya kama hotel ya hole da yan matan da yake so, dan haka yasa a ran shi dole ne ya dakatar dani tun kamin in rusa mishi tsari. Anan ya neme ni cikin lumana yake ce min in rabu da yarinya nan babu aure balle soyayya a cikin tsarin kungiyar mu ko na ga wani a cikin mu da mata? Sosai kalaman shi suka tada min hankali tayaya zan rabu da Zareefa yarinyan dana rayu da soyayyar ta tsawon shekaru kusan 7 yace min in rabu da ita? Ban tab'a yi mishi musu ba balle gardama amma a ranan shafawa ido na toka nayi nace babu abinda zai saka in rabu da ita koda kuwa zan fita a kungiyar ne, sosai hankalin Emeka ya tashi yayi ta rarrashi na amma na nuna sam abinda yake so ba zai tab'a yiwa ba, gsnin da gaske nake Kuma rarrashi ba zai saka in canza ra'ayina ba yasa ya fito min a ainihin suffar shi da yake boyewa a gaban mu wato d'an kungiyar sirri ne shi yana yaye wata kofa sai ga kayan tsafin sa kalala sun bayyana a gaban mu , Yana fara wasu kalmomin tsafi sai ga wata yarinya ta bayyana tana tafiya a cikin kasuwa, wata wuka ya ciro ya daba a kirjin yarinyan nan sai ga jini ya fara zubowa cikin kwaryan tsafin amma a zahiri mutane sai gani sukayi ta dafe kirji ta yanki jiki ta fad'i mutane suka taru akanta ana neman ba'asi. Juyowa yayi ya kalle ni yana murmushi yace ya umarce ni da in rabu da ita a yau din nan ba sai gobe ba ko kuma ya halaka ta, tunda na san kaina a cikin duniyan nan ban taba shiga rud'ani da tashin hankali irin wannan ranan ba jikina har karkarwa yake na shiga bashi hakuri akan kar ya kashe ta nayi mishi alkawari a yau zan rabu da ita. Shine naje a wannan ranan nayi mata munanan kalamai duk dan taji na fita ranta , koda muka rabu ta shiga gida kasa tafiya nayi har Innar ta ta fito ta same ni a Lokacin kuka nake kaman karamin yaro sosai ta shiga tashin hankali take tambaya ta me yake faruwa nan nace mata rayuwata da nata duk na cikin hadari muddin in ya kasance muna tare saboda wasu dalilai daban dana lissafo mata yanda zata fahimta kuma Allah cikin ikon shi ta gamsun sannan na bar kofar gidan. A zahiri na rabu da ita amma kuma a bad'ini ina tareda ita ko wani motsin ku akan ido na yake, na kasance kaman mutum mutumi komai na duniya ya fita akaina rayuwa ba Zareefa is like living in a hell, shiyasa lokacin bikin ta na kawo maka gudumawa ta akan ayi mata kayan d'aki na kece raini sanin gidan masu kudi za'a Kai ta amma dan mugunta irin naka ka cinye kudin kaki yi mata sai daga baya naji labarin shine na bawa mahaifiyar ta akayi mata duk abinda ya dace, wannan abinda kayi ya Kara harzuka ni dama ina neman hanyan dazan d'auki fansa akan ka shiyasa na fara ambaton sunanka da aka kama ni. Shi kuma mai gidan mu na dad'e da d'aukan alwashin sai na d'auki fansa akan shi in tarwatsa rayuwar shi kaman yanda ya tarwatsa nawa shiyasa daya bani kud'i in sayi securities d'in Minister nayi zagaye na dawo ban saye su ba kaman yanda ya bukata, ni naso suka kamani dan ko harbin da kake gani a kafana ni na harbi kaina kawai dan a kama ni kuma nayi abinda ya tabbatarwa sauran yaran da muka zo tare na mutu na san iyanzu Emeka ya d'auka na mutu ". [12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99