Chapter 24
Chapter 24
mahaifiyar ki tun muna kanana har zuwa girman mu" "Koma menene Dije su d'in 'yan uwa na ne, jini d'aya yake yawo a jikin mu daurewa kawai nake ina share su amma ina kaunar su har cikin raina ina kuma sha'awa in ga mun had'a kan mu kaman sauran 'yan uwa" Hawayen da ya zubo min na share na mike na kama hanyan bangaren mu itama Dije ko motsi kasawa tayi dan maganganu na sun kashe mata jiki,ko da na shiga d'akin mu na samu Inna zaune gefen gado ta rafka tagumi da alamu itama taji zancen kenan. "Tun d'azu ake kiran wayan ki" ta ce min ba tare da ta sauke tagumin ba saboda wannan al'amari ya bata mamaki da tsoro samarin yanzu mayaudara ne kuma macuta ne, in banda cuta kazo da wata siffa da suna dan a baka mata me yasa ba zai zo a yanda yake ba? Ko da yake Maman Dije ta ce wai sun riga sun nunawa duniya cewa in ba mai kud'i ba akai kasuwa shine yasa shi zuwa da wannan siffa. Ajiyar zuciya ta sauke wanda sai da na juya na kalle ta dama rply na tex nake rubutawa 'yar ajin mu a islamiya ta kira bana kusa shine ta min tex tana min tuni kan abubuwa da muka shirya na walimar mu. "Inna lafiya kuwa na gan ki haka?" Na tambaya. "Hmmmm ba komai je ki wanke min hijabi na da da yake cikin bukiti a waje" da toh na amsa na fita wankin. Ina fara wankin naga Gwaggo Aisha sun shigo da kannen ta 2 duk sunyi wujiga-wujiga ko kallon inda nake ba suyi ba suka wuce, a zuciya ta na ce," chab Gwaggo Aisha ana cikin tashin hankali tunda bata harare ni ko ta tsaya ta zage ni ba, lalle yau tana cikin matsala, d'aki suka shige suna neman mafita. Har gari ya waye ba'a cimma abu d'aya ba sai shige da fice suke, sun samu Baban mu da maganan yace toh me zai mata, ta riga da ta fita a hannun sa lafiya dan haka sauran ya rage musu ita da mijin ta. Gwaggo Aisha takaici ya hana ta sauran sauran bayanin nashi tayi ficewar ta, ta rasa ina zata kai kukan ta a share mata hawaye, babban burin ta shine a raba auren domin jiya da daddare ita da kannen ta daga gidan Hajaran suke suka ja mata kunnen kada ta yarda ta bashi kan ta duk rintsi duk wuya dan gobe-goben za'a raba auren nasu sai gashi har sha biyu ta kusa babu alamun nasara ko kad'an. Gwaggo Aisha bata gama shiga tashin hankali ba sai da d'ayan kanwar ta da ta tura gidan Hajara dan a dubo mata lafiyr ta ta dawo da mummunan labarin cewa Haladu yayi nasaran kusantan Hajara jina-jina suka same ta abun babu kyan gani ko taimaka mata bai tsaya ba ya tsallake ta yayi tafiyar shi. "Yanzu fisabillilahi duk fad'an da muka yi mata sai da ta sakewa wannan mayaudarin jiki ya gama da ita?" Gwaggo Aisha ke tambaya tana goge hawaye da gefe zanin ta. "Ba laifin ta ba ne shi mijin ne tantiri, ta bamu labarin komai cewa da ta fara mishi taurin kai shine d'aure ta a jikin gado yayi abinda ya ga dama da ita wai bata isa ta hana shi more kud'in sa ba" 'yar uwar ta ta bata amsa. "Amma wannan yaro anyi tsinanne Allah ya isa tsakani da shi, ina zan shiga da wannan abin kunyan, kayyah " yanzu kam kuka Gwaggo Aisha take tsakani da Allah tana tunanin tayaya zata kalli idon 'yan gidan bayan duk abubuwa da tayi musu wai ita 'yar ta zata auri mai mota. "Mama kada ki tada hankalin ki domin nayi miki alkawarin saka ki farinciki, ba zan tab'a kula kowa ba kuma ba zan auri talaka ba sai mai kud'i" Jamila ke fad'an haka da take sauraron su tun d'azu ba tare da sun sani ba,d UK kallon juna suka tsaya yi babu wanda ya iya bata amsa sai dai ita Gwaggo Aisha ido ta zuba mata tana nazari tare da hasko yiwuwa da nasara a cikin abinda ta fad'a domin Jameela tafi Hajara kyau da tsarin jiki nesa ba kusa ba. Haka akayi wannan wunin a tsaye babu wanda ya lek'a gidan Amarya wasu ma saboda bakinciki a ranan suka koma inda suka fito shiyasa gidan namu ya zama shiru kaman ba biki ake ba. Bayan kwana 2 da bikin Hajara Yaya na yazo da rana bayan azahar cikin kananan kaya wandon kaman na sojoji sai bakin t shirt da bakin glass sosai yayi kyau, muna hira a kofar gidan mu yana tambaya ta me da me nake bukata a walimar saukar mu? Ni kuma ina ce mishi bana bukatan komai duk abinda ake bukata mun gama shirya su. A wannan lokacin ashe Baba yana gida ya dawo saboda wata bukatar shi lokacin da yazo Yaya na bai zo ba yana ciki ya zo dan haka bai san da zuwan shi ba,yana d'aki Gwaggo Aisha tabi shi tana magiya akan yayi wani abu akan al'amarin Hajara a raba auren domin muddin tana raye ba zata tab'a barin auran nan ya dad'e ba. Bata san duk haushi ya cika shi ba tazo ta ishe shi da surutu alhalin shi in ya tuna tsoro ya hana shi gaisawa da Yaya na da yanzu yana cikin kud'i yanzu gashi bashi da kud'i a hannu, tsaki yaja yana bin ta da mugun kallo ya ce," ke Aisha wai wace irin mace ce ke da zaran kin ga mutum ya shigo gida sai ki bi shi da korafin ki na banza da na wofi yarinya tana gidan mijin ta shine kike neman wai ni uban ta inje in fito da ita wannan wani irin rashin kan gado ne, toh ba dani ba wallahi kije can ki gama haukan ki kada ki kara tunkara ta da wannan iya shegen ko kuma ranki yayi mugun b'aci". Yana gama maganan shi ya mike a fusace zai fita ya juyo ya ce," ba sai kin kara gani na a gidan ba balle ki zo ki takura ni" Fita yayi rai a b'ace yana ta masifa shi yasa kai zai fita da sauri ya koma baya yana tunanin anya idon shi dai-dai ya nuna mishi kuwa? Kara lek'a kan shi waje yayi yaga dai da gaske ne Yaya na ya gani fuska a murtuke wai shi ala dole yayi fushi me yasa ban fad'a mishi maganan saukar namu ya d'auki nauyin komai na ba nayi da kai na. "Innalillahi wa inna ilahi rajiun wai shi wannan yaro banda bala'i irin nasu na sojoji meya kawo shi da rana tsaka yana muzurai sai kace anyi mishi dole" Baba ke fad'in haka bayan ya koma cikin zaure ya manne da bango wai duk dan kada Yaya na ya gan shi. Da kyar na shawo kan sa ya daina fushin muka ci gaba da hiran mu cikin annashuwa da shaukin soyayya, abinda bamu sani ba ashe Baba yana nan mak'ale a zaure yana jiran tafiyan Yaya na ya samu shima ya tafi majalisa, yaki komawa cikin gida kuma saboda rigimar su da Gwaggo Aisha kada taga ya koma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99