Chapter 80
Chapter 80
fashe da kuka sosai jin ta ambaci sunan waya nace " yanzu Baban mu yana cikin wannan halin shine babu wanda ya kira ni dan a gaya min?" "Baban ku karami shi ya hana a gaya miki sanin cewa ba zaki tab'a kwantar da hankalin ki ba dole kice zaki fito shi kuma baya son fitowan naki saboda ko cikakken wata 3 baki yi a d'akin ki ba" Inna Asabe ce ta bani amsa a daidai wannan lokaci kuma Baban mu karami da Zafar suka shigo tare da sallama. Amsawa su Inna sukayi suna gyara lullub'in jikin su ya durkusa har kasa ya fara gaishe su kai a k'asa, amsawa sukayi suma kawunan nasu a kasa sun kasa kallon shi a zuciya ta na fara gulman shi ina dube shi yanda yake ta tsunne kai kaman da gaske. Suna gama gaisawa Baban mu karami yaja shi zuwa b'angaren Baban mu da yake a rufe ya bud'e suka shige ciki, bayan wucewar su Inna ta ture ni daga jikin ta tana " ke Kam ban san ranan da zakiyi hankali ba ya zaku taho tare da mutum ki shigo ki bar shi a waje ba tare kinyi mishi iso ba?" Baki na turo mata na shagwab'a zanyi magana ta nuna min hanyan ciki tare da had'e fuska, banyi gardama ba na juya zan shiga kenan naji muryan Hajara cikin ihu ta ambaci suna na nima na juyo cikin murna ina amsa mata da d'an karfi ta taho cikin sauri muka rungume juna sannan muka shige ciki su Inna kuma suka cigaba da aikin su. A can b'angaren Baban mu kuma koda suka shiga Zafar zubewa ya karayi a k'asa ya fara gaida shi cikin sauri Baban mu karami ya dakatar dashi yana haba ya zauna akan kujera mana ai sun riga sun gaisa a waje. Tashi yayi ya zauna amma bai hau kan kujeran ba ya sunkuyar da kai yana sauraron Baban Dije daya fara koro mishi bayanin yanda al'amarin ya faru da irin wahalhalun da suka sha amma ko takamaimai inda yake basu sani ba balle akai ga maganan fito dashi. "Tun farko da na samu labari da ba zai kai har war haka a hannun su ba kasan wani lokacin mutane suna yiwa mutum cune su Kuma ba zasu bi diddigi ba su kama mutum su jefa cikin barracks d'in su shikenan in mutum bashida gata sai a nemi labarin shima a rasa but insha Allah akwai abokina da mukayi karatu tare a abroad Baban shi Marshal ne zanyi mishi magana in Allah ya yarda komai zai zo karshe" . Cike da farinciki Baban mu karami ya fara mishi godiya amma ya dakatar dashi yana " haba nima ai Baba nane dan bana son Abba na yaji labarin ne saboda wasu dalilai amma da waya kawai zaiyi ba tare da mutum yaje ba zasu sako shi". Nan ma Baban Dije gyad'a mishi Kai yake cike da gamsuwa da bayanin nashi domin karshen ta in Abban Zafar d'in yaji wannan labarin babu dad'i ko dan kare mutuncin sa hakan yana da kyau, sai yaji Zafar d'in ya kara birge shi . Sun dan kara tattaunawa sannan yace zai tafi wajan friend din nashi duk yanda sukayi zai zo musu da labari kamin nan nima zai barni anan sai in ya dawo sai mu koma tare, har bakin gate ya rako shi sannan suka rabu. Ni kuma muna parlour Inna da ya sha gyara sai kamshin turaren wutan sandal yake nake ce ma Hajara " ni dai nayi fushi tunda irin wannan abu ya faru ace harda ke wajan masu boye min, ba dan Dije ta Kira ni tayi min jaje ba Ina can ban san me yake faruwa ba aiko ba abinda zan iya yi zan taya shi da addu'a". " Ke ni tunda abun ya faru da washe gari naso a fad'a miki ko dan mijin ki kila zai iya yin wani abu amma Baban Dije ya hana kuma yayi gargadi kan kada a kuskura a gaya miki wai yaushe aka miki aure " Hajara ta tari numfashi na. Haka muka yini muna ta hiran mu da Hajara a parlour Inna har kusan Azhar sannan Maa da yan uwan Baba da suke gidan ta suka shigo nan suma suka hau murnan zuwa na daga baya kuma muka jajantawa juna aka zauna ana maida abinda ya faru har wannan lokaci Gwaggo Aisha tana ciki bata leko ba duk da hayaniyan mutane da ya cika gidan dan harda makota duk sun shisshigo. Kasa hakuri nayi na sassauta murya na tambayi Hajara ko ina take? Ita kuwa cewa tayi ta fita anguwa tunda sassafe ta boye min, ni kuwa abin ya bani mamaki ace ana cikin wannabe halin har ta iya zuwa anguwa. Zafar tun a mota ya kira abokin shi mai suna Hamis kan yana Ina? "Ina gida " ya amsa mishi bai bari ya Kara cewa wani abu ba ya katse kiran tare da yin hanyan Pori dan a wannan anguwan yake da zama, tafiyan kusan minti 40 ya kawo shi kofar gidan Hamis horn d'aya kawai yayi mai gadi ya bud'e mishi gate ya shigo hadadden gidan daya qawatu da flowers kana ganin gidan kasan shima ya taka kasa . Parking yayi a wadatattacen parking space na gidan ya fito ya nufi cikin gidan cikin takun katsaita da ya zama jikin shi, door bell d'in ya danna ko second 30 ba'ayi ba aka bud'e kofan wani matashin saurayi da ba zai wuce sa'an shi ya bayyana a gaban shi yana murmushi yace " wai da gaske kake dama zaka zo, ni wallahi ban d'auki abin ma da gaske ba sai da gan ka da idona" ya karasa yana bashi hanya . Shiga yayi ciki bakin shi d'auke da sallama bai kula abinda Hamis d'in yake ce mishi ba, shima Hamis d'in murmushi yayi yabi bayan shi bayan ya rufe kofan, anan hadadden parlour nashi suka iske kyakkyawar matar shi da cute kids d'in su mace da namiji sun baza toys a tsakiyan parlorn suna ta wasa abin su gwanin sha'awa. Gaishe shi sukayi da kanuri ya amsa musu yana musu murmushi maman su ma gaishe shi tayi sannan ta tattara kayan wasan yaran tayi ta kai su d'akin su sannan ta had'o drinks ta kawo wa Zafar ta shige ciki. Gaisawar su ta abokai sukayi Hamis na kara tsokan shi amma bai tanka ba ya shiga yi mishi bayanin abinda yake tafe da shi. "Hahhh dama na sani haka kawai ba zaka tuna dani har ka kawo min ziyara ba saida dalili" nan ma bai ce mishi uffan ba sai ma kara daure fuska daya karayi dan ya riga ya san dole sai Hamis ya mishi iskanci kamin ya saurare shi. Haka ko ya karaci neman maganan shi Zafar bai kula shi ba daga baya kuma ya koma serious suka fara magana akan abinda ya kai Zafar d'in gidan sa. "Ban san me yasa ba yanzu duniya ta lalace da zallan mugunta, mu talakwan ma kenan da ace wani mai mulki ne yayi hakan sai ace dan Allah ya bashi saurauta yake taka mutane. "Mutum ya san shi kad'ai ya shuka tsiyar shi amma in yaga abun zai rufta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99