Chapter 77
Chapter 77
ka kasance da ita ko sau d'aya ne, yaro yaro ne ni tunda kace min zaka iya auren ta tun a lokacin na san there is something special about her in your heart da kaima baka san da shi ba, but for now ya kamata ka sani cewa ka riga da kayi nisa a cikin son ta....." " Enough of this bullsheet Sadeeq kada ka kara tara ta da wannan banzan maganan, ba son ta nake ba I repeat myself ba sonta nake ba....." Ya fad'a a tsawace tare da ficewa fuuu cikin fushi kaman zai tashi sama, dariya Sadeeq yayi yana " zaka dawo ne ka same ni yaro". [12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *51&52* A gidan mu Inna ta cigaba dafa abincin sadaka suna rabarwa , Inna Asabe da Hajara suna taya ta kullum sai dai har yau Gwaggo Aisha bata ce ci kan mu ba ko Kuma ta fito su jajantawa juna game da kame Baba da akayi , kullum tana d'aki ko motsinta ba'a cika ji ba. Ta d'auki fushi da Hajara sosai kan taki yarda su karasa aikin da suka fara akan Zafar ga kuma aikin abincin sadaka da take taimakawa su Inna ya kara tunzura ta shiyasa ko kallon inda take bata yi, itama Hajaran share ta tayi domin tana cike da takaicin halin ko in kula da take nunawa akan halin da Baban mu yake ciki dan haka kowa tsabgar gaban shi yake. Jameela kuwa yau ta kai kusan wata bata leka gida ba sannan babu wanda ya san inda take kuma babu wanda ya damu da ya neme ta ko dan sun saba ganin haka sai ranan da taga dama take dawowa gida. Yauma su Inna suna cikin aikin su sai gata ta shigo cikin maye kaman yanda ta saba, ko sallama batayi ba ta fad'o musu cikin gida tana layi. Cak ta tsaya tana bin su da kallo baki bud'e cikin murya irin na 'yan maye tace " wato biki ma kuke a gidan nan shine babu wanda ya fad'a min, da ban zo na iske ba shikenan sai kuyi ya wuce ni ko? Ala dole kun mayar dani saniyar ware...." Tab'e baki Hajara tayi ta cigaba da aikin ta ba tare da ta kara kallon inda take ba sai kanwar Baban mu Gwaggo Hinde da suka iso yau da safe ta bata amsa da " kaji min ja'irar yarinya a gidan uban wa aka ganki da za'a fada miki abinda yake faruwa a gidan, keda kika saka yawo a gaba da shaye-shaye toh uban ku sojoji suka tafi da shi yau kwana 2 bamu san ina suka kai shi ba....." Ga mamakin su dariya suka ga ta kyalkyale dashi harda rike ciki, saida tayi mai isar ta sannan tace " dan Allah ku kaini wajan sojojin nan in basu tukuicin abinda sukayi koda round d'aya-d'aya ne, wallahi sun matukar birge ni su Baba ana can ana girban abinda aka shuka. Ke kuma Inna ya kamata kifi kowa murnan wannan al'amarin ko dan cin kashin da yayi akan ki amma dan rashin zuciya shine wai harda ke ake addu'an fitowan shi, Allah yasa ya dauwama acan su gana mishi irin azaban da yayi ta gana mana tun tasowar mu" Tana kaiwa nan tayi hanyan d'akin su tana cigaba da wasu suratai da ita kanta bata san ma'anar su ba. Da ido duk suka raka ta har ta shige sannan kanwar Baban mu tace " toh Allah ya shirya mana zuri'a" da ameen suka amsa mata suka cigaba da aikin da yake gaban su. Gwaggo Aisha ce ta tare ta cike da farinciki dan duk abinda ya faru akan idon ta akayi shi domin tana tsaye ta jikin windown ta tana kallon su. "Allah miki albarka jameela ta kece kad'ai kika biyo halina a cikin ku, inama ace baki b'ata kan ki da shaye-shaye nan ba da kin cika duk wasu buruka na da 'yar uwar ki ta kasa cika min" cewar Gwaggo Aisha. Cikin muryar ta na 'yan maye tace " ke wai umma meyasa ba'a hiran arziki dake ne, kina wani zancen shaye-shaye ki sani ko kece kika tab'a ba zaki iya rayuwa ba sai da shi,kin san nishadi'i da ake samu kuwa in ansha......" Ta karasa harda lumshe ido alamun abinda ta fad'a har cikin zuciyar ta haka take Gwaggo Aisha kuwa kallon takaici ta bita dashi ba tare da iya cewa uffan ba. ********************** "Kai kar ka b'ata mana lokaci ko a kara mayar da kai inda aka fito da Kai ne?" D'aya daga cikin manyan sojojin da ya fara fusata da inda-indan Baba ya daka mishi tsawa. "A'a zan fad'a wallahi....wallahi zan fad'a ranka ya dad'e" Baba ya amsa cikin sauri. "No ka bari a kawo d'ayan partner shi d'in zaifi sai suyi mana bayani gaba ki d'aya" cewar babban cikin su, ba musu wasu 2 daga cikin kananan sojojin suka juya zuwa wani b'angare dake can nesa dasu shi kuwa Baba har a wannan lokacin kan shi a kasa yake ya kasa d'agowa sai had'a zufa da yake kaman ana mishi wanka. Bayan kaman minti goma yaji dawowar su tare da ingiza wani ya zube a kusa dashi har yana bige baba da yayi tangal-tangal kaman zai fad'i da kyar ya samu yayi gaining balance din shi ya zauna amma har yanzu bai d'ago ba balle yaga waye aka kawo. " Kai d'ago ka dubi mutumin gefen ka nan" Baba yaji an daka tsawa amma duk da yaji muyar da akayi maganan sai bayi saurin d'agowa ba domin duk a zaton shi da wanda aka kawo yanzu suke, a babu zato balle tsammani yaji saukan gindin bindiga a gadon bayan shi har sai da ya kwanta saboda azaba " how dare you ana yi maka magana kana jin mutane". Yaji wanda ya buga mishi bindigan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99