Chapter 66
Chapter 66
zuba santi,sai da nayi nak sannan na tattara sauran na kai kitchen ban gan shi a parlorn ba ban kuma bi ta kan shi ba nazo na cigaba da charting na. ****************** Washe garin ranan da suka dawo daga wajan boka Gwaggo Aisha tasa Hajara wanka da sassafe ta shirya wai ta taho gida na su fara aiwatar da kudurin su tunda wuri, bata musa mata ba ta shirya tsab tayi kwalliyar ta cikin doguwar rigar ta na atampa daya amshe ta sosai,tana bari tayi breakfast kamin ta fita amma ta hana ta tace in azo nan gidana taci. Haka ta fito wajan 8 da wani abu ba tayi nisa da gidan namu ba ta samu kwata ta jefa maganin a ciki tayi wucewar ta, bata son zuwa gidan da sassafe haka ta san duk yanda akayi kila ko farkawa daga bacci bamuyi ba, tunda ta shigo anguwan da nake ta fara jan kafa dan bata san kowa a anguwan ba da ta shiga ta dan ja lokaci har sai Zafar din ya fita kamin ta shigo. Dole haka ta karaso kofar gidan tayi knocking mai gadi yazo ya bud'e mata kofan ta shigo daga ciki sannan ta gaishe shi cikin girmamawa da yake ya dan manyan ta, amsa mata yayi cikin kulawa kasancewar yaji dad'in yanda ta gaida shin. "Dan Allah Baba masu gidan sun tashi kuwa?" Ta tambaya shi lokacin yana shirin komawa dakin shi. "Gaskiya bana jin sun tashi dan sai kusan goma sannan muke kin motsin farkawan su" ya amsa mata. " Toh dan Allah zan zauna a nan kamin su farka" tace tana nuna mishi wasu kujerun roba da suke can gefe cikin furanni. "Toh toh shikenan ki zauna sai sun fito" yace yana shigewa dakin shi, karasawa tayi ga kujerun ta zauna tana ajiyar zuciya samun relief ta ciro wayar ta daga cikin jaka ta fara game dan ya rage mata zaman kad'aici, ya ko taimaka matan dan bata san lokacin da taja a wajan zaune ba hankalin ta duk yana kan wayan taji saukan ruwa kaman daga sama a jiki ta, a firgice ta mike tana " innalillahi wa Inna ilaihi raji'un" a masifance ta juyo da niyyan ciwa wanda yayi mata wannan danyen aikin mutunci sai dai tana jiyowa idanun su suka sarke dana juna shima ya taho da niyyan bata hakuri saboda sam bai kula cewa da mutum a zaune a wajan ba domin kullum yazo haka zaiyi aikin shi ya koma ba tare da yaga wani na gidan ba gwara shi Zafar din sukan had'u wasu lokutan. Da kyar ya samu bakin bata hakuri cikin sanyin muryan shi da ya zame masa jiki, sai a lokacin Hajaran ta dawo hayyacin ta ta janye idon ta akan shi a kunyace tare da ce mishi babu komai. Ajiye tiwon hannun shi da yake bawa flowers ruwa dashi yayi cikin sauri ya koma can inda ya ajiye kayan shi wajan Baba mai gadi ya d'auko wani babban handkie ya dawo duk tana tsaye tana bin shi da ido yazo ya goge mata ruwan da ya jika kujera da take kai sannan ya dube ta wannan karon fuskar shi d'auke da murmushi yace " ki zauna Hajiya kiyi hakuri wallahi ban lura da mutum a wajan bane d z an kullum Ina zuwa aiki ban tab'a cin karo da wani a nan zaune ba shiyasa". Zama tayi a hankali itama fuskar ta d'auke da murmushin tace " kada ka damu na san ba da gangan kayi ba, nima na zauna a nan ne kamin masu gidan su farka daga bacci, ba matsala ka cigaba da aikin ka nagode". " Toh Hajiya nima nagode" yace yana komawa kan aikin shi sai dai tunda ya fara hankalin shi gaba daya yana kan ta haka itama ta kasa natsuwa hankalin ta kacokan yana kan shi sai kallon shi take ta kasan ido dan ba laifi shima kyakkyawa ne gashi da hasken sa dan yafi ta haske sosai. Suna had'a ido sai su sakarwa juna murmushi a haka har ya kammala aikin shi ya dawo wajan ta yana ko ya taya ta zama ne tunda har yanzu da sauran lokaci, bata musa ba ta bashi dama ya zauna sai gashi suna hira kaman sun dad'e da sanin juna kamin Zafar ya fita har sunyi exchange na phone number tsakanin su. Zafar ya fito zuwa gaishe da iyayen shi kaman yanda ya saba ya shiga mota ya wuce su sun ga fitowan shi Amma shi sam hankalin shi bai Kai kan su ba yaja motan shi ya fita bayan mai gadi ya bud'e mishi gate. Koda Zafar ya fita sai da suka kara kusan minti 20 tare kamin su rabu ta samu daman shigowa cikin gidan a lokacin ni kuma na gama breakfast nazo nayi kwanciya ta naji salkamar ta, cikin ihun murna na fito na rungume ta zan iya cewa bayan yinin bakwai da akayi sai yau wani nawa yazo min dan haka cike da farincikin na tarbe ta ina tambayan ta Inna ta da mutanen gida tace min duk suna lafiya. Bayan gama gaishe-gaishe na gabatar mata da sauran abincin da na rage ta fara ci muna hira cikin tsananin farincikin da kewar juna. Shi kuwa Zafar tunda ya tafi gidan su hankalin shi na kaina dan ya kasa sakin jiki suyi hira kaman yanda suka saba, bini-bini sai kallon agogo yake har Abban shi ya gano shi yace" ya kamata ka tashi ka koma gida son dan my daughter tana bukatan kulawar ka musamman a halin da take ciki yanzu". "Wani hali take ciki kuma?" Mom da tundazu taki saka baki a hiran nasu ta tambaya a d'an rikice. "Ke kuwa ai zaki fimu sanin halin da take ciki tunda ke macece, yau ta tashi bata da lafiya wai tana fama da jiri da ciwon kai kinga alamun ciki sun bayyana a tare da ita amma fa a nawa hasasshen kenan ko kunje asibiti?" Abba ya amsa mata da wadatattacen murmushi saman fuskar shi yana kallon Zafar daya duke kai shima yana murmushin tare da girgizawa Abba kan shi. "Ja'iri ji wani murmushi dan Allah Hajiya yaran yanzu da shegen son 'ya'ya suke" ya karasa yana dungure mishi Kai. Mom da tayi suman zaune ko jin abinda yake fad'a ba tayi ba har yayi musu sallama ya fita ya bar ta baki bud'e. Anan Kuma nida 'yar uwata sai hira muke zubawa yanda tun daga kofar shigowa zaka ji hayaniyar mu ba dan komai ba sai na labarin sabon saurayi da tayi na gidan mu take tana yayi mata amma tana gudun kada yaji ta tab'a aure da haihuwa ya guje ta... Ni kuwa ina kara karfafa mata giwan cewa babu wanda zai kalle ta yace ta tab'a aure balle har ace ta haihu, muna cikin haka Zafar ya dawo gidan jiki a sanyaye amma tunda ya fara jiyo murya ta cike da nishadi muna hira yasa ya shigo da karfin shi, sallama yayi ya tsaya daga bakin kofa fuskar shi d'auke da tsantsan farincikin samu na a haka da yayi, bude min hannuwa yayi alamun inzo gare shi har zan watsa masa harara na tuna cewa ashe fa in a gaban mutane ne drama muke
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99