Skip to content

Chapter 8

Chapter 8

Ba Sonta Nake Ba Book One Complete Hausa Novel 1,216 words 0 views Progress saved
Download Book

sauri na fito ina goge gumin jikina,kallon tausayi tabi ni dashi ta san Allah bai bata haihuwa dayawa ba amma alhamdullilahi tana alfahari dani domin jumm'ar da zatayi kyau tun daga laraba ake gane ta. Na zata zatayi min fad'a ko ta ce wani abu akai amma naji tayi shiru bata ce komai ba sai tagumi data zuba tana yawan ajiyan zuciya,da taga zaman ba zaiyi mata ba ta mik'e ta saka hijabi tare da yi min gargad'in kada in fita koda k'ofar d'aki ne kuma kar in kula kowa duk abinda zasu ce min. Bata jira amsa ta ba ta fita daga gidan zuwa gidan su wato gidan kakanni na da muke makotaka dasu,da sallama ta shiga. Kakata Ya Jalo da suke kira da Maa tana soya gyad'a na sayarwa ta amsa tana mata sannu da zuwa,bata gama suyar ba ta sauke gyad'an ta taso sanin cewa in taga kafar Inna ta a gida da dalili ne ya kawo ta duk da kasancewar muna makota basu bata daman zuwa gida any how ba. "Bintu komai da kike gani na duniya mai wucewa ne sannan kowa yayi hakuri zai ga riba a gaba dan haka bana son kina sawa kan ki damuwa ko kad'an ki cigaba da hakuri wata rana sai labari" cewar kaka ta kenan ganin damuwa karara a fuskan Inna ta,dama haka take mata kullum koda tazo da damuwar ta bata bari ta fad'a sai dai tayi mata nasiha tare da kwantar mata da hankali ta koma gida. "Nagode Maa Allah ya kara girma amma ba matsalan gida ne ya kawo ni ba akan Zareefa ne...." nan ta kwashe labarin Abdulbasit tun farko har zuwa yau da yazo ya tafi. Shiru kaka tayi tana tunani kaman na second 20 can ta d'ago ta ce," a yanda na fahimci maganan nan yaron nan bashi da aibu da gasken sa taimakon yake yi in da bashi da gaskiya a yanda kika ce yana da kud'i nan ba zai tsaya yi miki wannan dogon bayanin ba balle ya gaya miki asalin sa,in kuma da yana da niyyan cutar da ita da tuni ya cutar da ita dan haka ki kwantar da hankalin ki Allah ne ya dubi zuciyar ki ya kawo wanda zai taimake ku ke da 'yar ki cikin ruwan sanyi". Cike da gamsuwa maganan mahaifiyarta ta ciro kud'in ta bawa Maa dubu uku a ciki amma taki karb'a ta ce," ki bar shi ki had'a dana wajan naki ki saka Zareefa makarantan gaba kaman yanda kika ce". "Maa akwai saura ai zasu isa ki karb'i wannan d'in ki saka albarka" cewar Inna kenan. Dubu 1 kawai ta zara a ciki ta mayar mata da sauran tare da cewa," Allah ya sanya albarka". Sun d'an tab'a hira kad'an sannan tayi mata sallama zuciyar ta fari kal ta dawo gida. D'ari biyar ta cire ta bani a cikin kud'in tace inje in sayo naman miya harda kayan miya,cike da murna na fita a guje yau za'a dafa shinkafa a gidan mu kuma harda nama abinda ada sai sallah yake faruwa. Ina dawowa Inna ta fito ta hura wuta ta fara girki nan da nan ko k'amshin miyan ta ya cika gidan, Inna Asabe ce ta fara mita," oh in da ranka zaka sha kallo yanzu fisabillilahi wannan abinci da aka samu ta haramtaccen hanya shi za'a girkawa 'ya'yan mu su shi?" Ta karasa maganan tana kallon gwaggo Aisha ko zata ce wani abu. "Hmmm ni yara na ba zasu ci ba dama kowa ya san ni ba irin ku bace ina da abinda zasu ci nan wata ko 3 ne koda ace bana sana'a dan haka ku kuka sani" Gwaggo Aisha ta fad'i haka tana yiwa karamar 'yar ta da muke sa'anni da juna kitso wato Jameela. "Ke kuwa daga magana sai ki wani dawo kaina kina wani cika baki,meye naki bamu sani ba wallahi mun san inda Hajara take zuwa tallah da abinda yake tafiya wallahi duk mun sani, a toh kada a cika mana baki kuma ba'a karya kusa da gida" Inna Asabe take mayarwa Gwaggo Aisha magana cikin fushi dan taji haushin maganan da ta yab'a mata. Nan fa fad'a ya kaure ba abinda kake ji sai ifacce-ifaccen su suna zagin juna tare da tonon asiri kala-kala, sai Maman Dije ce da ta gaji da hayaniyar tasu tazo ta shiga tsakanin su sukayi shiru. Inna ta dai tana gefe tana aikin ta ko inda suke bata kalla balle tayi gigin raba su domin ta sha gwadawa a baya sai fad'an ya dawo kan ta data fahimce su sai ta kama kanta ta koma gefe ta zama 'yar kallo. Ana kiran sallah magariba Inna ta gama girkin ta duk da taji sun ce ba zasu ci ba amma haka ta nemo kwanukan kowa ta zuzzuba musu ta bani na kaiwa ko wacce d'akin ta suka bini da zagi da tsinuwa kuma wai inzo in d'auke tsiyar mu amma nayi musu kunnen uwar shegu domin Inna taja kunne na kan ina ajiye musu in juya in basa ci su bawa almajirai amma ni kar in d'auko. Sai bayan sallah isha'i Baban mu ya shigo dama ko girkin Inna tane baya shigowa d'akin mu bare yaci abincin mu dan haka Inna tana jin muryan shi tace in d'auki abincin shi in kai mishi. "Na'am" na cewa Inna ba tare da na shirya ba jin tace wai in kaiwa Baba abinci,sai naji abin wani banbara kwai. "Ki kaiwa babanku abincin shi nace" ta kara maimaita min,amsawa nayi na d'auki tiren abincin da Inna ta d'aura kwanon tuwo daban miya ma daba sai kofin silver mai murfi da ta zuba ruwan randa mai sanyi. A tsorace na nufi d'akin nashi ina jan k'afa dan na san karamin aikin shine ya koro ni da abincin,ba yanda na iya haka na karasa bakin k'ofan d'akin cikin rawan murya nayi sallama,da yake tsanan da yake min bana wasa bane nan da nan ya gane murya ta cikin tsawa ya ce," uwar me kike nema a nan?" "Inna tace ta ce in kawo abinci" na bashi amsa cike da fargaba. "Ita Bintu dan yau ta haukace shine zata aiko ki kawo min jagwalgwalo,kafin in kirga uku ki bar nan ko kuma in na tashi wallahi...." Ai ban bari ya karasa ba na jiyo cikin sauri Allah ya taimake ni babu kowa a tsakar gidan dan haka babu wanda ya ganni na shige d'akin mu. Inna murmushi tayi ganin na dawo da abincin ta ce," koro ki yayi ko?" Gyad'a mata kai kawai nayi bata kara cewa komai ba ta sauke min tiren akaina ta zuba mana namu muka fara ci abin mu. Saida naji ciki na barazan fashewa sannan na hakura da tura shinkafa da jan miyan da nake na kwashe kwanukan na fitar sai ga sauran yaran ma suna fitowa da nasu kwanukan suna ta tsid'e hannu su da iyayen su suka ce ba zasu ci ba. Ina dariya na koma d'aki nake bawa Inna ta labari ta kwab'e ni kan bata son surutu in nemi waje in kwanta,ba musu kuwa na kwanta kan shimfid'a ta cikin abinda bai kai minti biyar ba bacci yayi gaba dani. Da washe gari da sassafe Innata da ta tashi

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99