Chapter 64
Chapter 64
ta jawo plate gaban ta ta zuba malmala kwaya d'aya tak ta zuba miya kaman bata so ko mai kyankyamin abincin ta kai baki a ba zata sai da ta lumshe ido, dan abincin yayi mata wani irin dad'i domin batayi tsammanin zata ji abincin haka a tunanin ta tunda ni 'yar talakawa ce ban iya komai ba. Zafar da yake kallon duk drama dake faruwa ya saki murmushi domin shi shaida ne in ta girki ne bani da ta 2, Abba sai santi yake ta zubawa wai ya akayi na san yana son abincin gargajiya, ashe wai dole su daina ganin Zafar wajan neman abinci a gida bayan cika baki da yayi ta musu a baya ko mata 4 be dashi abincin Mom d'in shi kad'ai zai ci. Mom tana ji bata ce uffan ba koda suka gama Abba cewa a ajiye mishi snacks din nashi ne shi kad'ai, Mom sai tabe baki take tare da jin haushi Abba yana tsinka su a gaban wannan jinjirar yana abu kaman bai tab'a cin abinci mai dadi ba, ni kuwa duk farincikin ya lullube ni ganin yanda Abba yake ta yabon girki na dan ni nayi ne kawai banyi zaton zasu ci ba balle in samu irin wannan yabon. Tattare kayan Mom ta fara Nima nayi saurin mikewa dan in taimaka mata amma cikin tsare gida tace in bar su, duk sai naji jiki na yayi wani irin sanyi na kasa komawa in zaunan, muryan Abba naji yana min magana yace " zo nan ki zauna daughter akwai hirar mu ta musamman dake" ya karasa yana nuna min gefen sa da hannu. Da kyar na ja kafafu na zauna a inda ya nuna min yayi kasa da murya yace " kyale uwar nan taku haka take bata son in tana aikin mijin ta wani ya saka hannu wai ladan ta zai ragu shiyasa bata barin masu aiki suyi sai ita da kan ta" ban san lokacin da murmushi ya kwace min ba dan salon da yayi maganan dole ne yasa mutum dariya. Zafar dake d'ayan gefen shima dariyan yayi dan ko shi baiji dad'in abinda Mom din nashi tayi ba amma yanzu daya ga Abba yana min barkwanci sai yaji hankalin shi ya kwanta kuma yaji dadi har cikin ran shi. Wani envelope mai dan girma da yake kan kujeran bayan shi ya d'auko ya miko min yace " ga wannan tukuici ne daga gare ni kan yanda kika bada gudumawa wannan stubborned son nawa ya koma gentle boy". Kasa karb'a nayi sai bin foldern nake da ido ina imagining what could be inside? Zafaar da yake sauraron mu ya b'ata fuska cikin shagwaba yace" Abba pls mana". "Kwarai hakane my daughter ki karb'a Mana" yace ganin na kasa karb'a, hannu na rawa na saka na amsa tare da cewa " nagode Abba Allah ya kara girma da daukaka" Ameen my daughter" ya amsa min cikin jin dad'in addu'an da nayi mishi. Muna cikin haka Mom ta dawo ta zauna hankalin ta da imanin ta duk suna kan abinda ke hannu na wondering ya akayi yazo hannu na, ganin irin kallon da take min yasa Abba ya maimaita mata abinda ya faru tare da ce mata " saura kema ya kamata ki kawo taki gudumawar" Dama ance in talaka ya rabe ka in ba kayi sa'a ba toh kaima sai ka talauce, if not ya zaayî ya d'auko takardun company shi na buga ledodi dugurungum ya bada kyautan shi ma yar mitsitsiyar yarinya? Duk a cikin zuciyar ta take wannan maganan amma a zahiri kuma sai ta kirkiro murmushi tace" lalle Alhaji kana ji da wannan surkuwar tamu sai dai ai ko ni ban kara komai ba nakan ma ya wadatar kyautan company fa ai ya wuce wasa" ta karasa zuciyar ta na suya. "Company? Ni Zareefa aka bawa kyautan company?" Na tambayi kaina da kaina hawaye na kokarin zubo min amma na shanye ina kara kasa da kai. " Ga complimentary card dina daughter duk private numbers dina suna jiki a duk lokacin da yayi miki ba daidai ba ko kina bukatan wani abu kada kiji nauyi ki Kira ni Kai tsaye ki fad'a min kinji ko?" Yanzu Kam sai da hawayen yayi nasaran zubo min nayi saurin saka gefen gyale na goge na saka hannu na amsa kamin in samu bakin magana naji muryan Mom da ta kasa hakuri tace " kaima dai Alhaji sai kace kaga wani alamun rashin zaman lafiya a tare dasu ko Kuma wacce bata da iya..." Wani kallon ki shiga hankalin ki da Abba yayi mata yasa ta had'iye sauran zancen nata tare da kawar da kai gefe, saida ya maye fuskar shi da murmushi sannan yace " ta riga da ta shigo wannan family dan haka muma iyayen tane ko kin manta ita zata haifo mana magajin gidan nan a gaba?" A razane take kallon Abban Jin wannan furucin da yayi me yake nufi kenan, duk shekarun da ta b'ata tare da shi ya tashi a tutan babu? Lallai ko sai ta kara tsayawa da kafafun ta ko ayi mata tsakiyar da ba ruwa. Amma a zahiri sai ta gyara fuskarta da nemo aron murmushi da ya tsaya mata a iya leb'e tace " hakane Alhaji Allah ya kara bud'i". Gaba d'ayan su suka amsa da "Ameen " daga nan Abba da Zafar ne kad'ai suka cigaba da hiran su game da business daya yake taya shi a gida ,zuwa kusan karfe 10 Zafar yace zamu tafi Abba yana ta saka mana albarka ita kuma Mom cewa kawai mu gaida da gida. Ga mamaki na har muka shiga mota bai kara hantara ta ba saima murmushi da yake ta faman sakewa shi kad'ai yana tukin sa cikin kwanciyar hankali ni kuma zuciya ta tana wani waje daban Ina rike da complementary card din Abba ina ayyana abubuwa da yawa a raina. [6/16, 9:22 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *INNALILLAHI Wa INNA ILAIHI RAJI'UN Muna taya 'yar uwar mu PRINCESS FATIMA MAZADU na babban rashi da tayi wato yayan ta HRH. ALH ABUBAKAR MUHAMMAD KWAIRANGA ( SARKIN FUNAKAYE) UBANGIJI ALLAH ya jikan shi da rahama yasa mutuwa hutu ce a gare shi AMEEEN* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99