Skip to content

Chapter 81

Chapter 81

Ba Sonta Nake Ba Book One Complete Hausa Novel 1,189 words 0 views Progress saved
Download Book

dashi sai ya nemo wanda a baya yake jin haushin sa ko kuma Wanda ya tsaya mishi a rai ya mishi cune , baiji ba kuma bai gani ba za'a je dashi a rufe shi, wani shikenan mai kara jin labarin shi saboda bashida gata ko kuma a kashe shi gaba d'aya a shafe labarin shi amma insha Allah zamu samo bakin zaren tashi muje barracks d'in su Dady muji kasancewar shi baya yarda da zalinci kuma baya yarda ayi a gaban shi sai dai in a rashin sani, shiyasa ko wani case in ya shigo hannun shi sai yayi bincike sosai kaman wani police kamin ya yarda a yanke hukunci" ya karasa yana mikewa tsaye yana kwalawa matar shi kira. Fitowa tayi da sauri tana karasa daurin dan kwalin ta yace mata "zamu d'an fita ne da Zafar " D'an Bata fuska tayi alamun bata ji dad'in hakan ba cikin lallashi yace " don't worry I will not stay long yanzu zan dawo". fuska ta sake tana murmushi tace " shikenan my love sai kun dawo Allah ya tsare" da Ameen" ya amsa Yana kissing goshin ta sannan ya juyo ya kalli Zafar da ya tsaya musu kallon sha'awa yana ji inama haka zaman mu yake a gida. Maimalari barracks suka nufa bayan sun fito suna hirar su jefi-jefi a cikin motan har suka iso bakin gate da sojoji suke birjik suna binciken ababen hawa da zasu shiga ciki, suna duba motan su ganin Hamis ne yasa suka basu hanya suka wuce, haka sukayi ta wuce gates sun kai 4 kamin su shigo ainihin inda office d'in Baban Hamis yake... Basu karasa ciki ba saida akayi musu iso sannan suka shiga katon office d'in nashi daya k'awatu da kayan alatu sai kamshi da sanyin ac ke tashi, da murmushi ya tare su yana daga ina suke haka yana nuna musu wajan zama. Zama sukayi a inda ya umarce su sannan suka gaishe shi ya amsa kamin su fara koro mishi bayanin suka ji knock a kofan office d'in wani soja ne ya bud'e ya shigo da wasu files a hannun shi ya kame a gaban shi tare da salute sannan ya ajiye files d'in kan makeken table dake gaban su ya kara salute ya fita. Jawo files d'in yayi ya fara duba su a tsanake yace " uhum ina jin ku ". Hamis shi ya korowa Baban shi bayanin da Zafar ya mishi tsab ba ragi ba kari, shi Kuma Zafar shiru yayi har ya gama fad'a mishi komai amma bai dago ya kalle su ba ya cigaba da duba files na gaban shi har zuwa wani lokaci mai dan tsawo sannan ya ajiye su a gefe ya d'ago ya zubawa Zafar ido yace " menene sunan nasa kuma yaushe hakan ta faru?" " Mallam Hassan sunan shi kuma yau kwana 3 da kama shin". Gyad'a Kai yayi cike da gamsuwa yace" muna da similar case da wanda ka fad'an nan amma shi ba yanda ba muyi dashi ya gaya mana gaskiya ba yaki cewa komai , so mun had'a su waje d'aya sannan an saka musu cctv camera a d'akin da suke dan mun san dole sai sunyi magana a tsakanin su". Duk shiru sukayi suna sauraron shi ya koma ya jingin da kujeran da yake kai yana jujjuya da shi yace " wannan files d'in ma na bayanan su ne bari mu tabbatar da abu d'aya zuwa gobe sai in neme ku ko?"yace yana duban su. Godiya sosai Zafar yayi mishi sannan sukayi mishi sallama suka shiga mota suka kama hanyan gidan Hamis sai dai bai shiga ciki ba a bakin gate d'in gidan shi Zafar ya sauke shi da yake a motan shi suka tafi shima ya nufo gidan mu . A can barracks din kuwa bayan fitan su Zafar Baban shi ya kira wayan da suke aikin tare kan su same shi a office d'in shi, ba'a d'auki lokaci mai tsawo ba suka taho su 3 kowanne su sai da ya fara mika gaisuwan shi gare shi wanda hakan yana nuna cewa shine babban su, gyad'a Kai yayi tare da yi musu alaman da hannu kan su zauna ba musu suka nemi waje suka zauna . "These are files about those people case yanzu sergeant Ibrahim ya kawo min su " yace yana ciro wata 'yar karamar memory card a cikin gidan ta ya saka a system dake gaban shi yayi wasu latse-latse sai ga shi ya fara nunawa ta can gefe kaman tv dukan su kuwa suka maida hankali kan screen d'in ga su Baba sun fito b'aro-baro a jiki suna zaune da kumburarrun fuskokin su. Shiru ranan da aka Kai su basuyi wani magana mai mahimmanci ba sai da washe gari da yamma sannan suka zo inda suka ga sun fara magana a tskanin su.. " Wai kai har yanzu saboda dakikancin ka baka gane ni bane bayan duk bayanin da nayi maka?" Cewar wanda ya kira kan shi da Abulbasit ma Baban mu. Murmushin takaici Baba yayi mishi yace" in nagane ka da ban gane ka ba duka d'aya ne tunda har ka iya min irin wannan kazafin ka kawo ni nan, ban san me nayi maka ba kake son ganin baya na......" Dariya da Abdul basit ya kece dashi shi ya hana Baba karasa maganan da yayi niyya ya zuba mishi ido kawai yana bin shi da ido dan shi bai ga abin dariya a cikin wannan halin da suke ciki ba. "Bani kad'ai ba kayiwa ba hatta iyalan gidan ka sun matukar cutu da mugun halayyarka, tayaya Allah zai baka mata da yaya ka mayar dasu abin wulakancin ka, ko abinci baka basu sun ci ba balle aje ga wasu abubuwan rayuwar na yau da kullum. Ko a yanda na shigo rayuwar Zareefa na d'auki nauyin karatun ta da sauran su amma a matsayin ka na mahaifin ta da Allah ya daura maka alhakin kiwon su baka tab'a damuwa ka san wanene ni ko kuma ka damu ka san a ina suke samun kudin ba saima nuna zalamarka da kwad'ayin ka akan abinda suke samu , farkon zuwa na da niyyan cutar da ita nazo domin kuwa mai gida na yana safaran yara kanana sai dai yanda naga rayuwar da take ciki da kuma yanda mahaifiyar ta ta nuna min ita ba mai son abin duniya bace duk da talaucin da suke ciki, ba karamin burge ni tayi ba sannan ta goge bakin niyya dake zuciya ta Allah ya darsa min tausayin su a raina tun daga wannan rana nake taimaka musu da zuciya daya. Ni maraya ne na taso banida kowa Kuma wannan rashin gatan shi ya jefa ni a halin da na tsinci kaina a ciki, ni dai na taso na ganni Ina garari a gari ban san kowa nawa ba cikin yawon da nake Allah ya had'a ni da Emeka shi ya kasance uwa da uba a gare ni ya saka ni makaranta kasancewar shi Christan bai sa ya canza min suna ko addini na ba hakan ya sa nima na rike shi da hannu 2 inayi mishi biyayya kaman shi ya haife ni" dago kai yayi yaga Baba ya zuba mishi ido yana sauraron yayi lakwas

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99