Skip to content

Chapter 57

Chapter 57

Ba Sonta Nake Ba Book One Complete Hausa Novel 1,298 words 0 views Progress saved
Download Book

nazo zan wuce na zata zai bar min kofan in fita ne sai naga matsawa kad'an yayi yace in wuce,ban san lokacin da na daga kai na kalle shi ba naga ya wqni kankantar da Lulu eyes din shi yana kallo na. " Toh... Z...an ...wuce" nace mishi murya ta na rawa. Na hana ki wucewa ne?" Ya tambaya Yana kara gyara tsayuwar shi, girgiza kai na kawai nayi ina maida shi kasa, da hannu ya min alama da inzo in wuce. Tafiya na fara yi kaman wacce take tsoron taka kqsa ba dan komai ba sai dan sanin in zan wuce sai jikina ya gogi nashi, karkata jiki na nayi sosai yanda ba zai hadu da nashi ba, na ko yi sa'a dan ko bai hadun ba har na kusa fita naga ya saka hannuwan shi duka 2 ya tare kofan ya zama banida daman fita Kuma banida daman komawa ciki. "Ni kike guduwa da wani kazamin jikin ki, ni banyi kyaman zaki had'a jikina da naki ba sai kece zakiyi?" Jikin na karkarwa kawai yake tsaban tsoro ban tab'a samun kusanci da d'a namiji kaman haka ba sai yau so ban san ya zan kwatanta muku halin da na shiga ba a wannan likacin. Sai da yaga ya gama tsoratani sannan ya bani hanya, haba kaman in kifa haka na fara sauri na shiga d'akin na maida kofa na rufe na jingina a jikin kofan ina maida numfashi, sai da na dawo hayyaci na sannan na tsaya kallon d'akin ko ina fes yake a gyara kaman d'akin mace sai kamshi ke tashi, ajiyar zuciya nayi na wuce bathroom din shima dai fes yake. Haka dai na had'a ruwan omo da hypo na goge ko ina na bayin nan ya kara kyalli da walwali, sai da na tabbatar komai yayi na bude kofa na fito. A razane na koma baya ganin shi tsaye a bakin kofan daga shi sai dogon wando ya cire rigan jikin shi, rab'awa nayi na wuce shi Kuma ya shigah har zai rufe kofa naji shi yana cewa in tabbatar na gama gyaran d'akin ya fito. Da toh na amsa mishi yana shiga na fara gyara mishi gado da jera pillows sannan na fara mopping din d'akin inda babu carpet, har na gama zan fita wata zuciyar ta zuga ni da yanzu shikenan ba abinda zanyi in rama yaci bulus kenan?? Bakin kofan bathroom din na dawo hankali na zubar da ruwan omo kad'an yanda ba zai iya ganewa ba na fita da sauri ina addu'an Allah yasa ya taka wajan da na huta takaici da ya guma min yau. Jikin kofan na d'aura kunne na na tsaya jiran fitowan shi, aiko ban dad'e da tsayuwa ba naji karan fad'uwa muryan shi da karfi yace " ouch my back" haba da gudu na koma daki Ina dariyan mugunta raina fari kal. [6/16, 9:19 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *35&36* Zaune take kan sallaya da carbi a hannunta tana ja a hankali tare da kurawa waje d'aya ido,kallo d'aya zaka mata ka gane tana cikin damuwa kullum cikin wannan yanayi take tunda aka fitar dani daga gidan sai dai in damuwar yayi mata yawa,sai tayi nafila tana kai kukanta wajan mai kowa mai komai kan Allah ya bamu zaman lafiya mai d'aurewa. 'Yan biki duk sun watse tun ranan yini saboda an riga da an daina zaman bakwai sai dai gobe ne satin auran kuma a goben uwa take zuwa ganin d'akin 'yar ta amma ita tana ganin ba zata je ba hakan zai fi mata kwanciya hankali bata son taje ta ganni cikin wani yanayi ko kuma cikin tashin hankali hakan zai tsaya mata a rai ya hana ta sukuni, ta yanke shawaran zamanta a gida ta bini da addu'oi samun zaman lafiya. Tana cikin zancen zuci baba yayi sallama ya shigo,sallamar nashi ne ya katse ta ta juyo tana kallon shi tare da amsawa a hankali tana bin shi da kallo yanda ya sauya zaka ce wani hamshakin mai kud'i ne,duk mamaki ya cika ta dan zata iya cewa tunda bikin nan yazo sai yau ta saka shi a ido saboda taga bashi da niyyan yin komai ya zauna akan abinda Abban Zafar yace na cewa kada suyi min komai su zasu yin min. A lokacin ta nemi su zauna suyi magana ta fahimta bai kamata su sake musu komai ba kaman wacce bata da gata koda kayan d'aki daya ne ya kamata suyi min gudun gori watarana amma yaki sauraronta sam,wai tunda sunce abari a bari kawai itama tunda ta lura da takun shi ta fita harkan shi tayi duk abinda Allah ya hore mata dana 'yan uwa da abokan arziki cikin ikon Allah kuma asiri ya rufu. Zama yayi a kan kujera ya d'auki remote ya kara volume na TV data rage,kaman ta share shi sai kuma taga koma yaya ne shine gaba da ita,tashi tayi ta kowa mishi ruwan sanyi da snacks na biki ta ajiye a gaban shi ta gaida shi tana zama a gefen shi. Amsawa yayi sannan ya d'an sha ruwan da ta kawo mishi yana kare mata kallo yana murmushi yace"kinga yanda kika dawo kaman kece Amaryar gaya min menene sirrin?" murmushi kad'an tayi bata ce komai ba wai yau ita yake fad'awa haka ya manta duk munanan kalamai da yake furta mata da kuma aurar dani ga wanda ba son sa nake ba.......... "Tunanin 'yar albarka kike ne ,nima nan kullum sai nayi tunanin ta a raina toh ya za'ayi dole ne kiyi hakuri kuma kiyi murna tunda tana gidan hutu" yace yana gyara zama "Yauwa ni abinda ya kawo ni daban, kin gan ni nan wallahi bikin nan ya cinye min duka kud'ad'en hannu na shine nace bari inzo ki bani wani abu na san 'yar ki na aiko miki tunda maganan da nayi ta jaddada

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99