Chapter 23
Chapter 23
irin wannan kyau ba sai yau, sai kallon kai na nake a madubi, su ma 'yan wajan sai yaba kyau na suke. Da zan fita na fara kokarin saka hijabi na, 'yan wajan ne suka min caa wai kar in saka daurin net d'in zai lalace tun ban isa gidan auren ba,tunda a mota muka zo in tafi a haka. Ba dan naso ba na fito a cikin saloon d'in ina takawa a hankali kaman mai tausayin kasa saboda tudun takalmin kafa na har na iso bakin motan Yaya na bai sani ba kasancewar ya kwantar da seat ya kwanta da earpiece a kunnen shi ban san me yake saurara ba. Bud'e kofan motan nayi na shiga na zauna kamshin turare na shi ya isar da sakon isowa ta a gare shi ya bud'e ido ya sauke su a fuska ta da nima shi nake kallon, mun dad'e muna kallon juna daga baya nice na sauke nawa idon kasa ina d'an murmushi. Ina jiyo shi sai da ya sauke ajiyan zuciya har sau uku sannan ya tashi ya zauna tare da gyara kujeran, ya juyo ya kara kallo na kaman zai ce wani abu kuma ya fasa ya tada mota muka kama hanyan gida,har muka iso babu wanda ya yi magana. Yana yin parking na ce," nagode Yaya naaa zan shiga ciki sai anjima". Har na bud'e kofan na fita bai amsa min ba na fara tafiya, nayi kaman taku uku naji muryan shi ya ce," Zareefa...." Da matukar mamaki na juyo dan jin suna na a bakin shi yau. " Kinyi matukar kyau....,kyan da baki ba zai iya furawa ba, amma dan Allah in muna tare ki rinka saka hijabin ki" yana gama maganan shi yaja motan shi ya tafi. A hankali na juya zuwa cikin gida ina murmushi da mamakin me yasa yake yawan cewa in saka hijabi ba. Ina saka kafa gidan mu ido ya dawo kai na kowa ni yake kallo da gudu Dije ta zo ta rungume ni cikin ankon da suka hana ni yi sai naga ashe da a lokacin ma naga ankon ba sai sun hana ni ba da kaina zance ba nayi. Can b'angaren su taja ni muka tafi tana in bata labari meye sirrin? A nan muka zauna ina bata labarin saloon d'in da muka je na fara jin sautin kid'a daga waje. Da mamaki na ce", kaman kid'a nake ji?" "Eh dama naji Hajara da kawayen ta zasu kawo DJ tun shekaran jiya suke zancen Ina ga shi d'in ne suka kawo" Dije ta bani amsa. "Taso muje mu gani...taso muje" cewar Dije tana jan hannun na . Muna zuwa kofar gida muka ga Amarya da kawayen ta suna ta rawa, jan hannu na Dije ta fara wai muma mu shiga nace mata ta shiga ina zuwa. Ina daga gefe ina kallo kawai naga mutane sun rufu a kai na suna min liki, maza da mata amma mazan sun fi yawa na rasa ta ina ma suka zo dan ni dai ban san su ba. Neman shiga gida nake amma sun tare ko Ina ba hanyan wucewa daga cikin matan naji wata tana ", ke Hindu ki zo ga Amarya nan kiyi mata liki" Da mamaki na d'ago na kalle ta na ce", ni fa kanwar Amaryar ce ga Amaryan can" na karasa ina nuna musu inda Hajara da kawayen ta sukayi sororo suna kallon mu. "Eh ga Amaryar can wannan kanwar ta ce " wata kanwar Gwaggo Aisha ta fad'a tana harara ta. Jiki a tsabule suka juya ga Amaryan su suna kallon ta har taji ta muzan ta, ni dai ban san ya suka kare ba na shige cikin gida na bar su. Da daddare bayan an kai Amarya gidan ta Dije tazo d'akin mu a lokacin ina kwance ina chatting da Yaya na. "Zo...zo...zo muje ki sha labari zo muje" ta ce tana jan hannu na ina ta tsaya in ajiye waya amma ina haka taja ni muka tafi bangaren su. "Mijin Hajara da ake cewa mai kud'i ne ashe karya ne,kin ga gidan nata gidan yawa mutane sun fi shida a ciki ga d'akin nata ya yiwa kayan ta kad'an ke abun b dad'in gani wallahi. Ina matar da ta zo tace ita 'yar uwar sa ce tayi magana a kan an fasa dinner ashe gidan haya ce ta had'a su". *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku* [10/10, 7:42 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *12* Bangane ba Hajara me kike nufi wai?" Na tambayi Hajara cike da rud'u. Kamo hannu na tayi muka zauna a bakin k'ofar d'akin su sannan ta fara magana," hmmmm duk abinda Alhaji Khalid mai gidan gona ya fad'a a gidan nan ashe zuki ta malle ne sunan shi haladu kuma sana'ar sa kuma bawa dabbobi abinci a gidan gonan Alhaji Mukhtar dake Sabon layi". Samun kaina nayi da matukar jin haushin sa sannan ga tausayin 'yar uwata daya rufe ni lokaci guda,cikin wani irin yanayi nace", amma Allah ya isan Hajara makaryaci kawai in bashi da kud'in menene amfanin shirga mata wannan karyan? Allah sarki Hajara ko wani halin take ciki yanzu?" "Lalle Zareefa kin bani mamaki meye naki na wani zakewa haka, wallahi kada ma kiji tausayin ta ita ta jawowa kan ta ko ince su suka jawo dan harda uwar ta su ala dole dake zasu yi gasa, chab ni wallahi ko kad'an bata bani tausayi ba hasali ma dariya ta nayi ta sha, a mota ina ta tunanin yanda Gwaggo Aisha zatayi in taji wanga batu" ta karasa cikin shekiyanci tana dariya. Girgiza kai na nayi hawaye na taruwa a ido na, na ce mata," Dije kenan taya ba zan tausaya mata ba ko kin manta cewa 'yar uwata ce jini d'aya yake yawo a cikin jikin mu" "Na sani mana amma ba kya ganin yanda suka saka ki a gaba su da iyayen su sun hana ki sakat ke da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99