Chapter 79
Chapter 79
suma a gaba na sannan ya durkusa Yana leka fuskata. "I'm very sorry for what happened yesterday dan Allah kiyi hakuri na miki alkawari hakan ba zai kara faruwa ba ki bar komai ya wuce let's be friends for the rest of the time we will spend 2geda" yace cikin sanyin murya. Ban iya d'agowa ba nayi shiru ina sauraron shi dan na rasa a wani mizani zan auna maganganun nashi, dan sun dan sanyayya min jiki kamin in samu abin cewa waya ta da na bari a kitchen ya d'auki kara, kamin in mike har shi ya rigani mikewa kitchen din naga ya koma sai gashi ya dawo da waya ta a hannu ba tare da yayi magana ba ya miko min.. Ajiyar zuciya na sauke bayan na gama maganar shi a zuciya ta na cewa ba girki da d'auko waya zai rinka yi ba ko menene zaiyi ba zai tab'a cin nasara a kaina ba tunda na riga da na gane manufarsa a kaina. Hannu na saka na karb'a daidai wayar ya katse duba sunan nayi naga Dije ce babu bata lokaci na kira ta kaman kuwa jira take bugu daya kawai ta d'aga cikin ihu tace " kaji matan mayan Alhazawa basa d'aukan kira sai dai su kira mutum". Murmushi kawai nayi dan yanda yake zaune kusa dani yana jin abinda muke cewa ba zan iya sakewa inyi magana yanda raina take so ba nace " Dije ba kya rabo da zolaya ya kike?" " Lafiya lau Zareefa ya muka ji da wannan iftila'in daya fad'awa Baba ku?" Ta amsa min cikin sanyi. " Wani iftila'i kuma Dije?" Nima na tambaye ta cikin rashin fahimta. "Ke kuma akwai ki da wani zance, wani iftila'i kuwa banda wanda sojoji suka tafi da Baban ku" " Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un!!! Kawai nake iya maimaitawa cikin mugun tashin hankali da ban tab'a tsintan kaina a ciki ba, Baban mu a hannun sojoji toh meya faru meyasa babu wanda ya gaya min a gida. Kuka na fashe da Ina" Baban mu sojoji suka kama Dije tun yaushe , meyasa babu wanda ya fad'a min" Cikin rashin jin dad'in kotobarar da tayi dan ita duk a zaton ta na sani shiyasa ta kira ta min jaje dan duk zuwanta gidan mu bata gani na ashe ban ma ji ba, maimakon ta bani amsa kawai sai ta katse kiran. Cikin tashin hankali na kara Kiran ta amma sai naji wai switch off, jefer da wayan nayi ina kara fashewa da kuka na kama jeka ka dawo a tsakar parlour na rasa ina zan saka raina inji sanyi. Kafadata naji ya riko ta baya tare da juyo dani muna fuskantan juna ya saka hannu ya share min hawayen da suke ambaliya a fuska na wasu na zubowa yace" shhhh ya isa haka kada ki sakawa kan ki ciwon kai, naji duk abinda aka fad'a miki a waya kada ki tashi hankalin ki kina da ni duk inda sojojin suka kai Baba nayi Miki alkawarin ni zan tsaya har sai naga ya fito". Kallon shi kawai nake kaman yau na fara ganin shi murna zanyi akan abinda ya fad'a ko akasin ta, duk bayan maganganun da ya fad'a min jiya why zai cigaba da nuna min kulawa haka? "Komai maza zasu iya yi dan cimma burin su " zuciya na ta kwab'e ni kamin in samu amsan bashi ya katse da " shhhhh kada kice komai kije ki d'auko hijabin ki mu tafi gidan ku muji ya maganan take"... Ban San lokacin da murmushi ya subuce min na farincikin zanje gidan mu cikin matukar jin dad'i nace " thank you Ya Zafar....." Nagode da soyayyar ku gare da wannan novel Allah ya bar kauna, nima ina muku fatan alkhairi my fans. [12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *43&44* Shiru motan ya d'auka babu mai magana a cikin mu sai dai yana tuki amma duk hankalin shi a kaina yake, ni kuma na maida kaina gefe ina kallon titi lokaci-lokaci na kan share hawaye da suke zubo min na kasa dannewa sai tunanin halin da Baban mu yake ciki nake, toh meya aikata haka da har sojoji suka tafi dashi... Sojoji bama police ba, Baba da ko police ya gani duk sai ya gigice balle ace yana barracks na sojoji ya Allah ya fitar da shi cikin sauki, duk a zuciyata nake ta wasi-wasin nan har muka iso kofar gidan mu cikin azama na fara kokarin bud'e kofan in fita naji ashe ya saka lock. Juyowa nayi na watsa mishi wani kallo da yake nufin menene haka? Bai nuna fushi ko b'acin rai ba yace " calm down pls ki bi komai a sannu insha Allah ba abinda zai samu Baban mu I promised u this, in kin shiga ciki pls ki min iso wajan kanin Baban inji ta ina zan fara" yana karasa maganan shi yayi unlocking d'in kofan jiki a mace na bud'e na fita. Ina fitowa Kuma sai naji kaman in d'iba da gudu in shiga ciki nake ji amma na daure banyi gudun ma sai uban sauri da nayi ta zubawa na tura gate din na shiga daga can na hango Inna ta da Inna Asabe suna ta kiciniya da murhun itace a tsakar gida zasu daura abincin sadaka, ai ban san lokacin da na kwasa da gudu na isa gare su sai kawai Inna ji tayi an fad'o mata akai . A zabure ta juyo muka had'a ido sai washe baki nake dan farincikin da nake ciki bai zai tab'a misaltuwa ba, itama cikin farincikin ta rungume ni fuskarta d'auke da zallan murnan gani na cikin koshin lafiya ga wani dan haske da na kara kana gani kasan ina cikin hutu. "Zareefa kece haka sulum bako waya?" Inna Asabe tace tana kallon mu cikin farinciki itama, sai a sannan na
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99