Skip to content

Chapter 74

Chapter 74

Ba Sonta Nake Ba Book One Complete Hausa Novel 1,291 words 0 views Progress saved
Download Book

mai nisa sannan yaji an ingiza shi ya Fad'i kasa daga bays suka kunce mishi idon, farko ma hasken rana ne ya fara dallaro mishi ido yayi sauri ya runtse idon tsawa da yaji an daka mishi yasa ya bud'e ido babu shiri yana rarraba ido duk da yanda yake jin zafin ranan har cikin kwakwalwan shi. Manyan sojoji ne sun kai su goma zaune akan kujera da wani table a gaban su, gefen su kuwa hagu da dama duk wasu sojojin ne rike da bindigu sunyi layi-layi. "Ka shirya gaya mana komai Mallam Hassan?" Daya daga cikin mayan sojojin ya tambaya yana kallon Baba da yake durkushe a gaban su kan shi a kasa kaman mai neman gafara, cikin rawan jiki yace " wallahi Allah zan fad'a muku ...Allah zan sanar muku da duk abinda kuke son sani ". Gyad'a kai sukayi gaba dayan su cike da gamsuwa " yace toh menene shirn ku na gaba?" Mukut Baba ya had'iye wani bushasshan yawu na fargaba da ya tsaya mishi a makoshi ya bud'i baki yace" Shirin mu na gaba shine........". Tofa me Baban ZAREEFA yake shirin dad's🤭🤭🤭🤭 [12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *47&48* Bai san adadin lokaci da ya b'ata a cikin duhun nan ba yana nan dai zaune ne kawai amma ba zai iya cewa dare ne ko rana ne ba, addu'oi kuwa babu wanda baiyi ba yana son yin sallah amma rashin sanin inda gabar yake da kuma rashin ruwan alwala yasa ya hakura. Zuwa wani lokaci ya tuna dai ko azahar ba'ayi ba suka kawo shi nan dan haka ya tashi yayi taimama da d'an kasa- kasa daya samu ya kabbara sallah, azahar,la'asar da magarib ya sallata ya sallame saboda tashin hankali da yake ciki ko yunwa baya. Haushin karnuka da yake jine ya san cewa dare yayi nisa sosai bai tsaya b'ata lokaci ba ya kawo sallah isha'i da 'yan nafilfilu ya raya daren ko gyangyad'i baiyi ba balle bacci, rabon da Baba yayi nafilan dare shi da kan shi ya manta balle Kuma wani. Da washe gari yana zaune makoshin shi duk ya bushe saboda kishi yaji an dallaro mishi fitila a ido wanda ya haddasa mishi rintse idanun nashi babu shiri har wani radadi yaji idon na mishi ko dan ya kwana a cikin duhun ne oho. "Oga he don wake up" yaji wani kakkausar murya daga wajan ana magana,tafiya ya fara ji na mutane da bai san adadin su ba sun nufo inda yake a tsorace ya mike tsaye jikin sa na karkarwa yana jiran yaga ta ina zasu bullo dan har yanzu bakin shi da suka buge yana nan a kumbure har fuskan shi. Cak yaji kafan ya d'auke lokaci daya amma baya iya ganin su kasancewar har yanzu hasken daidai fuskan shi yake wajan su kuma duhu. "Kai ne Mallam Hassan ko?" Yaji an daka mishi tsawa, jikin shi na cigaba da bari ya gyad'a musu kai. "Open ur mouth and answer me my friend, nace kaine Mallam Hassan?" Duk da bai fahimci turancin da akayi mishi ba amma cikin sauri ya amsa da " nine...nine Mallam Hassan ranka ya dad'e". " Good bana son gardama ko taurin kai ka gaya mana menene next target d'in ku me kuke shirin aikatawa a gaba?" Yaji wani murya daban ya tambaye shi cikin gurb'ataccen hausar shi. Cikin rashi fahimta yake kallon inda yake jiwo muryan su duk da baya iya ganin su dan kwata-kwata bai gane inda zancen nasu ya dosa ba. "Ka bamu amsa ba wai ka tsaya zare Mana ido ko kuma kana so mubi da kai yanda muka bi da partner ka" wani cikin su ya kara daka mishi tsawa, Baba duk ya rud'e ya rasa inda zai saka ran shi yaji dad'i sannan ko kad'an bai fahimci tambayan nasu balle ya basu amsa kaman yanda suka bukata illah jikin shi da yayi ta b'ari kaman an jona mishi shocking. "Dole yayi mana taurin kai oga saboda babu wani criminal da za'a kawo ya amsa laifin shi cikin sauki but zamu bi dashi yanda muka bi da sauran. Step 1" yaji wani murya daban har yana amsa kuwwa, kalle-kalle ya fara yi a matukar tsorace kamin ya ankara yaji ruwan sanyi harda kankara suna zubowa daga sama daga inda yake tsaye nan da nan yaji wani irin sanyi da tunda yake bai taba jin irin shi ba ya rufe shi a take ya fara rawan sanyi hakoran shi na had'uwa da juna. "Ka huta cikin sanyin ka in ka shirya mana bayani zamu dawo" wani yace suka juya suka bar Baba cikin rawan sanyi yana son tsaida su amma ya gagara bud'e baki balle magana ya fito, yana ji yana gani suka tafi tun yana jin sawun kafan su har ya daina ji. ****************** A gidan mu kuwa babu wanda yayi baccin kirki saboda tashin hankali domin ganin har dare babu Baba babu labarin shi, masu nafila nayi masu addu'oi nayi in ka cire gwaggo Aisha da tasha baccin ta harda minshari, koda gari ya waye Baban Dije da wasu 'yan uwan Baban mu suka fita bin baracks ko Allah zai sa su dace su sami inda aka kai Baba. Bayan tafiyan su babban tukunya Inna ta daura a tsakar gida na abincin sadaka da tayi niyya tun cikin dare sanin cewa sadaka yana maganin masifa, Inna Asabe tana gani ta fito ta kama mata suka fara aikin tare. A can dakin Gwaggo Aisha kuma drama ce ta kaure tsakanin su ita da Hajara kan cewa wai lalle sai ta fita tazo gidana sun kammala aikin su da suka fara ita Kuma Hajara tace babu inda zata je ta bar ta taji da tashin hankali na rashin Baban mu. "Ke me yasa baki da wayo a rayuwar ki ne, ban san yaushe zakiyi hankali ba Hajara wani uban

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99