Chapter 19
Chapter 19
shi, ban musa ba yayi gaba muka bi bayan shi ya bud'e seat na bayan motan ya karb'i tiren akan yaron ya saka a ciki sannan ya min nuni da in shiga ciki nima. Sororo nayi da jug a hannu na kasa shiga kasancewar ban tab'a shiga motan shi ba kuma ga nasiha da Inna ta min d'azu, sai da ya shiga ya zauna ya ganni nan tsaye banida niyyan shiga. Kara cewa in shiga yayi nayi shiru ni ban shiga ba kuma ban tafi ba sai raba ido nake nan ya fahimci cewa tsoro nake,sai da ya nuna min cewa tunda ban yarda da shi duk shekaru da muka d'auka tare in d'auke abinci na baya ci. Ganin kaman ran shi ya b'aci yasa na d'an dosana duwawu na kad'an na zauna, yana murmushi yace toh in bud'e yaga me na dafa mishi mai dad'i. Ina bubude mishi ya ce," iyye lalle k'anwa ta an girma,ke kika girka min ko Inna ce?" *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [9/23, 4:26 AM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *Addu'ar Cin Abinci* Idan mutum zai ci abinci sai ya ce; بِسْمِ اللهِ. Bismi l-lahi. Da sunan Allah Idan ya manta to sai ya ce (yayin da ya tuna) بِسْمِ اللهِ فِي أَوَّلِهِ وَآخِرِهِ. Bismi l-lahi fi awwalihi wa akhirihi. Da sunan Allah a farkonsa da karshensa. Wanda Allah ya azurta shi da abinci ya ci, to ya ce; اللّهُمَّ بارِكْ لَنَا فِيهِ وَأَطْعِمْنا خَيْراً مِنْهُ. Allahumma barik lana feehi wa-at'imna khayran minh. Ya Allah! Ka sanya mana albarka a cikinsa, kuma Ka ciyar da mu wanda ya fi shi alheri. Wanda kuma Allah ya azurta shi da madara ya sha, to ya ce; اللّهُمَّ بارِكْ لَنَا فِيهِ وَزِدْنا مِنْهُ. Allahumma barik lana feehi wazidna minh. Ya Allah! Ka sanya mana albarka a cikinta, kuma Ka kara mana ita (madarar) *10* Rufe fuska ta nayi da hijabi na ina dariya ba tare da nayi magana ba,shima dariyan yayi ya d'auki yam ball d'aya ya kai baki ya gutsura ya fara taunawa har da lumshe ido wai dad'i ya kawo sauran baki na cikin sauri na kawar da kai na duk kunya ya gama mamaye ni. Yaci ba laifi dambun naman da kunun ayan ne dai yace su kam gida zai tafi dasu sunyi dad'i sosai ya kara da cewa duk ranan da zai zo toh ya daina cin abinci anan zan rink'a mishi yana ci, koda ya gama muka sha hiran mu yauma kaman kada ya tafi haka nake ji amma haka muka hakura da zai tafi wani babban jaka ya bani yace in bawa Baban mu sannan muma ya bamu namu tsaraban mu nida Inna ya tafi. Sai da na nemi taimakon wasu yaran sannan muka shiga da kayan cikin gida Gwaggo Aisha da sauran 'yan koron ta suka bini da harara wanda ban san ma sunayi ba. "Ni ba wai bana son yayiwa Mallam alkhairi bane ba a'a yanzu Baban ku yazo yaga wannan tulin kayan da sunan nashi, gaba zai iya neman gidan yaron yace zai je maula ya zubar miki da mutunci gaba d'aya" Inna ke fad'an haka bayan na nuna mata jakan da Yaya na yace na Baban mu ne. Shiru nayi ina tunanin maganan dan na san gaskiya Inna ta fad'a, zuwa can na fara murmushi ni kad'ai saboda na samo mana mafita. "Inna in kin bashi kayan kice mishi a hukuma Yaya na yake aiki, kinsan yanda Baba yake tsoron hukuma na tabbata daga wannan rana ba zai yarda su had'a hanya ba balle har ya roke shi" na karasa ina dariya sosai dan na tuna yanda Baba yake bala'in tsoron su ban san kome yasa b ba. Dariya Inna kanta tayi bata kuma ce min komai ba nima ban kara magana ba na kwashi tulin kayan da Yaya na ya kawo min da sunan tsaraba na fara jerawa cikin babban trolleyn kaya na. Bayan sallah magariba Baba ya shigo d'akin mu ina gama mishi sannu da zuwa na wuce wajan Dije abina na basu waje wanda sam Inna bata san hakan domin ina barin wajan zai fara kokarin canza salon hiran nasu dan haka ba b'ata lokaci ta d'auko jakar kayan tsarabar shi ta ajiye a gaban shi ta koma can nesa dashi ta zauna. Fara bud'e jakan kayan yayi yana mitan wai Inna ta maida shi dodo da zaran sun kasance su 2 a waje d'aya sai ta koma can gefe......... Kasa magana Baba yayi saima jikin sa daya fara b'ari ya zaro ido yana kallon jakan in shock kawai, Inna da ta watsar da lamarin sa tana wasu sabgogin ta bata san halin daya shiga ba sai da ta juyo, a tsorace ta mike ta nufo shi tana," Mallam lafiya meya faru?" Bai motsa ba kuma bai bata amsa ba sai da ta saka hannun ta a kafadar shi ta jijigashi da karfi tana," Mallam.... Mallam..." Sai a wannan lokaci ya firgita yaja dogon numfashi ya d'ago da kai yana kallon ta ba tare da yace komai. "Kamin magana mana Mallam meya faru nace?" Ajiyar zuciya yaja ya sauke kusan sau uku sannan ya ce," Bintu wayan nan kayan masu tsada kuma masu yawan da nake gani duka nawa ne kika ce?" Ajiyan zuciyar itama Inna ta sauke jin cewa ashe wai kayan ne suka firgita shi ta koma wajan zaman ta ta zauna sannan ta amsa mishi da nashi d'in ne. Firfito da manyan shaddodi da suke ciki ya fara bakin sa kuwa kaman gonan auduga sai da ya fito da guda shida suka kare sai takalma suma masu kyau guda 2 da huluna mu had'u a banki guda 2 da kud'in d'inki a kasa dubu hamsin. Suma ne kawai Baban mu baiyi ba a wannan rana ya rasa ya zaiyi da rayuwar sa ya d'aga wannan kaya ya kalla sai ya d'aga wancan ga kud'in kuwa ya rike a hannu gam ya kasa ajiyewa kaman
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99