Skip to content

Chapter 83

Chapter 83

Ba Sonta Nake Ba Book One Complete Hausa Novel 1,196 words 0 views Progress saved
Download Book

mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *Wannan page din naku ne masoya na kuyi yanda ku ka ga dama dashi, ina mika godiyata gare ku kan yanda kuka nuna min kauna ba abinda zance sai dai nayi muku fatan dacewa da duniya da kiyama ina matukar alfahari daku a duk inda kuke kan jajircewan ku sai da kuka sa na dawo online, Allah ya bar kauna bounch of love*. *58&59* A baya na kulla ce shi naji na tsane shi saboda duk halin da na tsinci kaina a baya shi nake daurawa laifin domin da bai guje ni ba da ban fad'a cikin tashin hankali da nake ciki ba, saidai wannan bayanai da naji yanzu ya ruguza min lissafi yasa naji zuciyata ta karye tausayin sa duk ya cika ni na irin rayuwar daya taso a ciki da kuma halin da maraici ya jefa shi a ciki. Kuka sosai nake kaman raina zai fita yasa hankalin kowa na parlour ya koma kaina suka shiga bani baki dan sun san irin shakuwar da yake tsakanin mu dole ne inyi kuka. Sai a lokacin Gwaggo Aisha ta kai duban ta gare ni a zabure tayi baya tana kare min kallo tun daga kan kayan jikina har tsarka da d'an kunne da na saka, sosai hankalin ta yayi kololuwar tashi irin rayuwar da take burin ganin yayan ta a ciki shine na samu. Bayan an jajantawa juna Baban Dije yace mu fita a bar Baba ya huta, duk muna shirin fitowa sai ga jameela kaman an jefo ta ta fad'o d'akin tana layi, ganin mutane cike da parlour yasa ta fara bin kowa da kallo har idon ta fad'a kan Baban mu da yake kwance shima yana kallon ta, for the first time yaji zuciyar shi ta kuntata da yanayin da yaga 'yar cikin sa ta zama sanadiyan rashin kulawar shi gare mu. Zaro ido tayi harda dafe kirji da murya ta yan maye tace " lah Baba dama basu kashe ka ba suka bar ka a raye har ka dawo gida...." " Ke baki da hankali ne mahaifin naki kike fad'awa irin wayan nan kalamai” Gwaggo Aisha ta daka mata tsawa ta hana ta karasa maganar da tayi niyyan fad'a. Kyalkyalewa da dariya tayi tana nuna uwar tata da hannu tace kai Umma bayan kece kika fara d'au......." Fincike hannun ta da taji uwar nata tayi yasa bata karasa abinda tayi niyyan fad'a ba tabi bayan mahaifiyarta da take Jan ta kaman ta kife suka fita a d'akin duk muka bi su da ido kowa da abinda yake sakawa a zuciyar shi, Hajara kuwa duk kunya ya rufe ta ta kasa kallon 'yan d'akin. Ajiyar zuciya Baban Dije ya sauke tare da furta " Allah ya kyauta, yanzu kowa ya fita a bar Yaya ya huta...." Bai gama rufe bakin shi ba kowa ya mike ana kara mishi Allah ya sauwake sannan muka fita tare da ja mishi kofa. Maimakon Baba yayi baccin kaman yanda akace sai dai kunan da zuciya shi keyi ya hana shi jin rad'ad'in da jikin nashi ke mishi balle har yaji wani abu wai shi bacci, yanzu wannan 'yar cikin sace a haka har take mishi fatan mutuwa saboda abinda yayi musu. Tabbas ba zai taba ganin laifin kowa a cikin mu ba domin ya cancanci fiye da haka ma dama duk wanda Bai bi hanyar da Allah yace yabi ba dole zai ga sakamakon abinda ya aikata tun kamin akai ga zuwa kiyama. Sai dai shi a yanzu babu abinda zaice sai ALHMDLLH ga Rabbil Izzatti daya ankarar dashi halin da ya jefa kan shi da iyalan sa amma ta ina zai fara gyara wannan babban barna da yayi??? Kuka sosai Baba yayi kaman karamin yaro Yana yi yana kara godewa Allah har la'asar tayi bai samu ya runtsa ba. Gwaggo Aisha bata saki hannun Jameela ba sai da ta kai ta can cikin d'aki Dan ko a parlour basu tsaya ba, watsar da ita tayi a tsakar d'akin tayi taga-taga kaman zata fad'i da kyar ta samu courage ta tsaya tana auna mata harara tace" wai ke Umma meye haka ina cikin magana zaki wani jawo ni ki kawo ni nan kaman wacce ta fad'i ba daidai ba" " Eh dole kice haka mana kina can kina kokarin tona min asiri cikin makiyana, ba zaki bari komai kike son cewa ki fad'a min a d'aki ba" gwaggo Aisha ta bata amsa itama tana mata mugun kallon. "Ni ina ruwana duk inda naga dama zanyi magana ta kuma babu wanda ya isa ya hana ni, gobe zan dawo in karasa abinda nayi niyyan fad'a sai na fad'a wallahi" tace tana mai juyawa ta kama hanyar fita. Cikin sauri gwaggo Aisha ta riko ta tare da fara rarrashinta kada tayi hakan domin ta san halin Jameela tsab zata aikata abinda yafi hakan ma tunda ba tsoron kowa take ji ba, da kyar ta rarrashe ta harda bata 200 kan ta bar maganan sannan ta hakura ta fita abinta cike da murnan ta samu na cakewa. Duk yanda nake kuka Inna bata kula ni ba wucewa tayi ciki ta kama aikin gabanta, a nan parlour na zube kan kujera na cigaba da kuka na a wannan lokaci babu abinda nake so kaman in sanya shi a ido na domin akwai maganganu dayawa da nake son muyi dashi amma tayaya zan samu daman ganin shi waye zai kai ni??? Zafar gida ya wuce direct sai huci yake shi kad'ai a mota dan sosai kukan Zareefa ya tsaya mishi a rai shaid'an kuwa sai kimtsa mishi yake kan cewa kukan rabuwa da masoyin ta take, tsaki yaja tare da dukan staring da karfi Yana " da aure na akan ta take wannan kukan rabuwa da b'arawon ko kidnapper ko? Hmmmmm I will show her" yace yana dannawa mai gadi horn kaman zai cire mishi kunne. Da gudu yazo ya bud'e gate d'in yana mishi barka da zuwa, ko kallon inda yake Zafar baiyi ba balle ya amsa mishi saima jan motan yayi dagudu kaman zai bi ta kan shi Allah ya bashi sa'a ya kauce cikin zafin nama yabi motan da kallo yana mamakin yau me ya b'ata ran mai gidan nashi haka ya shigo cikin fushi haka?? Ko parking d'in kirki baiyi ba ya fito cikin wani takun da zai tabbatar maka da ran shi a matukar b'ace yake ya nufi kofan parlour ya shiga ya kama safa da marwa shi kad'ai " na san yanzu Allah Allah take in sake ta dan ta samu komawa gare shi ko??" Ya tabayi kanshi. Toh kai meye naka a ciki in ta koma gare shi ko ka manta ba son ta kake ba? Yaji zuciyar shi tana tuna mishi abinda ya manta " yes ba son ta nake ba but dole she should mind her business kamin in sa......" Yay shiru yana jin girman furucin da yake shirin furtawa kuma yana ganin abune da ba zai yiwu ba. Jagwab ya zube akan

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99