Chapter 43
Chapter 43
da zuba musu ido ya san in har zai cigaba da nuna halin ko in kula asirin shi zai iya tonuwa. Akwai wata mata daga sudan take ta kware wajan gyaran amare Inna ta nemo kuma wai dole sai kaje gidan ta da farko ta ganki sannan zata duba gyaran daya dace da fatar ki,sun gama magana da Inna saura wai ta tura ni ta ganni, ba dan naso ba Inna tasa na kira Maryam a waya kan tazo ta rakani. Da washe gari kuwa tazo muka tafi gidan nata da yake can Shokari, koda muka je gidan ta cike yake da matan aure harda sabin amare ana tayi musu aiki dan harda 'yan mata masu taya ta tana biyan su. Tarba na musamman akay mana a babban parlour ta inda take sauke bakin ta na musamman,bamu dad'e da zama ba tazo wajan mu bayan mun gaishe ta cikin girmamawa itama ta amsa mana cikin kulawa sannan ta fara aikin ta wato rubuta duk kayakin da zasu dace da fatana da kuma gashi na sannan ta sallame kan cewa sai next week zan fara zuwa, godiya mukayi mata muka fito zuwa gida. A gajiye tibis muka dawo kasancewar Anguwan nata da nisa sosai da namu, mun shigo layin mu kenan wata had'add'iyar mota baka wuluk tazo zata fita mu Kuma muna shiga kaman ance min dago kanki ina d'agawa na tsaya cak tare da dafe kirji na da hannu biyu ina zaro ido waje duk at da same time bakina na rawa nace " YAYA NAAA..." [1/26, 7:14 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *25&26* Yanda ka san statue haka na tsaya ko motsi na kasa yi sai motan nabi da kallo da idanuwana kaman zasu zazzago kasa ga kuma zuciya ta na ta lugude kaman zai faso kirji na ya fito. " What's wrong with you Zareefa daga ganin mota sai kice ga Yayan ki, ke duk wulakanci da mutumin nan yayi miki ashe baki cire shi a ranki ba har kina tunanin zai dawo gare ki Kuma ga dukkan alamu zaki karb'e shi da hannu bibbiyu kenan...." "Maryam shi na gani fa ba imagination bane" na katse ta da muryar tausayi. "What ever, zo muje ga Inna can da kaya a hannu zata shiga gida muje mu taimaka mata ba wannan surutu mara kan gado ba" tana magana ne tare da jan hannu na muka fara tafiya ina waiwayen baya ko zan ga motan zai dawo amma har muka shiga gida banga ko kalar motan ba, kamin mu karasa Inna har ta riga mu shiga gida. A parlour muka iske ta zaune tana kallo babu lodin kaya da muka ga ta shigo dasu, zama mukayi muma anan Maryam tana yi mata bayqni akan zuwan mu gidan mai gyaran amma hankalin ta yana kai na ganin nayi shiru na zama wani iri ba kaman yanda muka fita ba. "Ke kuma lafiyan ki kuwa ana magana kinyi wani zuru dake?" Kaina na mayar kasa ina kokuwa da hawayen da naji suna son zubowa, harara Maryam ta b'alla min tana muskudawa sannan ta bawa Inna amsa. "Kyale ta Inna ni takaici ma ya hanani kula ta, muna shigowa layin nan wai kawai dan taga mota ya wuce kin ga yanda ta daskare waje d'aya wai taga wannan mayaudarin da kyar fa naja ta muka biyo bayan ki lokacin kina shiga gida ga kaya a hannun ki nace muzo mu taya ki". "Ban san meyasa taki sakawa ranta dangana ba ko kin manta aure zakiyi, haka zaki je gida wani kina wanna shirmen da shashanci? Ki kama kanki daga irin haka na gaya miki" Inna take dad'in haka cikin fushi ba tare da ta bawa Maryam amsar tambayar ta ba, nima hakuri na shiga bata ina cewa na daina ba zan sake ba Maryam tana taya ni sai da muka ga ta sauko sannan muka bari. Bayan mun huta mun ci abincin da Inna ta ajiye mana sannan Maryam ta wuce gida tare da cewa sai munyi waya. Tun daga wannan rana suka kara kaimin shirye-shirye da suke Inna ta ta zama busy sosai these days sai fita sayayya suke da Maman Dije wata rana Kuma da Inna Asabe, Gwaggo Aisha ce dai ko kallo basu ishe ta saima yad'a habaice-habaice da take. A haka satin da matan tace zan fara zuwa gyara ya zagayo na fara zuwa wajan gyaran a motan su Maryam wanda Mamanta ce ta d'auki nauyin hakan kullum driver zai zo ya d'auke ni in mun gama zuwa yamma kuma waya kawai zanyi yaje ya maido ni gida kasancewar tace ba'a son ina shiga rana saboda zai maida aikin baya. *************** A gidan su Zafar suma ba karamin shiri suke ba abinka da masu kud'i an gyara mana gidan da zamu zauna duk da sabon gini ne sai da suka Kara da d'an gyare gyare,kayan da za'a saka na cikin wannan gida Abban Zafar ne yayi order su daga kasar waje haka ma kayan lefe na suma duk a kasar waje suka had'o su, shi dai yana gefe yana kallon su yana jin ina zai iya hana su ko kuma inama zai iya fad'a musu gaskiya cewa auren da zaiyi temporary ce ba permanent ba su daina kashe kud'in su amma hakan ba mai yiwuwa bane dan yayi Imani Abban shi yaji abinda ya shirya suna iya batawa na har abada. Sadiq kuwa in ka ganshi zaka zata shine angon kan yanda ya kasa ya tsare komai yana tafiya daidai, baya ko neman shawaran Zafar yake abinsa shi kad'ai ko Kuma suyi da sauran friends d'in su saboda ko ya nema baram-baram suke rabuwa dan haka suma suka ajiye shi a gefe suke abinda ya dace. Ana saura kwana goma bikin duk an gama komai a gidan nasu had'a dasu cards da kayan da zamu saka na duk event d'in
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99