Skip to content

Chapter 39

Chapter 39

Ba Sonta Nake Ba Book One Complete Hausa Novel 1,195 words 0 views Progress saved
Download Book

sirkata ta nemi wani abu kace mata babu" yace yana dariya. Shima dariyan yayi yana kara sadda Kai kasa. Cikin wani irin kwarin guiwa ya nufi part d'in iyayen nashi bayan yayi wanka ya sha gayun shi kaman kullum sai kamshin tsadaddaun turaruka yake, tsab'anin da in Abba yana gari da kyar yake iya zuwa saboda ya san in yaje ma ba zasu kwashe da dad'i ba. Da sallama ya shiga parlour amma babu kowa sai masu aiki da suke kai kawo, kowa na aikin da yake gaban shi, zama yayi kan d'aya daga cikin royal cussion d'in da suka lamushe kusan set 2 ya d'auki remote yana canza channel zuwa aljazeera sports yaji motsin saukowan su. Ajiye remote d'in yayi ya mike tsaye ya tarbe su basu tsaya anan ba direct dinning suka wuce kowa yaja kujera ya zauna banda Mom da sai da tayi serving din su sannan ta zauna suka fara cin abinci Basu dad'e da farawa ba Zafar yaga alert na zunzurutun kud'i har 10 million cikin tsananin murna bai san lokacin daya durkusa jiki na rawa har kasa ya fara godiya yana" Abba naga sako nagode Allah ya kara girma da nisan kwana" ba dan komai ba Abba yafi shekara rabon shi daya bashi kud'i sai dai Mom ce ke bashi a cewar shi ba zai bashi kudin shi yaje yana shashanci dasu ba. Abba kuma ya kalli Mom da take bin tilon d'an nata da kallon mamaki yace" da fatan kin fahimci abinda nake nuna miki kika kasa fahimta kinga tun kamin ayi auren ta fara canza mana shi ina ga Kuma anyi auren?" "Oh yanzu duk sun d'auka wannan village girl d'in ce ta canza ni..." Muryan Mom yaji tana cewa" na fahimta Alhaji ya tabbatar da alkhairi" "Ameen Ameen addu'an ki yake bukata dama, Kai kuma a yau d'in nan ka cewa 'yar Mallam gobe zamu je mu tsaida magana da Baban ta" Murmushi da bai shirya bane ya kwace mishi jin sunan da Abba ya kira ni dashi wai 'yar Mallam. "Ja'iri ji duk wannan washe bakin dan nace gobe zamu je ne, ina ga inda aka daura auren Kuma ya zakayi?" Dariya yayi kawai yana ficewa ya nufi part d'in shi yana kara dariyan sunan da kuma na Abban shi da yake ganin auren soyayya zaiyi bai san auren contract zaiyi ba. Direct bedroom d'in shi ya wuce yana cigaba da dariyan shi yayi dialing no Sadiq , saida ya gama ringing kamn zai katse sannan ya daga yana cewa " meye ya faru??" " Hey Ni ba fad'a yasa na kira ka ba, I just called dan in fad'a maka gobe Abba zai je nema min auren 'Yar Mallam" ya karasa yana dariyan da sai da yasa Sadiq ya cire wayan a kunnen shi ya kalli screen d'in ya kara tabbatarwa eh zafard'in ne sannan ya mayar kunnen shi. "Wacece da wannan sunan ko cikin relatives d'in ka na kauyen ne aka samo maka wata". Sadiq ya tambaya. "God for bid, bakin ka ya sari d'anyan kashi mugu kawai meya had'a ni da 'yar kauye, wannan village girl da kuka had'a ni da ita mana Abba ne ya saka mata wannan funny name d'in koda yake it suits her" ya karasa yana kara saka dariya dan d more zai fad'i sunan d more yake saka shi dariya. "Ikon Allah, amma ban san Kai cikakken d'an rainin wayo bane sai yau, yarinyan da ta sace maka zuciya at first sight shine zaka ce mu muka nemo maka ita?" "Damn it wai har sai yaushe zaka fahimta ni *BA SONTA NAKE BA* kuma kafi kowa sanin why I will marry her amma ba zaka daina fad'a min rubbish ba, anyway phone no ta nake nema in fad'a mata sakon Abba" yana kawo nan a zancen shi katse kiran yayi jifa da wayan kan gadon shima yabi shi ya kwanta ringine yana huci shi ala dole an b'ata mishi rai. Ko minti 5 baiyi da kwanciyar ba yaji karan shigowan sako wayan shi, sai da yaja tsaki sannan ya bude sakon ba dan komai ba sai dan yaga daga Sadiq ne. Number kad'ai ya gani babu rubutu hakan ya tabbatar mishi da number na daya nema ne ya turo mishi, sai da ya fara saving sannan ya kira ni lokacin muna zaune da Inna tana had'a min tea dan tace inzo mu karya nace bana jin yunwa, shine ta shiga had'a min wai ko shi kad'ai in sha. Inaji har tagama ringing ban d'auka ba ganin sabon no ce, kara kira yayi Inna ta dakata da had'a shayin tace min " Wai ke ba wayar ki ake kira bane?" "Inna sabon number ce babu suna" na amsa mata a sanyaye. "Ko ba suna ai zaki daga kiji ko waye ko?" Inna ta sake fad'a min. Koda na juya da niyan daukawa naji ya katse dan haka banyi magana ba nayi shiru Inna ma bata kara cewa komai ba ta cigaba da had'a min. Miko min tayi bayan ta gama harda 🍞 tace in gusura ko kad'an amma na ce mata sai anjima, sama-sama itama ta karya bata ci wani abu dayawa ba ta ture gefe duk gani na cikin rashin walwala yana hana ta sukuni itama. Gwaggo Aisha sai bayan fitan mu da kusan minti goma ta tashi ta zauna tana goge fuskan ta da hijabin da Hajara ta lullub'a mata ba hawayen amma duk ta jike da zufa. Harara ta zabgawa Hajara da take ta jera mata sannu tayi kana tace" ke dai Allah yayi magulmaciya da kinibibi in banda gulma waye yace ki gaiyato min wacan manufukar matan can da 'yarta fitinanniyan nan?" Baki a hangame hajara take kallon ta tace " haba Umma in baki gode musu ba ba zaki tsine musu ba, ihu fa kike tayi kina birgima kan an k'ona abinda kika binne dan su cutu ita da yarta amma matan nan ta zauna tana tofa miki addu'oi ita da yarta har kika samu lafiya, mutane nawa ne a gidan nan babu Wanda yazo kan ki sai su hatta Baba ma tafiyan shi yayi ya bar ki....." "Ki min shiru wawuya kawai mai fifita uwar wasu kan uwar ta koda yake ba laifin ki bane duk asirce ku tayi Kuma wallahi ba zan saduda ba sai na warware duka mugun kulli da tayi a cikin gidan harda Baban naku..." Shiru tayi tana wur-wurga ido kaman me neman wani abu, a zabure ta mike tana " kan bala'i in na yarda shigiya nake" tana gama magana ta fice fuuu zuwa tsakar gida. Cikin daga murya ta fara magana" ina kake ka fito shanyayye kawai wallahi na gaji da rashin adalci da kake nuna min a cikin gidan dole ne ayi abu d'aya ehe" "Ke Wai wace irin dakikiya ce mara hankali meya faru da zaki zo tsakar gida kinawa mutane ihu" cewar Abba kenan daya tsaya daga nesa yana kallon ta. "Eh dole ka kira ni da sunaye da kaga dama Amma kada ka manta ko rigar sakawa na kirki baka da ita lokacin da na aure ka sai yau dan ka samu abu zaka wukanta ni, ace Wai gini zakayi a gidan baka fara ta kaina ba

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99