Chapter 75
Chapter 75
yawani irin ware manyan idanunshi yace "Bid" wani irin tsalle yayi ya shigo dakin batare daya lura da komiba yay wani irin jumping ya rungume Aabid kaman zai kadashi yace "oyoyo Bid" kyam idanunshi suka sauka akan ring din dake aman kudin har lokacin daidai lokacin Abie shima ya shigo cikin dakin, yanda gabanshi yafadi saida dan gajeren fitsari yazubomai daga wando yana tuna warning din OZo aranan da akabashi zoben kudin nan. "koda wasa karka bari zoben nan yay aman kudi agaban idanun wayanda basu taba shan jini ba, danka na zoben nan, karka bari zoben nan yay amai agaban mutanen daba yan gidaba, ka kiyaye, ka kiyaye idanu mashan jini ne kadai aka yarda su kalli zoben nan alokacin dayake baka kudi, idanun masu tsarki wanda suke gauraye da jini kadai sukeda ikon ganin lokacin aman kudin zoben nan, kariga kasan ranan dayake aman kudi sanan kariga kasan lokacin dazaima aman kudi ka kiyaye Tursoso, kakiyayeee". Wani irin race da zuciyarshi Abie yafara yasa yaji saliva bakinshi ya bushe gabaki daya zaiyi magana, yana kokarin magana amma maganan taki fitowa sai iska yake fita. "ahhh, huuuu".... Ahankali Aadil yasaki Aabid yamike tsaye kanshi narawa sosai miyau nazuba daga bakinshi, kafe zoben Aadil yayi da ido yana kallon kullutun jikin zoben yaga yakawo wuta a jan wuta a idanunshi, kanshi yagani ajikin kullutun amma dan karamin shi, yana cikin keji an rufe, ganin Aadil karami yayi yarike karfen kejin yana girgizawa yana mai magana directly. "free me, free me kafin yagama aman nan, ninekai dasuka shanye, nine brain dinka dasuka shanye, free meee nowww, yakusa gamawa" wani irin juyawa idanun Aadil sukayi sama gabaki daya kafafunshi su lankwashe, duk dakin babu wanda ya lura dashi asandare yay baya ya zube akasa gabaki daya asume akan kudaden, ihu Hamida tayi ta shigo dakin da gudu kafin ta iso Aabid ya dagashi afirgice ya rungume kanshi a kirjinshi Mami ma ta shigo daidai nan su Muhammad suka shigo da limam dawasu malamai guda biyu alarammomi, dago kai Aabid yayi ya kalli Hamida data tsaya gefe takasa zuwa kusada shi tafashe da kuka sosai tana kallon Aadil datake so ta taba amma takasa sabida yanda Aabid yarikeshi, kallan Mami Aabid yayi yace "Mami take her to your room ta nemi hijabi tasaka please" tashi Mami tayi takama hanunta suka fita daga dakin Mami ta karbo mata hijabi [12/13/2019, 9:59 AM] Aishat Muhammad: . _karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan or pay achan_ _this book is for sale, just 300 naira zaki turo ta 3107021073 first bank aisha Muhammad, idan baki da account u can send MTN card, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_ Shiga malaman sukayi suna kallon abinda ke faruwa da karfi liman din ganin yanda baban zobe ke fitar da kudi yafara karanto addu'a. "Bismillahil lazi la yadurru ma' ismihi shai'un fil-ardi wa-laa fil-samaa'i wa huwas Samee'ul Aleem" yakaranto addu'an yana tsugunnawa yakai hanunshi kan saman idanun Aadil dake hanun Aabid yabude idanun yana ganin yanda idanunshi suka juya sama baka ganin bakin ko kadan, jinin jikinshi yasha batare dayay magana ba ya kalli sauran malaman dake tareda shi, hakan yasa daya daga cikinsu yakalli baffa yace "muna bukatan ruwa a gora Alhaji danka kodai aljanu sun shafeshi kokuma da sihiri ajikinshi" gyara zama limam yayi yana kallon zoben dayake fitar da kudi har lokacin yafara karatun al Qur'ani, sauran malaman suka zauna kusa dashi suka jonashi suna karantowa atare da karfi sosai kaman zasu fasa dakin da zakin murya, wani irin girma zoben yakarayi kaman an huramai iska, Suleman Big Mum tarike gam dan wani irin tsoro taji tanaji kowani mutum na dakin tambayoyine fal aransu daga ina zoben nan yake? Daga ina tayaya yazo dakin nan? Abie ko kyafta ido bayayi yay kokarin dazaiyi yay magana yakasa kaman wanda aka dinkemai baki yana kallon yanda zoben ke kumbura yana kumbura yana kumbura. Ayoyi daban daban suke karantawa suna fuskantar zoben wani irin girgiza zoben yafara yana rawa rawa kaman abinda ke shirin fashewa kafin tuss yawani irin fashe ya tarwatse, kumfane yafara fita daga bakin Aadil jikinshi na girgiza kaman mai ciwon farfadiya yana mikewa yana bankarewa da sauri Aabid dake rike yana neman fizgemai yace "innalillah, Malam my brother meke faruwa dashi" cigaba da karatu malam yayi batare daya amsa Aadil ba, wani irin girgiza dakin yafara kaman saukan aradu hakan yasa malaman suka kara karfin karatu suna kiran Allah, rike Baffa Muhammad yayi gam yayi dakin na kara yana making sound kaman sound din guguwa, wutan dakinne sukai kara suka fashe tareda tarwatse wa dakin yay duhu dumdun abunku dadama darene kara karfi karatu malaman sukayi Aabid ya rungume Aadil da jikinshi ke rawa sosai har lokacin miyau nafita daga bakinshi yana zuba awuyanshi. Wani irin bulluwo Ozo yayi da kwarangwal dinshi jikinsu na hayaki sosai ta bango, magana sukaji kaman daga sama maikama da murya irin ta abumai tsoratarwa. "Tursoso kanagani ana konamu kai shiru bakace komiba, Tursosooo!" yakira sunan Abie cikin wani irin fushi tone, tundaga silin gashin Abie nakai har zuwa karkashin tafin kafarshi rawa yake jin muryan Ozo, cikin wani irin yanayi na daburcewa da rashin sanin mai yake fadi yace "O...Ozo the g..great bansan cewa anan nabar zobena ba hala danazo inajan Aadil ne yana fada dani shine zoben yafita daga hannuna, Ozo dan Allah karafumin asiri kayakuri" Abie yakarashe maganan cikin tone din kuka, waya Baffa yaciro tsabagen son ya gasgasata me kunnuwanshi suka gama jiyemai ya kunna flash kaman dukansu sun hada bakine gabaki dayansu harda Aabid wayoyinsu atare suka ciro suka kunna flash light dakin yay haske bauu duk suna kallon Abie da idanunshi yay kuri alamun mara gaskiya sunyi jajir kirjinshi nawani irin bugawa gabaki daya yay wani iri yana kallon Ozo da kwarangwal dinshi dake jikin bangon dakin jikinsu na hayaki while malaman na karatun su har lokacin batare dasun yankeba, wani irin kara Ozo yayi ya buga karfen hanunshi sabida konewan dayakeyi yace "bazaka hanasu konamu ba Tursoso" da sauri Abie kaman mahaukaci ya tsugunna yanajan gwuiwa ya zagayo tagaban malaman yace "kuwa Allah, kuwa Allah nace baniba kudena karatun nan zan fadi muku komi, kunga ran Ozo the great yariga yabaci, inhar kuka konashi kashe Aadil zaiyi, wlh, wlh, billahillazi la'ilaha illahuwa kuruwan Aadil na tareda shi, kai rayuwan Aadil gabaki dayanta ma yana wurinshi, shine ya shanye rayuwan Aadil ya shafemai kwakwalwa, shine ya zamad da Aadil abinan dakuke gani, inhar baku denaba mutuwa zaiyi, zuge jinin Aadil zaiyi tass" babu wanda bai girgiza ba dajin kalaman Abie ba, shiko Abie ko kadan bai damuda wanan ba yasan dukansu babu abinda suka isa sumai, yanada kudin da zai iya kullesu dukansu, yanada kudin dazai iya batar dasu aduniyan nan gabaki daya anemesu arasa, sanan yanada kudin da zaije daganan harbangon duniya inyanaso yaje just to free his self daga shame and talk of the town. Wani jarababben tsawa Ozo yadakamai karfen hanunshi yay haske yace "bazaka hanasu ba Tursoso" da sauri Abie yasa hannayenshi ya rufe bakin limam kaman zaiyi kuka yace "kudena konamin Ozo, Ozo ne rayuwata, shine gatana, yabani abinda wanan mutumin marikina bai baniba dudda uwarshi tacemai yasoni sama
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128