Chapter 50
Chapter 50
yafita daga gidan, ba'a wani jimaba wani yaro ya shigo shiru tayi tabuga tagumi batason tasa ranta awanan karan. "Salama Alaykum wai ance ana sallama da masu gidan" da sauri Kaka ta mike tana murmushi sosai ta kwalama Abba kira. "Sama'ila, Sama'ila kufito ku shigomin dasu" fitowa Abba da Abban Ra'is sukayi da sauri Kaka ta nuna musu gate tace "kuna bata musu lokaci tun dazufa sukazo, shashina zaku kawosu" tawuce shashinta sukuma su Abba sukai gate wondering who could bakin Kaka be, bakaramin mamaki sukayiba dasukaga mutanen jiyaba amma duk suka boye mamakin nasu suka gaisa sosai cikin mutunci sanan sukai musu iso. Baffa ne da yaranshi maza uku su sulaiman sai kuma limam dawani amininshi duk sunci manyan fararen kaya suja shigo, ta window Zainab da Hamida da Ihsan suke lekawa sukace su waye wayan nan ita Hamida bama ta ganesu ba wlh hakan yasa suka dinga lekensu har suka shige sasan Kaka. Zama akayi dayake falon Kaka da girma fes ya daukesu harda wani enough space dazai dau kusan mutane goma ma, gaisuwa akai ta mutunci suka gaishe da Kaka sosai ana raha ana dariya kaman ansan juna nan Anty Lami da Zainab suka gabatar da aban sha da kulolin abinci, ba laifi sunci abincin sosai suka sha lemu sanan aka tattara komi Baffa yabude taro da addu'a ya kalli su Abba yana wani irin murmushi mai nuna tsantsan farin ciki yace "bazan taba mantawa da karamcin ku da alkahirin ku aduniyan nanba, kun taimake ku kun share mana hawaye, ba kowani musulmi zai iya abinda kukayi ba saimai karfin imani da taqwa, kuma inamai tabbatar muku bazamu taba wulakantar muku da yarku ba da izinin Allah, xamu riketa amana sanan ina mai shaida muku da in sha Allah Hassan dinma yakusa samin lafiya yanzu haka zamu faramai na gargajiya ne dazaran yasami lafiya an sallameshi daga asibiti kuma munasa ran za'a dace in sha Allahu, yanda kuka taimake mu kuka sharemana hawaye ubangiji Allah ubangiji ya share muku hawaye kuma ranan gobe kiyama, shi aure dakuke gani yana tattare da dunbin rahma da ni'ima damu bazamu taba sanin mai Allah ke nufi da auren nan nasuba sai nan gaba domin kuwa komi dakaka yafaru aduniyan nan kaddara ce kuma da dalilin faruwanta, fatan mu shine ubangiji Allah ya basu zaman lapiya Allah yakuna albarkaci abinda muke kokarin hadawa ayanzu" atare duk akace Ameen dudda dai Abba bai gama gane kan zancen ba he's a lil bit confuse, gyara zama Kaka tayi tana murmushi tace "yauwa to Alhamdulillah komi daka gani kaddara ne, mun hadu ta alkhairi insha Allahu mun daura kenan yanzu sai afara gabatar da kayayyakin dana fada muku jiyako, kudin kun gani kunaso, kudin gaisuwan iyaye, kayan sarana dakuma kudin sadaki" wani irin kallonta Abba yayi zuciyarshi na neman bugawa, dauke kai tayi kaman bata ganshiba Abban Ra'is kuma yadanyi tapping cinyar Abban ahankali alamun karyay wani abu dazaisa suji kunya hakan yasa yay relaxing wearing a smile, murmushi Baffa yayi yace "to Hajiya" ya kalli su Suleman da Muhammad yace "Bismillah" tashi sukayi suka fita daga dakin basu jimaba suka fara shigowa da kaya niki niki tareda wasu yara yan anguwan akwati set biyu suka kawo guda shida shida na Louis Vuitton, sai manya manyan tabarma guda biyar, dasu goro jaka goma, su dabino sai wasu kwalayen hadaddun sweet da chocolate katon goma, sai su kwalin biscuit saikuma kudi yan dubu wrappers na dubu daidai da bama tasan na nawa bane sai harba ido take shiko Abba da Abban Ra'is shiru sukayi suna kallon ikon Allah, aminin Baffa ne yasake bude taron akaro nabiyu da addu'a yace "ga kayan nagani ina so dinan, gakuma kayan sa ranan, munaso ayanke mana sadaki sanan asaka ranan ko to Bismillah Alhaji" yay maganan yana kallon Abba da miyan bakinshi gabaki daya ya kafe ya bushe, hadiye miyau yayi ahankali ya kalli Kaka data zuba mai idanu irin kallon nan na kace bazaka karamin jayayyaba, dan gyara zama Abba yayi Anatse yana kallon kayan yace "wanan kaya haka Alhaji kaman muna sayar da yarinya agaskiya sunyi yawa, banda haka wanan akwatin ai babu bukatar su awajen sa rana ko? Kawai abarmata su amatasayin akwati kar akawo wan..." "kaga yaron nan nawa bai iya komiba haryau" Kaka tafada tana dariya ganin Abba na neman mata bukulu tace "ko yayyin Hamida gabaki dayansu nina aurar dasu saisa baisan kan abubuwan al'adun mu na hausawa ba, yanzu dai maganan sadaki muke ko?" tai maganan tana hararan Abba ta kasan ido ahankali ya saukar dakai, tace "yauwa sadaki" tace "yauwa sadaki kubada dubu dari, kudin kun gani kuna so dubu dari, sanan kudin gaisuwan iyaye dubu dari" innalillahi wa innailaihi raji'un Abba kawai yake fadi aranshi wace irin uwa gareshi dakeda shegen son kudi haka sabida taga masu kudi ne takeson siyar da yarshi haka dan anasu Ayush duk batai abinnan ba, patting cinyarshi Abban Ra'is yayi hakan yasa yasake murmushi, abokin Baffa yace "to Masha Allah" ya dauko wrap na yan dubu daidai guda uku duba dari uku kenan yamikama Abba cikeda ladabi, asanyaye Abba yamika hannu ya karba yana murmushi Kaka ta saki buda. "ayiriririi" Abba ya kalleta ganin yanda take murna yasa ya kalli Baffa yace "nabaku ubangiji Allah ya kaimu ranan yaja mana rai" Ameen duk akace Kaka tace "sati hudu, nan da sati hudu biki, asabar din dazata fado ana sati hudu ne biki da izinin Allah" takara sakin musu guda dayasa su Baffa dariya sosai nan aka kachame ana hira Abba yadan saki jiki yana basu amsa wuraren karfe daya suka tattara suka tafi bayan sunma Kaka kyautan ragowan kudin wai tarabama jikoki aiko Kaka harda rawa tarakasu har gate saida taga tafiyar su sanan suka shigo gida ta daure fuska rass dan karma Abba yakawo mata wata maganar ta kwalama Mama da Anty Lami kira tace "kuzo mu bude akwati muga abin ciki". Tai sasan ta Abba yabita da kallo zaiyi magana Abban Ra'is yace "kayakuri iyayen mune, babu yanda zamuyi dasu sai hakuri kawai, ko zaka mata ba yanzu ba, kabari anjima koda da daddare ne saika mata magana kaji" gyadamishi kai kawai yayi Abban Ra'is yace "muje gidan kaji kawai" fita kawai sukayi waje suka shiga mota suka tafi.. Zama Kaka tayi akan kujera tana kallon kayan daidai nan Mama da Anty Lami suka shigo, da mamaki suke kallon kayan Anty Lami tace "kayan waye wayan nan haka Kaka?" cikin tsananin murna Kaka tace "dukna Hamida ne wlh, mai sunana nada kashin arziki wlh, mutanen jiya nakirawo suka dawo dan sunban tausayi nabasu auren Hamidan ansa rana sati hudu, wanan akwatunan fa duk na sa rana ne, akwai na asalin aure na nan zuwa gab da biki" shiru daga Mama har Anty Lami sukayi dan maganan ta mugun basu mamaki bama tasan tayaya zasu amshi maganan ba. "dalla kuzo kuyatayani bude akwatin" ahankali suka shiga Mama ta kakalo murmushi Anty Lami tafara bude akwatunan suna dubawa kayane hadaddu bana wasaba, Kaka tabasu su sweet da dabino da goron tace "gashi nan a kulla a aikawa makota sati hudu, akwatin anan shashina za'a barsu ni yanzu fita zanyi akwai abinda zanje nayi" tai maganan tana Jan babban gyalenta dake kan kofa Lami tace
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128