Skip to content

Chapter 47

Chapter 47

In Bani Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

mana badan muba bakuma dan halinmu ba kubamu auren Hamida" yakarashe maganan ahankali akuma sanyaye cikin wani irin mugun sanyin gwuiwa ya fawwalama Allah komi dan yasan abu mai wuyane su yarda, gyara zama Abba yayi yadanyi gyaran murya ya kalli Baffan dayaji yana wani irin jin mugun nauyinshi zaiyi magana Kaka ta dagamai hannu. "kamin shiru anan Sama'ila" sanan ta juyo ta fuskanci Baffa tana kallonshi tana warware kullin zanin jikinta tana ciro namijin goro, ta balli goron takai bakinta tana taunawa sanan tace "magana zan maka ta gaskiya" wani irin sanyi Abie yaji a aranshi yazaro ido yana kallon Kaka, dafa kirjinta tayi ta bubbuga harsau biyu tace "kaganni nan bazan taba daukan jikana nabama mahaukaci ba ana zaune lapiya? Hamidan tawa ce zan dauka nabama tababbe haba adinga adalci Alhaji to tama yaya abin zai yuwu..." da sauri Abba yaja gefen zaninta ganin rashin mutunci datake shuka musu wanda bai daceba da girman su da kuma darajan su, nakama hanunshi duka tayi batare data kalleshi ba tace "barni nafadi musu gaskiya Sama'ila kadena hanani" tasake kallon Baffa tace "ku masu kudin nan kunada son kanku dayawa na rantse da girman Allah, yanzu fa da ace mune mukeda tababben yaro mukazo neman auren lafiyayyar yarku, da wlh, billahillazi, da bazaku badaba koda dan namu mutuwa kuwa zaiyi, amma dayake mune zakuzo nema, to bari ma na tambaye ka idan muka dauki Hamida muka bama mara lafiyan dan naku wani irin zama zasuyi iye? Shikenan saidai ta dinga ganin sa'ointa da yara ita banda ita haba mana anya baku so kanku da yawaba kuwa Alhaji, gaskiya ku tattara yinaku yinaku kubar mana gidan mu bazamu baku yarmu ba, bazan bada jikata ga mara lafiya na, shidai mara lafiyan ubangiji Allah ya bashi lapiya yakuma tada kafadar shi, sai anjiman ku" tunda Abba yake Kaka bata taba bashi kunya irin nayau ba hatta Abban Ra'is sunnar dakanshi yay kasa dan Kaka tagama dasu bahaka ake magana ba ko kadan, murmushi sosai Baffa yayi irinta manya dan ko kadan baiji zafin maganganun Kaka ba dan gaskiya tafada, dama yasan saman ma Aadil aure abune mai wuyan gaske, gaskiya babu mahaifin dazaiso yadau yarshi yabama mara lafiya bakowa ne zai iyaba, murmushi yasakeyi yace "shikenan angode sosai mun gode da lokacin dakuka bamu" yataso zaizo ta wajen su Abba da kansu ke kasa yabasu hannu da sauri Abba da Abban Ra'is suka tashi suka mika musu hannu, Abba yama kasa magana sabida yanda Kaka ke binsu da kallo yasan gwara yay shiru inba hakaba bakaramin aikin Kaka ba tasake yanko wata maganan yanzun nan ba, ahankali Baffa yana rike da hanunshi yana kallonshi ganin yanda duk kunya tarufe shi yaki yarda su hada ido yace "bakomi karka damu, arziki ta hadamu kuma in sha Allahu amfara kenan" murmushi Abba yayi yana kara kai kanshi kasa, Baffa yace "to Amana sallama da matan, su samemu awaje mun barku lafiya" to Abba yace Baban Ra'is yarakasu shikuma Abba yay corridor ya kwalama Zainab kira tafito yace "jeki fadama su mamanki su fito zasu tafi" da sauri ta juya bayan ta amsa da to ta tafi shikuma yawuce yafita batare daya kalli Kaka daketa rakashi da ido ba, fitowa su Mami sukayi suka gaishe ta Kaka tace "Allahu akbar, kidena kuka haka baiwar Allah addu'a zakimai Allah yana amsan addu'an bakin uwa, wuce kutafi suna jiranku awaje" waje duk suka fita bayan sunyi sallama suka shiga mota suka tafi Abba da Abban Ra'is kuma suka dawo cikin gidan. Zama duk sukai a palon Abba ya kalli Kaka yace "gaskiya Umma abinda kikayi bai daceba, kince bazaki basu ba bai isaba saikinci musu fuska, babu kyau fa aibasu suka dauramai ciwon ba ko naga, haba mana Umma" kallonshi Kaka tayi saikuma tafashe da kuka sosai tasa bakin zaninta tana share ido tace "nika zaga Sama'ila, nikake ciwa mutunci akan nafadi gaskiya?" sakin baki Abba yayi yana kallonta cikin mugun takaici, Anty Lami dai murmushi tayi Mama kuma girgixa kai kawai tayi kanta akasa, da sauri Abban Ra'is yace "a'a Kaka ba zaginki yayi ba tayaya ma zai zageki eh Kaka, cewa yayi dakince musu kawai bazaki basu ba basai kin ci musu fuska ba anan ne baki kyauta ba" rushewa tayi dawani irin masifaffen kuka tace "nikuka tasa agaba harku biyu kunmin taron dangi kuna cimini mutunci, d'ana wanda na haifa ya zageni kaikuma kana gayamin baka akan nafadi gaskiya" da sauri Baban Ra'is zaiyi magana Abba ya girgiza mai kai alamun karyayi yabarta kawai, fashewa tayi da kuka sosai tace "sabida banso Hamida ta cutu nafadi gaskiya shine kukamin taron dangi? Yo inda sune mukaje nemama tababben mahaukaci danmu yarsu bamu zasuyi? Ba gaskiya nafada ba amma shine kuka mini rashin mutunci haka, innalillahi wa innailaihi raji'un, Sama'ila ni ka nuna ma iyakata, to wlh wlh yau zan mugun baku mamaki" mikewa tayi tsaye tai hanyar fita daga dakin da sauri Abba yatashi yabita yace "ina zaki Umma" juyowa tayi cikin fushi sosai tana zare ido ta nunashi da hannu tace "ba ruwanka, tunda haushina kakeji akan gujema Hamida tsiya danayi ai shikenan badai kai kaga masu kudi ba kana kwadayi ko yakara budema wasu manya manyan gidajen kaji ba, zan baka mamaki, kuma wlh ka biyoni Allah ya isa" tai hanyar gate da sauri, su Mama da Abban Ra'is suka fito, Abban Ra'is ya kalli Abba yace "ina zata?" ahankali Abba kamam zaiyi kuka yace "bansaniba wlh tace inna bita Allah ya isa" duk suka tsaya suna kallonta yanda take tafiya da sauri da sauri kaman ana ingizata tana kuka sosai, daidai zata bude gate Faruk dake sanye cikin uniform na sojoji ya bude gate din ya shigo, fashewa tayi da kuka sosai tana ganinshi tace "Faruk kaga ni ubanku Sama'ila yacima mutunci ai bainar jama'a ko, zoka kaini gidan Alhaji Gambo Sawaba ai kowa na kano ya sanshi" kafin ma yay wani magana ta fizge hanunshi cikin kuka tafita sukai inda yake parking mota akofar gidan tace "budemin" budemata motar yayi ahankali ganin yanda take kuka kaman wacce aka Zane ta shiga baya tace "ni tsoron gaba nake yan gaba ke mutuwa a hatsari bana bayaba wlh" murmushi yayi yatada motar yaja yace "ina zankai ki haka bako mayafi" hararan shi tayi tana share hawaye tace "uwarka bata siyamin mayafin ba saisa ban yafaba, kuma dan ubanka Sama'ila ai nacema gidan Alhaji Gambo Sawaba zaka kaini ko" yatsine fuska yayi tareda tabe baki yace "mekuma yahada ki da gidan babufa wanda kika sani awanan family tsohuwa" shewa tayi tace "da kenan kasani yaro, kajani da sauri nidai" tabe baki yayi bai kara cemata komiba ganin yau haukan nata takejin yima mutane haka har new GRA agaban gidan securities suka tsaida su, tabe baki yayi ya waigo ya kalleta yanda take zazzare ido tana kallon durmemen gate din gidan yace "aisai kimusu bayanin wanda kike nema" da sauri tana zare ido tace "har munkai gidanne kai wanan gida ai yay na ubanku sau hamsin, kaito saukar min da glass din kasa namusu magana" saukar da glass din Faruk yayi Kaka ta leko kai ta kalli security dayake jira suyi ya saukar mata yaga su waye tace "kai wajen mai gidan Alhaji gambon nazo, yasan

Table of Contents

Chapters

128 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128