Skip to content

Chapter 55

Chapter 55

In Bani Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

directing dinshi yake abinda yakeyi, da duka karfinta tasa hannu ta ture kirjinshi ganin kaman zai cire mata baki hakan yasa yasake a tsorace, cikin fushi ta waska mai mari da karfi tana hararanshi sabida bakin cikin abinda yamata da sauri yadafa wajen yana kallonta, goge bakinta tayi tanaji kaman tai ihu hawaye na zuba daga idanunta kafin ta kalleshi shima ita yake kallo hanunshi dafe da kucinshi, harara tasake ballamai tama rasa mezatace mai tajuya da sauri zata fita daga dakin dan ko ina na jikinta rawa yakeyi, wani irin fashewa yayi da kuka yana girgiza mata kai cikin kuka sosai yace "don't go please" tsayawa tayi chak tajuyo ta kalleshi batare datama san meya hanata tafiyan ba, sakin mata wani irin kuka sosai yayi daya wani irin narkan da zuciyanta yana girgiza mata kai cikin kukan yace "please don't leave me again" karasawa ciki tayi asanyaye batare data sake kallon fuskarshi ba taja plastic chair ta zauna tareda daukan furan ta rufe ta ijiyemai akan saman drawer sai kallonta yake soyake ya shige jikinta kozaiji dadi but he's scared bayaso tamai fada kota sake marinshi, baiso yaga tana fushi, dan kallonshi tayi ganin yanda yay wani irin zuru zuru sai goge kwalla yake yasa tadan sakin mai murmushi da sauri ya sakin mata murmushi yana clapping hands da sauri hawaye na zuba daga idanunshi yace "Hamida my wife is smiling" murmushi tasake mai tai shiru tana kallonshi dan wani irin mugun tausayi yake bata zataso taji yanda yafara ciwon nan, zataso taji labarinshi, zataso taji ya akayi shi baida lafiya and dan uwanshi is fine, hakanan takeji zata iya komi dan kawai taga yadawo kaman kowani babban namiji, sosai takejin Aadil aranta kuma tarasa mesa hakan, bude kofan da akayi yasa duk suka dago kai, Baffa ne ya shigo tareda Kaka sai Mami da Abie da Aabid dake tareda Mami dan sun shirya yanzu duk yay wani iri, ahankali ta saukar da kanta kasa tana wasa da yatsun ta, Kaka ta kalli Aadil din dake kallon Mami yana mata alamu datazo tace "sannu da jiki, Allah sarki ya rame sosai, idanunshi sun kode alamun ciwo, ya jikin?" kallonta yayi saikuma yaturo mata baki tareda mata fari da ido yace "fine" sanan ya kalli Mami batare daya kalli Aabid daketa kallonshi ba cikin tsananin farin ciki yamata alamu datazo yana mata pointing Hamida yace "Mami come and see My Hamida, tazo" ya kalli Baffa daketa murmushi yana kallonshi ganin yanda yay kaman bashiba yace "come and see her grandfather" Mami ce takaraso kusa dashi yawani irin fada jikin Mami cikin tsananin murna yana nuna mata Hamidan da hannu yana wani irin cute smile dake karamai wani irin mugun kyau, murmushi Mami tayi tace "naganta amma yanzu Hamida zata tafi itada grandma dinta she will come tomorrow okay kaga yamma tayi" kallon Mami yayi da sauri kafin ya make mata kafada yace "no i don't want her to leave me again" ahankali Mami tace "please Aadil zata dawo kaga magrib tayi ko" make mata kafada yayi kafin yasaki kuka ahankali, Mami ta kalli Hamidan data kasa dago kanta tace "tashi kutafi daughter kinji" sakin Mami yayi yarikema Hamidan hannu da gudu yana kuka yana bubbuga kafa da sauri Kaka ta share hawayen dake neman zubo mata ta girgiza kai, kai wanan yaro na bata tausayi bana wasaba wlh, hakan yasa ta matso kusada Mami tace "kinga maman yan biyu barshi kinga sai kuka yake kar zazzabin yarufe shi kuma, anjima inyay bacci matafi" da sauri Baffa yace "a'a baza ai hakaba, magrib tayi Hajiya in aka biye tashi ba yanzu zaiyi baccin nan ba" yay maganan yana dogara sanda yana kallon fuskan Aadil din daya rirrike hanun Hamida yana kuka sosai yana bubbuga kafa, wani irin jin kukan nashi Hamida take har akasan ranta amma takasa dago kai balle ta lallashe shi sabida kunyan su Mami gashi saijan hanun nata yake yana kuka, ahankali Baffa ya dafa kafadarshi yace "zokaji" magana yamai a kunne da sauri ya kalli Baffan cikin kuka sosai yace "are you sure?" gyadamai kai Baffa yayi cikin lallashi yana sharemai hawayen, ture hanunshi yayi ya tsugunna agaban Hamidan ya daura hannayenshi akan cinyarta ya leka fuskarta hawaye nafito daga idanunshi jiyake kaman zaiyi hauka, hada ido sukayi da Hamidan, ahankali cikin kuka yace "is it true zamuyi video call?" gyadamai kai tayi dudda bamata da waya, girgiza mata kai yayi yace "please don't go and leave me zan mutu" yanda yay maganan yana kuka saida yataba zuciyar kowa adakin da sauri Abie yafita daga dakin ya shiga restroom dayake hanyar dakin, ya shiga wani bayi da sauri yarufo kofa yaciro handkerchief daga aljihun shi ya daura akan idanunshi yahau kuka, kuka sosai bana wasaba. "wani irin kwadayin duniya yakaini na jefa d'ana wanan halin dayake ciki yau? Banrasa ci ba, ban rasa shaba, ban rasa sutura ba, inada su Suleman dasuka daukeni a matsayin dan uwan su, inada mahaifin su daya daukeni a matsayin danshi, ina da aiki na, ana biyana daidai na level din karatuna a kamfanin Baffa what push me? Wani irin greed yakaini nafada wanan halakan? Aadil na cuceka, na cuce ka bana wasaba, nacuce ka my son, i can't forgive myself, i can't forgive my self, my son has been suffering yanzu for more than 30yrs all because of me ya zanyi? Tayaya zan bulloma wanan tsaka mai wuyan danake? Tayaya zan hana Aadil auren nan? Tayaya zan ciremai son yarinyar nan? Tayaya zan rabashi da yarinyar nan" yabata kusan rabin awa abayin yana kuka sanan ya wanke fuskarshi ya share tass sanan yafito. Fitowa yayi daga bayin daidai lokacin Mami tafito daga dakin hada ido sukayi da sauri ya saukar da idanunshi kasa dan bayason tagane yay kuka, hakanan kawai yaji yana wani irin jin nauyin ta dan ya mugun yaudaranta, ya cuceta itada yayan su, hanunshi dayaji an kama yasa yadago kai suka hada ido da ita, tattausan murmushi ta sakin mai tasa hannu ta shafa sajenshi cikin muryan kwantar da hankalin miji down tace "kadena damuwa Abie, Aadil dinmu zai warke da izinin Allah, watarana duk wanan abin labari zai zama kaji" gyadamata kai yayi asanyaye hakan yasa tai murmushi tace "zomuje office din Dr, kaina fito na nema dama Aadil yay bacci, Dr yace muganshi, ni inaso a sallameshi ma gobe kawai dasafe mukoma gida mai maganin da Baffa yakiramai yazo afara gwada maganin gargajiyan kafin bikin nashi ko, let's see what Allah has install for us and banda hakama aure rahama ne let's just team up and be praying for our children ko Abie" gyadamata kai yayi yama kasa mata magana sabida yanda jikinshi yay mugun sanyi, yasha attempting yafadi mata gaskiya but bayataba iyawa he loves Mami so much da he's afraid of losing her, bayaso yafadi mata gaskiyan wayeshi ta tsaneshi taki zama dashi, his heart cannot bear that, ahaka suka bude office din Dr suka shiga shiga sai tunane tunane yake. ** Gari yafara dan duhuma dan gab da isha'i suka isa gida, Mama kadaice a tsakar gidan tana nannade tabarma zata shiga daki, da sauri Hamida tai wurinta tafada jikinta tana murmushi tace "Mama mun dawo" dan murmushi Mama tayi dan sosai take

Table of Contents

Chapters

128 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128