Skip to content

Chapter 35

Chapter 35

In Bani Book One Complete Hausa Novels 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

kanta daga bayanshi, mutanen data gani yasa da sauri ta komar da kanta bayanshi ta labe. Sake zaro ido Aadil yayi sosai ya kalli Aabid dayay shiru yana kallonshi kaman yanda kowa na dakin ke kallonshi yanda yay mugun butu butu, wandon jikinshi kaman an kwaba kasa akai, kafarnan da babu ko takalmi ajiki tai busu busu, shimin jikinshi ma tai datti idanunshi sunyi suntum sunyi wani iri alamun yaci kuka, fashewa dawani irin Kuka Mami tayi ta shigo dakin da sauri tayo kanshi tace "Aadil, my baby" budema Mami hannu yayi yana wani irin jumping yana murna kaman dan yaro. "oyoyo Mami, oyoyo Mami, oyoyo Mami na" tana karasowa gabanshi yawani irin fadajikinta ya kankameta yana tsalle da kafa hakan ya bayyanar da Hamida dake labe abayanshi ta sunnar dakai kasa tama rasa ma me zatayi har wani soshe soshe take, kallon ta Mami da duka kowa na dakin suke yi barin ma Aabid dayaji gabaki daya numfashin shi ya tsaya chak, Cikin wata irin murya yace "Amatullah" da sauri ta dago kanta ta kalli direction din da aka kira sunanta daidai lokacin Aadil yasaki Mami shima yajuyo cike da murna yace "Mami look at Hamida, my wife" kallon Aabid Hamida tayi saikuma ta kalli Aadil dayay magana yanzun nan wani irin faduwa gabanta yayi bana wasa ba dan bambamcin da ayanzu tagani ajikinsu shine daya tsaf tsaf yake yaci shadda gizna kanshi sanye da hula tangaran, shaddar jikinshi har wani irin kyalli yake yana walkiya sai dayan kuma wanda yake daka daka yana sanye da singlet da dogon wando amma kamaninsu daya tsaf, kasa kallon sauran manyan mazan dakin tayi da tsohon dake sanye da glsass yana rike dayar Sanda tasake sunnar dakai tahade hannayenta dake wani irin bari tana murzawa da sauri da sauri tana numfashi sama sama. Sakin Mami Aadil yayi yaje dawani irin gudu yafada jikin Aabid batare daya lura da yanayin dayake ciki ba yaja hanunshi yace "come, come and talk to My Hamida Bid" yaja hanunshi yakawo shi gaban Hamida da kanta ke kasa har lokacin tana murza hannuwanta yace "Bid see my Hamida" yasaki Bid yajuya da sauri ya kalli Mami daketa binshi da kallo kaman zata hadiyeshi da so yace "Mami see Hamida my wife" da gudu yay wurin Baffa yafada jikinshi wani irin murmushi tsohon yayi ya shafa kanshi yace "Hassan" da sauri ya dago kanshi yana turamai baki a shagwabe yace "Am Aadil grandfather not Hassan" sake bubbude manyan idanunshi yayi yakama hanun Baffan yace "zokaga My Hamida Baffa" da sauri yakawo grandfather wajen, sanan yakoma yana wani irin tsalle yana kallon Abie da idanunshi sukai jajir yanamai wani irin murmushi kaman ya cinyeshi da so yace "Abie come and see my Hamidaaa" yaja hanun Abie yakaishi wurin kafin yakoma ya kwaso duka Uncles dinshi yakaisu gaban Hamida sanan ya tsaya shima kusa da Aabid yana kallon Hamidan da duk suka tsaya suna kallonta babu wanda yay magana cikinsu yana murmushi yace "Bid u see my Hamida, she's my Hamida" wani irin murza hanunwanta Hamida take jikinta nawani rawa, murmushi Mami tayi tace "baiwar Allah a ina kikaga Aadil?" ahankali tadago kanta ta kallesu, wani irin jiri tafara gani yanda duk suke kallonta bakinta har rawa yake tana nishi sama sama tace "i...ina...na...w...wun..." batakarasa gaisuwan ba tai wani irin baya a sume dan kwalin ta data lulluba dashi tai daurin ta wuya ya xame yay kasa arude Aabid ya mika hannu zai tarota yace "Amatullah! " arude Aadil yamika hanunshi zai tarota shima yace "my Hamida" da sauri Aabid yatarota Aadil ya tsugunna ya dafa kafadar Aabid yana kallonta yasaki kuka yana kallon fuskarta yace "wat happen to her Bid?" dagokai Aabid yayi yace "mutafi da ita gida Mami" da sauri Abie yace "munsan tane da zamu kwasheta mutafi da ita gida?" makemai kafada Aadil yayi yana goge kwallan dayake hakan yasa Baffa yace "muje akira likita yadubata koba komi ga Aadil nan yasaba da ita, daga gani ita ta taimake shi, kumuje, yaka Aadil" zuwa wurinshi Aadil yayi yana waigen Hamida da Aabid yadaga, Baffa yarike mai hannu duk suka dunguma suka fita daga wajen, saida suka salami su inspecta sanan suka shiga mota sai gida. Wani hadadden daki Aabid ya shimfidar da ita kan makeken gadon dake dakin yana kallon fuskarta, tsugunnawa Aadil yayi gefen gadon yana kallonta shima idanunshi yay jajir, ahankali Aabid yajuyo da kanshi yana kallon yanda Aadil ke kallonta yana leka fuskarta, runtse idanunshi yayi da karfi yanajin ciwo aranshi sosai, daidai lokacin Mami ta shigo dakin karasawa tayi gaban gadon ta zauna ata saitin kafafun Hamidan tana kallon fuskarta tace "ga Dr nan zuwa ya dubata Baba yakira shi, Aabid stay with her karta tashi bakowa" ta kalli Aadil dake wani irin kallonta tamikamai hannu tana murmushi tace "come Aadil, muje kai wanka and change this cloth, kaima Dr zai dubaka inyazo duba friend dinka" make mata kafada yayi yana hararanta a shagwabe yace "she's my wife" shiru Mami tayi tana kallonshi saikuma tai murmushi tace "naji, muje kayi wankan to kafin kafito nahada maka abinci" tashi yayi ahankali kanshi narawa yana kallon Hamidan tashi itama Mami tayi taja bargo ta lullubeta dashi tarike hanun Aadil suka fice suka rufo kofan, wani irin runtse ido Aabid yayi yafuzar da iska kafin yadaura hanunshi kan zuciyarshi yana dukan zuciyarshi yay hakan kusan na 2min sanan yadawo daidai, zama yayi agefen gadon yay shiru yana wani irin kallon fuskarta, dawani irin murya mai rauni sosai yace "tayaya kika hadu da brother na Jewel? I'm the one for you Amatullah" yay shiru yana kallon fuskarta, knocking da akayi yasa yatashi yay wurin kofan bude kofan yayi Dr ne da Baffa suka shigo dakin, Baffa yace "yauwa gatachan likita adubata" karasawa Dr yayi bakin gado yaduba ta sanan yaciro drip daga katon jakan hanunshi yamata fixing yay allura aciki wurin 15 minutes yabata akanta sanan yajuyo ya kalli Baffa yace "fever ne kawai, i guess tsoron kune yasta ta suma, yanzu dai komi lpy dazaran drip dinan ya kare aciremata and yanzu dai bacci take zuwa anjima chan haka zata farka" murmushi Baffa yayi yace "masha Allah itace taga jikana ta taimaka mai, muje kadubamin jika" wucewa sukayi suka fita daga dakin Aabid yadawo ya zauna. Duba Aadil Dr yayi yarubuta magungunan daza asayomai sanan yamai allura da kyar ya yarda akamai, yaci abinci nan wani baccin gajiya da wahala yay gaba dashi shima. Saida yay bacci sanan Mami tarufa mai bargo takashe wutan dakin nasu tarage karfin Ac tafito, dakin da Hamida take tawuce ahankali tabude kofan har lokacin Aabid na zaune agefen gadon yazuba mata ido, budewan kofan dayaji yasa yadago kai, murmushi Mami ta sakinmai takaraso ta zauna kusada shi, ahankali yadaura kanshi kan kafadarta ya sauke ajiyar zuciya, shafa kanshi Mami tayi tace "menene Son?" dan murmushin yake ya kakalo mata yace "babu komi Mami na" dagashi tai daga kafadarta ta kalli fuskarshi jin yanda yay maganan danta tabbatar da abinda ke damun shi, lumshe ido yayi da sauri dan yasan tsaf Mami zata gano da damuwa a idanunshi, ahankali kira sunanshi. "Aabid" bude idanunshi yayi ya kalleta, nunamai Hamida tayi da ido tace "you called her Amatullah dazu kasanta ne daman?"

Table of Contents

Chapters

128 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128