Skip to content

Chapter 56

Chapter 56

In Bani Book One Complete Hausa Novels 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

fushi ta kalli Kaka data karaso wajen tace "sannu da zuwa Umma, ina yini" "yauwa Haleematu, lpy lau ina sauran yaran?" Kaka tafada tana daure fuska ta kalli Hamidan tace "ke wuce mutafi akwai gyaran dare dazan miki" tai maganan tanajan hanunta tai gaba da ita Hamida tajuyo da sauri tana kallon fuskar Mama data shige daki abinta, Kaka tawuce sasan ta da ita, akwatin falon ta nuna mata tace "ga akwatunan kayan sa ranan ki nan keda Aadil sati hudu baban ki yasaka, shi suka kawo dazu da safe shine ubanki yace na dauke ki nakaiki ki gaida yaron, ashe haka yaron ke sonki yarnan? Jibi yanda yadinga babbaka kuka dazaki tafi, Allah dai yakaimu bikin mu auramai ke yahuta da wahala wlh yaron na masifan bani tausayi" da sauri Hamidan ta kalleta dan bakaramin faduwa gabanta yayi da maganan ba ahankali bakinta har rawa yake tace "ni Kaka? Nace muku ina sonshi ne? Ninace zanyi aurene? Ba Anty Zainab za'a aurar ba kafin niba" mugun harara Kaka ta watsa mata tace "kisami ubanki kimai maganan ja'ira rasakunyan beran tanka, ai bani nabada auran nakiba, wuce kije kiyo alwala kiyi salla akwai abinda zan hadamiki kici, kuma wlh aure bafashi saisa daga yanzu andena ganin murmushi na balle wani shege ko shegiya takawomin maganan banza a gidan nan, bazan bude ido inaji ina gani kumin bukulun gidan hutuba, arziki inaji ina gani kumin bakin cikin samuba" taja tsaki tawuce tabude dakinta ta shige tana ihu tace "kuma wlh nabaki minti goma kiyi salla kizo nan wurin, gobe yar buzu zata zo tafara miki gyaran jiki" da gudu Hamida ta shige dakinta tafada kan gado wani irin kuka neyazo mata sai maimaita kalman aure take abakinta tama kasa yarda wai ita za'ama auren, to wani irin aure ma, Aadil, ita ta shirya aure ne yanzu? Tayaya zata auri Aadil ma? Haka taci kukanta takoshi saida Kaka ta kwala mata kira sanan ta tashi ta shiga bayi ta daura alwala tafito tahau kan dadduma tai salla sanan tawuce dakin Kakan tana goge kwalla. Misalin 10 nadare Abba ya shigo gidan, abinci Mama takaimai, sai bayan yagama ci yay wanka sunyi shirin bacci sanan Mama ta gyara zama ta fuskance shi fuskanta adaure, ahankali tace "tundazu kadawo kai shiru ina kallonka nazuba ido inji kozakamin maganan amma kai shiru ko kala bakace min bako, ka dauki y'ata kabama mahaukaci baka fadanmin ba baka shawarceni ba saidai naji abakin wasu sabida kaganni shiru shiru kome kakeso shinakeyi ina binka sau da kafa saika nemi ka takemin hakkina a matsayina na mahaifiyar Hamida gas...." da sauri Abba yatareta ta hahanyar cewa "Hamida ba yarki bace kadai ba nima y'ata ce, sanan yanda abin nan kemiki ciwo haka nima yakemin ciwo, yakike so nayi eh Haleematu? Umma ita taje tahado komi kawai nima ganin mutane nayi yau da kayan saka rana sun taho, so kike na nabada Umma agaban su? So kike amana kallon kananun mutane da basusan mesuke yiba? Yayama zanyi eh" da sauri Mama tace "gaskiya bazan yardaba, nibazan bari Hamida na ta auri mahaukaci ba nafadama bazan bari ba kacema Kaka anfasa, nibazan bama y'ata mara lafiya ba" shima Abba cikin tsananin bacin rai kyace "sokike ta tsinemini? Ke bakiga Umman bane? Yaya zanyi da ita mahaifiyata ce dole kome tace namata biyayya, yaya zanyi Haleematu fadamin" fashewa da kuka sosai Mama tayi takasa cewa komi hakan yasa ya dafe kanshi yay shiru yasan Mama da mugun hakuri kuma yasan da gaskiyan ta amma yaya zaiyi? Shi kanshi abin yafi karfinshi, ahankali ya janye hanunshi daga kan goshinshi ya matsa kusa da Mama ya rungumota jikinshi yana shafa bayanta yana jijjigata harta rage kukan ahankali yace "kiyakuri Haleematu, i need your support more than anything ayanzu, kece karfi na, idan kika karaya haka ninai yaya eh? Nasan Umma bata kyautaba amma kiyakuri, bamu miki adalci ba amma kiyakuri uwata ce dole nabi abinda tace, addu'a zamubi yarmu dashi, babu wanda ya isa yahana kaddara faruwa, kuma rabo na kisa bamusan me Allah yagani yahada suba, kawai mubisu da addu'a kinsan Allah na karban addu'an uwa akan yaranta, mumata addu'a kinji muga me Allah zaiyi, am sorry for hurting you kinji best wife, stop crying" gyadamai kai Mama tayi ahankali hakan yasa ya sumbaci gaban goshinta yasake rungumeta da kyau yace "akwai wasu kudi danake expecting once anbiyani zan baki kije ki siyo mata duk abinda yadace kinji" gyadamai kai tayi nan yadinga bata kalamai masu ddi da sanyaya rai harta sauko sosai ta share ta barma Allah komi kawai ta tasa addu'a agaba. *** Kwanaki nataja sosai gidaje biyun aketa shirye shiryen biki, gabaki daya Aadil baida lafiya magungunan hausan da Baffa yasa akemai da in yasha ma amai yakeyi gashinan gashinan ne kawai mugun so yake yaga Hamida bana wasaba, gashi kullum yana dakin Mami inyaga Aabid wani irin tsoranshi yakeji yayta tuna yanda yamai mugun duka yay lamo koya kulle ido, Aabid gabaki daya yadawo wani iri shima saiyahau ciwon abun yama Mami yawa ga Aadil ga Aabid Abba yay wani irin ramewa shima haka dai suka dinga lallabawa Dr na zuwa treating nasu a gida, Aadil harda drip yasha kusan hudu. Kaka takawo yar buzuwa anata ma Hamida gyaran amare bana wasaba, gabaki daya Hamida duktai zuru zuru kullum saitaci kuka, ko kadan batason auren nan dudda kullum tunanin Aadil take bana wasaba takuma rasa mesa take tunanin shi, tasan yana chan yana nemanta yanzu yana kuka rabonta dashi tun yana asibiti. Kuka, kukane aikinta gashi tai wani irin kyau tai haske bana wasaba, fatarta dama yanada taushi saiya kara wani extra ordinary taushi, ga sheki ga kamshi datake yi, ana saura sati daya biki family Aadil suka kawo akwati nagani nafada guda 12, Kaka harda rawa tama manta da Faruk da rabonta dashi yafi sati, dasuka tashi tafiya aka hadamusu shatara na arziki, Hamida kin duba kayan tayi Zainab da Ihsan sai rawa suke sunata murna Hamida zatai aure, Mami dai kullum bayan magrib takan koya mata yan dabaru na zaman gidan miji, ko kadan tarasa sukuni bama ta iyacin abinci hakan yasa wani irin ciwo yakamata tafara zazzabi bana wasaba, har aka fara sha'anin biki yayyinta duka harda su Ayush duk sunzo sai mamakin aurenta suke yaushe Hamida tai miji, yaushe tai saurayi kawai sunji bikin ne, ranan walima saida Abba yakira wata likita sabida yanda ta dinga kwara amai hankalin Mama duk yabi yatashi sai sannu kowa yake mata. Ana gobe daurin auren Abie yakusa karamin hauka adakinshi, baisan me Ozo zaimai ko Aadil gobe idan an daura auren ba, baisan wani hukunci Ozo zai yankemai ba, dudda dai har yau baisan meye dalilin dayasa Ozo yace kar Aadil yasake yay aure ba amma yadamu, abinda haryau yake bashi mamaki shine Ozo yariga ya maidashi yaro ababba to menene dalilin shi nacewa karya sake yabari yay aure, kodai aure zaisa Aadil yadawo normal ne? Ajiyan zuciya ya fuzar yana fifita kanshi da hulan daya zare daga kanshi yacigaba da tunani, gashi yanzu Ozo bai bayyanar mishi ba koda warning ne yabashi ba, kawai yay shiru yasakamai ido kome yake planning oho. ******** Hausawa sunce rana bata karya! Yau asabar misalin karfe biyu na rana dubbanin jama'an

Table of Contents

Chapters

128 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128