Skip to content

Chapter 49

Chapter 49

In Bani Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

Hamida tayi kaman ba itaba tawani irin fashe da dariya tana kallon Zainab din tana yatsine hanci tace "hmmm saisa naji wari" wani irin gudu Zainab din tayi tabita, da gudu Hamida ta saki tsintsiyar akasa tana ihu tana dariya tana kwalama Mama kira Kaka tace "Allah ya wurgo ubanku gidan yaga abinda kukemai kulllum agida inya tafi masallaci" tasakai ta shige falon tana Kwalama Mama kira, fitowa Mama tayi daga dakinta rike da charbi tace "ina kwana Umma" daure fuska Kaka tayi ita a dole fushi take tace "lau, ba gaisuwar ki nazo najiba nazone nafada miki ki kira Lami tazo ita da mijinta, sanan kuyi hadadden girki, baki zanyi da sassafen nan, girki mai rai da lafiya fa" ahankali tace "to Umma" juyawa tayi zata fita saikuma tajuyo tace "ina Ihsan banganta ba?" "tana daki ne, tari take da mura shine nace kartai sharan" "maganin shan ruwan sanyi, babu randa bana wakar subar shan ruwan sanyi amma saisu nuna nai kadan, anjima tazo ta amshi zuma da tafarnuwa awajena tasha zatasami sauki, tarin zai lafa" ahankali Mama tace "to Umma angode" yaye labulen tayi tafice daidai Baba na bude gate yana shigowa sanye da farin jallabiya da hula akanshi da sauri su Hamida suka gaidashi amsasu yayi da sauri ganin Kaka yasa yataho dadan saurin shi yasamu ya lallabata, shan mur Kaka tayi ta dauke kai kaman bata ganshi ba tai hanyar Sasan ta, da sauri ya cin mata yasha gabanta cikeda damuwa kaman zai mata kuka yace "haba Umma inata gaidake kinki amsani wai har yanzu baki huce ba eh?" hararanshi tayi tace "gafara kabani sasana zan shiga ko" matsawa yayi hakan yasa tabude kofa ta shiga yabi bayanta da sauri ta shiga falo ta zauna akan kujera da sauri ya zauna kusa da ita ya daura kanshi akan kafarta ko kadan ya tsani yaga Kaka na bata rai dudda yasan ba'a mata komai kawai itake kirkiro rigima da kanta amma baya taba barinta ta dinga fushi for long, ta riga ta tsufa d fact dat she's very strong bai zama guarantee na cewa wani ciwon bazai kamata ba saisa yake lallabata dan yawan fushi zai iya jawo mata hawan jini ko ciwon zuciya, ahankali yace "kiyakuri Umma na bazan kara ja dakome zaki ceba, kowani hukunci zaki yanke kinyi daidai bazan kara cewa wani abuba Umma kinji" sosai zuciyarta yay sanyi amma saita daure tace "kai alkawari bazaka kara ja da hukunci naba?" da sauri ya daga kanshi jintamai magana yace "eh Umma kome kikafada daga yanzu hakan take kuma haka za'a bita bazan kara cewa wani abuba" kallonshi tayi saikuma ta kece da kuka taja bakin zaninta ta daura akan fuskanta tana share hawaye, arude yace "dan girman Allah Umma kidena kuka, wlh, wlh, wlh Umma kinji na rantse miki bazan kara, bazan kara ja da maganan kiba ke zaki dinga yanke hukuncin komi daga yanxu" cikin kuka sosai tace "baka sona ka tsaneni Sama'ila gani kake takurama nakeyi dankaga kai kadan karagemin aduniya baban Faruku mai sona maijin maganata ya rasu, wayyo Allah na, kaduba fa da baki daya nacemai yasaki shegiyar matar nan nashi Maman Faruku ya saketa amma kaiko kullum nunamin kake ban isa dakaiba, banjin dadinka ko kadan, agaban matarka, yayanka, kai agaban duk duniya ma kake nunawa niba komi bace agareka ba, nasan inda ace kasan guban dazaka sakamin a abinci naci namutu da tuni kasamin naci na mutu danka gaji da wahalata da matsalata so kake ka huta" "innalillahi wa innailaihi raji'un Umma, Umma dan yarasullullahi kiyakuri wlh bazan taba iya kashe uwata ba uwardata haifeni ba" tadan hujin yatsun data daura akan fuskarta take kallonshi yanda taga yay kaman zaiyi kuka dukya tsure yasa tai wani irin murmushi jin dadi aranta dan tasan ko yaji abinda ta aikata anjima bazaice kalaba sabida fargaban karta sake irin abin nan, share hawayen tayi tass tass tai tagumi tai shiru tana kallon sama kaman wacce akama rasuwa, ahankali yace "Umma, Ummana dan Allah ki kalleni" kallonshi tayi sai shar saiga hawaye, rudewa yayi gwanin ban tausayi yatashi tsaye daga kan kujeran yasa hannu a aljihu yaciro yan bandir din dari biyar biyar da wani makocinshi yanzun nan bayan sallan asuba yabiyashi kudin kaji guda dari daya saya, yadaura mata kudin acinya yace "gashi Umma sukenan gareni yau, nabaki kome zakiyi dasu kiyi amma dan Allah kiyakuri kinji" washe baki tayi kaman ba itace tagama kukan ba tadaga kudin tana kallo tace "kai Sama'ila wayan nan sababbin kudaden fa nawane?" "dubu dari da hamsin ne" murmushi tayi sosai tace "a'a baza ai hakaba, bandai dubu hamsin din saman kaika rike darin ko, Allah ampana" tai maganan tana kwance robalin ta kirgo dubu hamsin ta cire ta tura a lalita sanan ta mikamai sauran tana murmushi tace "Allah shi maka albarka, Allah karo kasuwa agidan kaji, Allah ya tsaremin kai yakaremin kai daga shairin mahassada kaji Sama'ila Sama'iloli yaci kafan bunsuru yahana Kaka bacci" murmushi yayi sosai aranshi yace Umma da son kudi yarasa uban me zatai da kudi haka hatta lipton shiyake kawomata ko tsinke bata siyafa amma sai masifar son kudi, "kanajina" da sauri ya kalleta tace "yau bazaka fita gidan kaji da wuri ba zamuyi manya manyan baki ne" da sauri yace "su waye Umma?" dariya tayi tana ballan goro tace "in sukazo zaka gansu, ka kira Mijin Lami yazo dakuma limamin unguwa, sanan kayoma Haleematu cefane nace ta girka haddden abinci wanda zamu tarbi bakin dashi, ka siyo lemukan kwali kaji" ahankali yana kallonta yace "to Umma shikenan" murmushi tayi sosai tana washe baki tace "yauwa dan albarka na, tashi katafi tun jiya banga Faruku ba baizo yasha furan shiba shegen goran" dariya yadanyi yace "kina kewan abokin fadan nakine kenan anjiman nan nasan zaizo wurinki" dariya Kaka tayi tace "wanan shegen goran ne zanyi wani kewan shi Allah kyauta, nidai yi sauri kaje kayi abubuwan dana saka" to yace yafice yanama kiran Abban Ra'is sukace suna hanya dan Mama takira, anty Lami na zuwa itada Mama da yaran su Hamida da Zainab suka fara girkin bakin Kakan, sukuma su Abba suna falo suna hira, wuraren tara da rabi suka gama komi Kaka dataci gayu cikin wani lashin hadari lace best lace dinta kenan tunna aurenta ne, bata saka lace dinan sai occasionally, tashigo kitchen din sai albarka take samusu, bakaramin Mamaki sukayi ba ganin kaka da kayan dan sunsan sai akwai babban abu take sawa, Zainab data gimtse dariyan ta tace "Kaka wlh hadari lace dinan baya miki kyau" dudda ta mata abaya Hamida ta sunnar dakai tana murmushi, Kaka tace "dan ubanki lashin nan ya girmi ubanki, tunna akwatina shegiya yar baka rubabbiyan yarinya kawai" turo baki Zainab tayi tawuce ciki Hamida tabi bayanta sum sum Kaka tabita da kallo. Kujera taja ta zauna a tsakar gidan, Allah Allah take suzo so kawai take dazaran taji sallama ta shigo dasu, wani almajiri karami ne yabude gate ya shigo da sauri ta tashi tace "kai baki suka aiko ka?" da sauri yace "a'a Hajiya sadakan biyar ko goma nasai omon wanki" wani irin dogon tsaki taja takoma ta zauna sanan ta chusa hannu a lalita tace "zo ungo" tamikamai naira hamsin karba yayi yanata mata addu'a sanan yajuya

Table of Contents

Chapters

128 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128