Skip to content

Chapter 32

Chapter 32

In Bani Book One Complete Hausa Novels 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

irin tureshi cikin tsananin fushi har yana buga bango tace "let go off me" da sauri tai wajen Abba ta kalli Abba cikin tsananin faduwan gaba tana kuka bakinta har rawa yake tace "A..bba wl..." cikin wani irin zuciya Abba ya dauketa dawani irin hadadden mari da baitaba mata shiba tunda ya haifeta jikake "pau!" tai wani irin tangal tangal tai baya zata fadi tsabagen yanda marin ya shigeta zaro ido Aadil yayi yazo wajen da mugun sauri yatare ta tafado jikinshi luuu kaman wacce ta suma, fashewa da kuka sosai Aadil yayi ya kalleta yanda take kokarin ta bude ido ma takasa, cikin wani irin tsananin fushi da zuciya yawani irin kalli Abba, fizge ta Abba yayi daga hannunshi cikin fushi yakara daga hannu zai sharara mata mari Aadil yawani irin fizgota da karfi ya rungumeta ajikinshi ya kankameta sosai kanshi na girgiza wa sosai jijiyoyin gaban goshinshi sun fito idanunshi sunyi jajir ya kalli Abba da jajayen idanunshi yay wani irin ihu ya nunamai hannu yace "stop beating her mugu". Yay maganan yana kara kankameta ajikinshi sosai da kyau yana kuka shima kaman yanda take kukan tana neman fizge jikinta daga nashi dan wani bala'in yake kara jefata, a zuciye Faruk yazo zai wuce Abba ya damko Aadil Abba yarike mai hannu cikin tsananin bacin rai batare dayace komiba, daidai lokacin Hamida ta fizge jikinta daga na Aadil dake kuka sosai da karfi ta tureshi tana kuka tace "stop touching me" tajuyo cikin tsananin tashin hankali da sauri ta tsugunna tasa guwiwanta akasa ta hada hannayenta, cikin kuka bakinta har rawa yake tace "Ab...ba dan Allah, Mama" takira sunan Mama da jikinta yay wani irin mugun sanyi idanunta sunyi jajir tana kallon Hamidan tace "Mama p..pl.." tama kasa magana tsabagen yanda zuciyar ta ke bugawa tajuya ta kalli Kaka dage mata wani irin mugun kallo tace "Kaka dan Allah kiyakuri wlh, wlh bansan yabiyo ni...." cikin tsananin fushi Mama ta fizgota tsaye tawani irin watsa mata mari, zatakai mata na biyun Aadil yajawota da karfi har Mama ne neman faduwa, yaboyeta abayanshi dudda yanda take fada dashi akan yasaketa yaki ya rike mata hannu gam yana make mata kafada Mama ta saki baki tana kallon ikon Allah yanda yarike Hamidan dayafi karfinta yana boye ta abayanshi kaman wani mijinta, cikin tsananin fushi Faruk yay kan Aadil Abba yawani irin dakamai tsawa yace "karka sake kataba dan mutane Umar karkai kisa agidana, yarmu itata nunamai gidan nan, ita ta shigo dashi, ita ta..." cikin fushi da kunan rai Kaka da tuntuni batai magana ba ta nuna Hamida dake kuka sosai a tsugunne Aadil shima a tsugunne a gefenta yana kuka yana leka fuskarta kaman wani yaro dan yaye tace "Hamida wlh kincuci kanki bamu kika cutaba, inda kinsan aure kikeso dakin fada anhada bikin ki dana Ayush tuni, kullum sai munafinci kina sussunar dakai ke adole mai tsoron mutane, ke adole ustaziya, hijabin nan biya biya har kasa yake sharewa ashe iskanci kikeyi, Sama'ila" takira sunan Abba cikin wata irin kakkausar murya tana share hawaye da bayan zanin ta tace "wlh Sama'il, kaji na rantse maka da Allah, tun jiya da Hamida tadawo bata bari nasata a idanunaba, bayan magriba yarinyar nan ta shigo gidan nan Sama'ila, yarinyar da kullum kofarta a bude yake kwana wlh tana shigowa jiya ta garkame kofan da sakata bam, ni dama nadinga jin motsi a dakinta harda ihu dasu barambarama kaman ana kaukawa.." tasake goge hawaye tana kallon Hamidan dake kuka sosai tace "babu yanda banyi da itaba tabude na dubata taki wai bacci zatayi, nai nai tafito to tazo taci abinci tadau tuwonta dake falo nan ma taki ashe tanada babban abinci ne acikin dakin, koda asuban nan danazo kin budemin tayi dudda mun saba sallan azuba tare a dakina ashe da kwarto tazo, yanzu Hamida har gida, har Sasa na, har gidan mahaifin ki zaki taho da namiji ki kawoshi shashina dankin rika, kin balaga, kinajin kanki sa'ar uwarki gaki kema kin tasako abinda uwarki kedashi kema kinada shi, to wlh bari kuji nafada muku dukan ku" tai maganan tana gyara tsayuwa tadawo gaban Abba ta tsaya ta nunamai Hamida da yatsa tace "nice uwarka daiko Sama'ila, nice kuma uwar mai gidan nan, sanan nidai bantaba iskanci ba dana auri ubanka ba, ubanka ma baitaba iskanci ba, sanan kaima baka taba iskanci ba dan haka bazan taba yarda dawata yar iska a matsayin jikata ba wlh, ni dama batun yauba nasha cewa Hamida ba jini na bace dan komi nata daban ne agidan nan bakaga kyan ta ba" tunda tafara maganan Mama ta kafeta da ido, hararanta Kaka tayi tace "kinsan menake fadi ai, dan haka Sama'il wlh dole ka zaba koni ko yarka, Hamida ta tattara tabar min gidana ga uwarta nan tafadi mata waye mahaifinta taje chan tasame shi, dagayau itaba yarka bace dan bama tayo komi nakaba, da uwarta take kama kaman tai kaki kanajina ko" wani irin runtse ido Faruk yayi zuciyarshi na tafarfasa dan sosai yaga haukan Kaka yatashi yau tafara maganganun banza, ahankali Abba cikin kwantar da murya yace "Umma kibari an...." "kamin shiru nace mara mutunci rubabben yaro kawai to wlh bazan bari kazama zanin daurawan mace ba" Kaka ta dakamai tsawa tace "tunda bazaka iya koranta ba nizan koreta kuma wlh inga wanda ya isa yadawo da ita gidan nan, na rantse da Allah saina tsine masa" ta kalli Hamida dake kuka sosai a tsugunnen tace "dau kwarton ki gashinan ya tasaki agaba yana kallo yana kuka kaman sabon maye, ki tashi kibar gidan nan yar iska, wato har cemai kikayi yadinga abu kaman dolo ko makira mai kama da uwarta, dau kwarton nan kibar gidan nan kafin nabar Faruku ya kaishi lahiran" Kaka ta daka mata tsawa. "tashi kibar gidan nan nace" cikin fushi Faruk yace "wai ina zatane Kaka? Ga wanda yabiyota bazaku ce komiba kuna cewa tabar gidan mahaifinta ina kikeso taje eh, kunki tsayawa ku saurari yarinya, ina kukeso taje?" "gidan uwarka zata" Kaka tabashi amsa cikin tsananin bacin rai tace "nace gidan uwarka zata, wlh ka kara magana anan wajen saina maka shegen duka na rantse da Allah, Sama'il kama Faruku magana ya maidani sa'arshi yauzan nunamai na isa da kowa a gidan nan dan ubanshi" ta kalli Hamida tace "tashi kibar gidan nan, wlh inhar batabar gidan nanba saina fada rijiyar sasan ku na rantse da Allah" kin tashi Hamida tayi sai kuka take tama kasa magana, kanta Kaka tayo hakan yasa ta tashi da gudu tafada jikin Mama tana kuka tana haki da kyar tace "Mama wlh shiya biyoni, mahaukaci ne, shine shine ya taimakeni a..." wani irin ingizata Kaka tayi har saida tabuge su Zainab tafita daga dakin tafadi akasa timm, da sauri Aadil yatashi yana kuka sosai ya bangaje Kaka da saura kiris ta fadi ta rike kofa yafita yadago Hamidan da sauri yana kuka sosai yasa hannu ya share mata hawayen yace "stop crying i will call police to come and arrest them, they're beating u, they're very wicked people" hanunta ya kalla data gurje yana dan jini yarike hanun da sauri yana zaro manyan eyes dinshi yakai hanun bakinshi da sauri yana lashe jinin yana kuka sosai, sosai take kuka tana kallonshi

Table of Contents

Chapters

128 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128