Chapter 83
Chapter 83
buƘatar ki samu kulawa sosai don haka kada ki Ɗaga hankalinki don Allah ciwon fa yanzu da sauƘi". da sauri na miƘe na ce"haba anty halisa ni fa ba yarinya bace kamar da,kowa fa ya shigo fuskarsa babu daƊi,ni nasan aƘwai abinda ake Ɓoyemin."Na faƊi hakan cikin kuka na tashi tsaye ina jin wani irin jiri yana Ɗiba ta,ga uwar yunwa da na keji wacce ta gama cika min ciki na ce"anty halisa don Allah zo muje ki nunamin Ɗakin da aka Ƙwantar dashi"?. da sauri ta ce"a'ah fa khairat bazan iya rakaki ba gaskiya,kinga ba kida lafiya kuma bayan haka mijinki ma fa yana cen yanzu na baro sa acen,kinga ai babu daƊi ki dai bari ki samu lafiya sai kije".da sauri na Ƙarasa kusa da ita ina kuka na ce"don Allah anty halisa ki rakani in duba sa,zuciyata ji na ke tamkar zata fito don Allah". sosai take kallona cikin mamaki,wato khairat micijin sari ka noƘe ce,wato duk tsanar da take ce wa ta yiwa yaya Bilal ashe duk Ƙarya ne?to idan ba Ƙarya ba me yasa ta damu don ba shida lafiya?. ganin khairat Ɗin ta dage ne yasa ta ce"to khairat muje".ta Ɗakko min jaririyar muka fito,ina dafe bango ina tafiya jirin yana Ɗiba na amman a haka har muka isa Ɗakin,duk naji jikina ya Ƙara yin sanyi sosai. da mutane sosai a Ɗakin duk suka zubomin ido mamaki Ƙwance kan fuskarsu har da shahid a Ɗakin,da ammi mahaifiyarsa da kuma mama har dasu yaya Aliyu,ga hajiya kaka a gefe su Rashida,sai maryam wacce bata fi wata biyu da haihuwa ba,ta haifi Ɗanta na miji,me sunan yaya Bilal. saurin dafe jikin bango na yi ina waro ido waje,ganin yaya Bilal Ƙwance kamar matacce an saka mishi abin shan numfashi ya yi wani irin fari fauu ga kuma ramar da ya yi,an saka masa kaya ruwan skye blue irin na marasa lafiya. wani irin kuka na fashe dashi tuni na tsugunna Ƙasa da rarrafe na Ƙarasa bakin gadon,saboda Ƙafufuwa baza su iya kaini wajensa ba,na ce"Yaya Bilal anya kuwa kai ne?me ya faru da kai?wani irin ciwo ne wannan?".duk ni kaƊai ke sambatu na kamar mahaukaciya sabon kamu,babu wanda ya cemin Ƙala,sai ma harara da wasu ke bina dashi. ban ma san na riƘe hannunsa ba sai yanzu na Ƙara ƘamƘame hannunsa na ce"don Allah yaya Bilal ka tashi,idan ka mutu nima tabbas zan iya mutuwa,da kai na saba yaya Bilal tun ina Ƙarama ta ka nuna min so,ka nunamin Ƙauna,haƘiƘa banyi maka adalci ba". Da sauri shahid ya tashi ya fita waje,duk zuciyarsa babu daƊi wani irin kishi yaji ya turniƘe masa Ƙirjinsa,ya zauna kan wani benci ya saki kuka kamar Ƙaramin yaro,mutane sai wuce wa suke suna kallonsa yana son khairat da duka zuciyarsa yana jin ciwon rabuwa da ita,amman ya zama dole ya yi hakan don ayanzu ya gano ce wa ba Ƙaramin so khairat ke yi wa tsohon mijinta ba. Yana zama ammi ta biyo bayansa don ganin halin da Ɗanta ke ciki,itama duk zuciyarta babu daƊi ko kaƊan,ta ce"shahid ka yi haƘuri ka ka baiwa Allah lamarinsa,sam banji daƊin hukuncin daka Ɗauka akan aurenka da khairat ba,ka sani shi Allah yana tsara lamarinsa yadda yaso,khairat suruka ce ta gari a azamana da ita dana yi,bata taƁa yimin wani abu da raina zai Ɓaci ba,kullum ƘoƘarinta shine ya za'ayi ta kyautatamin,don haka ni sam banji daƊin wannan abinda ka aikata ba." Murmushi shahid ya yi wanda masu iya magana suka ce yafi kuka ciwo ya ce"Ammi ki daina magana ki yi shiru,saboda ni kaƊai nasan halin da nake ciki xuciyata tana yimin zafi sosai akan wannan sakin da na yi wa khairat,wanda ita kanta bata san na yi mata ba,ammi jiya fa dana shiga wannan bawan Allahn kiran sunan khairat kawai ya ke,sannan ciwon zuciya ya kamasa saboda Ƙaunar khairat da ya ke yi,Ammi ina da imani ina kuma da tausayi bazanso nima ayimin hakan ba,ni nasan nima zan iya shiga wannan halin akan Ƙaunar khairat,amman babu komai zan karƁi Ƙaddarata insha'Allah". ya rungume mahaifiyarsa yana kuka me tsuma zuciyar me sauraro,shahid kiran sunan Allah kawai ya ke yi,halisa ta fito daga cikin Ɗakin da jaririyar a hannunta ta tsaya a tsaye tana kallon shahid wanda ke Ƙwance kan cinyar mahaifiyarsa yana kuka kamar Ƙaramin yaro. sosai ya bata tausayi ta matso a hankali inda suke ta fara magana cikin harshen turanci ta ce"shahid ka yi haƘuri ka fauwalawa Allah komai,amman banji daƊin sakin da ka yiwa matarka khairat ba,don ba'a wasa da aure". a hankali shahid ya tashi daga kan cinyar ammi ya ƙarasa wajen halisa ya amshi ƴarsa.wacce ke ta baccinta hankali ƙwance.me kama dashi sosai ya zauna yana kallon ƴarsa cike da so da ƙaunarta.sai yanzu ma ya tuno bai yi mata huɗu ba ba.wasu hawaye suka zubo masa ya share su tuno da halin da yarinyar zata kasance na rashin mahaifiya akusa da ita.shi da yarasa mahaifinsa ma ya damu sosai balle kuma mahaifiya.gashi nigeria ba wajen zaman bane dole zai koma masar.ko england tunda dai shi ɗan asalin ƙasar england ɗin ne. yana gama raɗa mata sunan Ammi ta amshe ta.tana manna mata kiss a goshinta na jin daɗin ganin jikarta ƴar shahid gudan jininta.lallai wannan yarinya zata sha gata.ya ce"Ammi na raɗa mata suna da Rahma(khairat)taci sunan mahaifiyarta. 07068606171 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨 _*Miss green ce*_🤙🏿 1003. . . . . . .1004 ---------Ammi ta ce"Allah ubangiji ya raya mana ita.amman ni dai zuciyata bata yimin daɗi wallahi,shahid ba kai kaɗai ka yi rashin khairat ba har ni,ni kaɗai nasan irin kyautatawar da take yimin.Allah ya tashi kafaɗar baban yaran na ta".dukkansu suka amsa da amin. Hajiya kaka ta ce"khairat don Allah ki fita a ɗakin nan ina ce wa kece kika tayar masa da ciwon nasa ko?tsabar rashin tausayi da kuma imani haka ki ka rufe idonki ki ka ce kin tsanesa.amman shine yanzu zaki wani dawo nan?maza ki tashi ki fita cen bama nemanki". Sosai na fashe da kuka har da majina na ce"haƙiƙa hajiya kaka ban yi wa kaina adalci ba.na cuci kaina da nunawa yaya Bilal tsana har haka.ko da me ya yimin bai cancanci inyi masa haka ba.don Allah ina neman yafiyarku ku yafe min".na faɗi hakan ina kuka sosai. Likita yana shigowa ya bada umarnin kowa ya fita zai duba Yaya Bilal,haka aka yi kuwa kowa ya fita sai ni kaɗai.har hajiya kaka ta fita sai kuma ta dawo ta ce"to ke uwar ƴan marasa jin magana komawa kika yi kika zauna kamar mijinki"?.jin hajiya kaka ta faɗi hakan tuni na tashi gabana yana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87