Chapter 16
Chapter 16
tare daya ciresu ba,kayan aikin likita yaya Aliyu likita ne na ganycology ma'ana likitan mata. Yana ganin Rashida ta shigo ya tashi da sauri yana kallonta jikinsa duj babu ƙwari ya zauna yana ce wa"Rashida kinga yanzu abinda shirin mu ya ja mana,kin fiya zurfin ciki Rashida kin hanani gayawa kowa saboda sai kin gama makaranta za'a sani how comes hakan ya faru."ya faɗi hakan yana kallon Rashida.mu dai duk muna tsaye mun kasa zama sai da kaka ta ce"to aadarawan sarki ku zauna kun wani tsayamin akai".zama mukayi a kan capet ɗin ɗakinta ba ta ce komai ba ta janyo wayarta ta ce"ke Abin cikin ƙwai kirawo min abdullahi dai malik dai auwalu duk ki kirawomin su alokaci ɗaya." Gabana yana faɗuwa na fara kiran Babana faɗa masa,sannan na kirawo su suma duk akayi sa'a suna cikin gidan dawowarsu kenan,su dukansu ta tarasu sannan ta ce"kun gane min waɗan cen ja'iran yaran".ta nuna su Rashida da Aliyu dukansu sunkuyar da kansu sukayi don kunya sannan kaka ta ɗora da cewa to kada ku ɗoramin laifi don nima ban sani ba?sai yanzu".duk iyayen nasu su suke kallo sun kasa gane inda maganar mahaifiyartasu ya dosa.Baba Auwalu ya ce"to umma me kuma ya ƙara faruwa kin sakamu acikin duhu?". "Duk yanzu zaku fito daga cikin baƙin gawayi ma ku ƙara tsundumawa cikin baƙin gawayin tsabar na sakaku acikin duhun?to waɗannan yara Rashidatu da Aliyu ashe soyayya suke basu taɓa barin wani ya sani ba sai yanzu ne fa ni na kama su". ni da bama dani ake ba kunya kamar ta kasheni dukanmu mu ukun muka sunkuyar da kai,ana cikin hakan Baba ya ce"shin da gaske kuna soyayya?".da sauri kaka ta ce"ikon Allah ka jini da malik au tambayarsu ma ka ke da gaske ne ko?na sambaɗa ƙaryar dana saba muku ko?to ko ubanku kafin ya mutu bai taɓa ce min na yi masa ƙarya ba sai kai soja marnari daga ne sa".ganin mahaifiyar ta su za ta sauka daga bigeren da suke ciki ya ce"ki yi haƙuri umma ba fa nufina kenan ba kin san yaran yanxu suna iya canja ra'ayi a ko da yaushe".ya faɗi hakan yana kallon mahaifiyar ta su. "Au to na ɗauka ƙaryata ni xaka yi ai ga Abin cikin ƙwai nan tasan komai sai ta faɗa maka,shegiya baƙar banza ai duk tare da ita aka ɓoye komai tunda sun iya munafunci".da sauri na ɗago kaina ina kallon kaka ta ce"daina kallona da idanuwanki gwala-gwala irin ns baba tunde inyamurin kakanki".da sauri na ɗauke idona don nasan kaka tana cikin fushine,arayuwarta ta tsani abinda zai taɓa mata jikoki sai kaga duk hankalinta ya tashi. "na ce daku na ke magana".cikin tsawa Babana ya yi maganar don shi aƙwaishi da zuciya Aliyu ne ya buɗe baki da ƙer ya cire farin glass ɗinsa irin na likitoci ya ajjesa acikin ma'ajiyarsa sannan ya ce"ƙwai Baba da gaske ne muna soyayya tun 2 years da ta wuce". "amman Aliyu anyi lusari wallahi yanzu kana son yarinya amman shine ka yi shiru har sai da aka fitar maka da mata?to yanzu yaya ka ke so muyi?so ka ke ka raba mana zumunci ko?to wallahi baka isa ba".inji Baba Auwalu wanda ya harzuƙa sosai don shi arayuwarsa baya son raini ko kaɗan. "To ni fa bawai na tara kune anan kuyi min wani ƴan faɗa ce faɗa ce ba,Aliyu dai ya tabbata mata 2 zai aura shikkenan sai ku tashi acigaba da shirye shirye,kuma duk shegiyar matarda ta canza muku karatun dana yi to wallahi sai ta fece garinsu".tana faɗar hakan ta tashi ta shige uwar ɗakinta. Sim sim ni da Rashida muka bita kawunanmu a ƙasa,shima Aliyun zai tashi suka zaunar dashi sukayi masa nasiha sosai sannan suka cigaba da hirar yadda abubuwan zasu tafi na biki.to Aliyu babu laifi yana da kuɗinsa doj yana samun kuɗi na albashinsa sa sannan yana sana'ar siyarda motoci daga cotonou zuwa nigeria wannan kuma shi da yaya Bilal suke don daman a manyan gidan daga Yaya Mohd sai Yaya Bilal sai Yaya Aliyu,su biyun duk rana ɗaya aka haifesu don haka tare suka taso babu abinda suke banbantawa,ko shawara ce sai Aliyu ya tambayi Bilal sannan ya ke jin daɗi,ammanfa akan zancen son ƙanwarsa ya kasa gaya masa don kunyarsa ma yanxu ya keji don ya zama suruki. Jin wannan maganar ba ƙaramin hargitsi ya haɗa ba,don mama mairo mahaifiyar yaya Aliyu tuburewa ta yi ita fa ɗanta bazai auri ƴar maƙiyiyarta ba,da ya ke macece tsayayyiya sai gashi tana neman canzawa Baba Aliyu tunani,ai kuwa kaka ta kirasu ta sillesu tsaf ta kuma ce"ke Mero sanda za'a aureki ba tuwo tuwo ki ke a bakin titi ba?".sai kuwa mero ta bazo idanuwa waje kunya duk ta isheta,ta sunkuyar da kai tana jerowa tsohuwar Allah ya i'sa. "Oho ke ban hana a aureki ba sai ni zaki hana a auri jikata ko?ta haɗiyi zuciya ta mutu ko?to wallahi baki isa ba aure kamar an ɗaurashi ne,don haka ki fita daga idanuwa na in rufe duk abubuwan da ki ke bana son yin magana ne don kada in zama uwar banza don haka kada ki yadda ki shigo gona ta don haka ki ki yaye duk sanda kika cikani sai na faɗawa kowa sirrinki". da sauri mama mero ta ƙwalalo idanuwanta don tasan kaka za ta iya faɗa to tabbas ta tarwatsa mata rayuwarta shikkenan ƙarshenta yazo,da sauri ta ce"Allah yaja daran Hajiya kaka insha Allah haksn bazai ƙara faruwa ba."harararta kaka ta yi sannan ta ce to ass- ass na sallami mutum ya tashi ya bani waje don nan ba filin tuƙa tuwo ba ne ehe". da sauri ta yi fit ta fita don ba ta son ƙara jin maganar da kaka za ta faɗa don yanzun ma ta gama faɗin abubuwa marasa ƙyau akanta. Tana tashi kaka ta kalli Baba Auwalu ta ce"to sallamamme ni kam yanzu na sallamawa mero kai dai ka tashi ka bita don na ga jikinka har rawa ya ke ka bita". Sunkuyar da kansa ya yi sannan ya ce"umma ki yi haƙuri daman wai ina tausayawa masa ne riƙe mata biyu a ƙananun shekarunsa".ya faɗi hakan kansa aƙasa. "Oh ni Ramatu idan baka mutu ba zaka yi kallo wai ni Auwalu ji ka ke na manta ne yanzu fa matanka biyu kuma kana son ƙaro ta uku ita mero kana aurenta ko shekara bata yi ba ka yi mata kishiya ba?babu yadda banyi ba akan kada ka ƙara amman ka ƙara saboda ka gano shuwa duk ka gigice to ka fita idanuwa na wallahi,daman kai Auwalu duk ƴaƴana kai ne sallamamme akan mata Kamar wani zakara,to dai Allah ya tsari Aliyu da haka". Sunkuyar da kai ya yi sannan ya ce"to umma na tuba ki yafe min insha Allah hakan ba za ta ƙara faruwa ba".da hannu ta nuna masa ƙofa ya fita a hanyar fitowarsa ne yaci karo da hajiya Inna aminiyar Hajiya kaka gaisheta ya yi cikin mutunci sannan ya tafi. Bayan sun gaisa ne Hajiya Inna ta ce"Ramatu wai me je faruwa ne acikin gidannan na ga duk yaran suna wani ɗa-ri-ɗa-ri da mutum suna wani sunkuyar da kai." "ah to ai dole ki gansu a haka tunda gidan mutuwa kika zo?wai fa akan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87