Skip to content

Chapter 37

Chapter 37

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,302 words 0 views Progress saved
Download Book

yi ƙwanan nan tunda dai yanzu na samu wadda na keso". sunkuyar da kaina ƙasa na yi,kaf duniya ina tunanin babu macen da za tace bata son Ahmad don babu abinda baagi dashi,ƙyau,kuɗi,addini,ilimi,tarbiyya,kamala,sanin ya kamata,kai har dama waɗansu abubuwan. Ganin na yi shiru sai ya ce"a gaskiya ni ada na fitar da yin aure arayuwata saboda bazan ɓoye miki ba na taɓa yin aure acen baya sai dai gaskiya ko kusa banji daɗin auren ba,saboda banyi dacen mata ba,zanso inji sunanki baiwar Allah don naga kamar wayo ki ke son yimin ina ta zuba ba tare da kin faɗa min sunanki ba?". a hankali na ce"sunana Rahma amman ana kirana da khairat". "Wow nice name,sunan mahaifiyata ne da ke gaskiya naji daɗi,ammsn ina son ki faɗamin kina da ra'ayina ko kuwa?Don gaskiya ni arayuwata bana magana biyu,kawai idan har ina son abu to babu tabbas shi ɗin na keso babu mai canjamin tsari na,don Allah khairat inason ki faɗamin gaskiyarki akaina?Ni dai har ga Allah kin tafi dani baki ɗaya,na sadaukar da aikina na awa kusan huɗu saboda ke,wanda atarihi na ban taɓa yin hakan ba". Sunkuyar da kaina na yi don a gaskiya bazan ɓoye masa komai ba,don ayanzu an bada ni kuma ma gaskiya ko da ba'a bada ni ba,maƙalalliyar zuciyar nan ta wa tana wajen Yaya Bilal,duk da babu abinda Yaya Bilal zai nunawa Ahmad ɗin sai dai kawai fari,amman banda wannan babu abinda zai nuna masa. A hankali na ce"kayi haƙuri C/M ayanzu haka har an saka ranar aure na nan da sati uku masu zuwa za'ayi bikina,amman ka yi haƙuri gaskiyar daka baƙata ita na faɗa maka".na faɗi hakan ina sunkuyar da kaina ƙasa. Wani mugun jiri yaji yana ɗibarsa duk da jikinsa yadda ya ke kamar rainon ƴan rastling amman sai da ya kusa faɗuwa,ya buɗe kyawawan idaniyarsa sannan ya ce"khairat haƙiƙa kin burgeni da faɗamin gaskiya da ki ka yi amman ko babu komai inason ƙulla zumunci da gidanku,idan an tashi ɗaurin aurenki zanzo,ga wayata sakamin number ɗinki".?Ya faɗi hakan yana jin adadin zafin zuciyarsa na ƙaruwa,ciwon kansa nasan tashi masa ƴan awanni da haɗuwa da yarinya yaji kamar zai mutu idan bai aure taba,gaskiya wannan yarinyar tana da sa'a sosai don matan da suka amsa sunansu mata masu ji da kuɗi da komai,sunsha zuwa wajensa da furucin soyayya amman ko kallon ƙurarsu baiyi yanzu gashi kan yarinya ƙarama wacce a ƙiyasinsa bata fi 17 zuwa 18 ba. Samun kaina na yi da murmushi na amsa na saka masa na bashi,ya yi murmushi sai naga kawai hawaye suna zubo masa ya ce"khairat Allah yasa albarka acikin wannan auren na ki,idan babu Albarka Allah ya wargazar ko ƴata Inaas ta samu uwa tagari kamarki". Buɗe idanuwana na yi sanna na ce"au daman kana da ƴa ne?".Murmushi ya yi sannsn ya ce"ina da ƴa shekararta biyar amman yanzu mun rabu da mamanta tana hannun mahaifiyata,kullum burinta in samo mata momi amman na kasa hakan tunda bab haɗu da wacce na keso ba,sai yanzu Allah ya yi gashi kuma wani mai sa'ar ya rigani,to shikkenan ni zan tafi khairat saduwar Alkhairi". Tafiyarsa ma kaɗai abin kallo ce ina tsaye naga sun tsaya akusa dani ya ce"khairat idan babu damuwa shigo mu sauke ki agida?wannan titin babu kowa kuma bai kamata ki tsaya ke kaɗai ba,alhalin kuma kina amatsayin mace,macen ma mai daraja". Samun kaina na yi da yarda dashi na shiga muka tafi,har mukaje bai ƙara ce wa komai ba nima kuma bance ƙala ba,da zan fita har na saka ƙafufuwana awaje ya ce"khairat"!. Juyowa na yi cikin mamakin jin kirana da ya yi,na juya ina kallonsa na sunkuyar da kaina don bazan iya kallon cikin idaniyars ba,don yana da ƙwarjini sosai. Ya ce"khairat idan na yi miki ƙyauta zaki amsa"?.Ya kunnomin wannan tambayar na ce"zan amsa C/M tunda daga hannun mutum mai alfarma ta fito kuma mai mutunta mutane". Ɗan murmushin jin daɗi ya yi sannan ya ɗakko wani envelope ya miƙomin,amsa na yi cikin nutsuwa sannan na ce"na gode!ka gaida min da Inaas". Sosai naga murmushi ya bayyana akan fuskarsa saboda aduniya yana son mai son nasa,musamman ma kuma Inaas ƴarsa ya ce"naji daɗi khairat insha Allah zan kai gaisuwarki wajen Inaas". Nima murmushin na yi sannan na ce"to na gode sai anjima".ina faɗar hakan na juya zan tafi gida sai naga Yaya Aliyu da Anty khadija zasu fita. Tsoro ya kamani don nasan sun riga da sun ga C.M don haka na sunkuyar da kaina,ganin hakan yasa M.C fitowa suka gaisa da Yaya Aliyu sannan ni kuma na yi cikin gida kunya duk ta isheni. ina shiga Anty Khadija ta shigo ita ma sai naga tana wani washe min baki ta biyo ni har ɗakina lokacin ina cire kaya da ɗaurin ƙirji ajikina, sai kuwa ta ce"am daman khairat tambayarki zanyi"?.Ɗan ɗaure fuska na yi kaɗan don nasan tambayar daza ta yi kenan na ce"uhm ina jin ki"?. Sai ta nemi waje ta zauna ta ce"yauwa me ye kuma haɗinki da Commisioner of police"?.Tambayar ce tazo min abaza ta sai na ce"babu komai sai zumunci". Sai kuwa ta ce"a'ah fa khairat bana son ƙarya ni dai a iya sanina kaf ƴan uwanmu ban taɓa jin ance ɗan uwan mu bane,sai dai idan saurayinki ne?Ammsn gaskiya kuwa idan haka ne kin more saurayi mutum har mutum a tsaye kamar shi ya yi kansa,ga kuɗi ga komai,kuma naji ma ance ɗan sarauta ne ko"?.Ta faɗi hakan tana washe baki. Ban kula taba sai kuma ta ce"amman khairat yanzu sabida Allah ai an kusa bikinki sai dai ya yi haƙuri,amman wallahi ni dai da so samu ne ki aureshi don ni har yafi min yaya Bilal wanda a kullum ya ke wulaƙanta ki". Banza na yi mata sannan na yi shigewa ta banɗakin dake manne ajikin ɗakina ina mamakin shegiyar gulma irin ta anty khadija. Ganin banyi magana ba yasa ta tashi ta fita,babu abinda M.C ya ɓoye wa Yaya Aliyu a game da haɗuwarmu,ya amshi number yaya Aliyu ya ce"idan auren Khairat ya tashi ku faɗa min".sosai Yaya Aliyu yaji daɗi sannan suka yi sallama da M.C ya shige mota. Bai dawo gidan ba ya shige mota don ɗakko mama a filin jirgi da ƴan uwanta har uku,saboda bikin khairat don Yaya Aliyu ya yi mata bayani sosai amman fa mama ta yi baƙin ciki sosai,don gani take ai itama uwa ce kuma ya kamata ayi mata uzuri a nemi shawararta don za'ayi wa ƴar ta aure ba tare da saninta ba,badon Aliyun ya faɗa mata ba sai dai taji a gari kuma ga auren Salim da kuma Auren Aliyu ɗin,mama ta dinga yi wa Aliyu faɗa akan ƙarin auren nasa,amman sai Aliyu ya yiwa mamansa bayani sosai na abinda yasa zai ƙara auren,itama maman tasan wasu daga cikin halin Khadija ɗin, ta yi musu fatan alkhairi da samun zaman lafiya mai ɗorewa. *** "Ahmad lafiya naga yau duk idanuwanka sun kumbura kamar ka yi kuka?me ya faru da kai"?.Hajiya Ramatu ce ke yi wa ɗanta C.M wannan tambayar?. Babu abinda ya ɓoye wa mahaifiyarsa akan Khairat,ya ƙara da faɗin "Hajiya yanzu mata nagari sunyi ƙaranci acikin wannan al'ummar tamu,za kiga mata suna shiga ba-ga matan aure ba ba-ga ƴan mata ba,haƙiƙa babu abinda yasa

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87