Chapter 1
Chapter 1
[23/09, 16:15] Miss Green🍀: *🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!🥚* 📃Littafi na 1 By🪶 *Ummu maher(Miss green)🍏* _✨TEAM GAWURTATTU BIYAR 5✨_ ----------------------- Noticed⚠️Labari ne akan zazzafar Ƙiyayya,ban tausayi ban dariya,ban al'jabi,wa'zantarwa,nishaƊantarwa. *Godiya:* ina miƙa godiya ta ga dukkanin masoya na marubuta da kuma makaranta,ina ƙara muku godiya wajen nunamin kulawa da kuma soyayya Allah ya barmu tare amin. *Sadaukarwa* na sadaukar da wannan littafin ga mahaifiyata hajiya maryam moh da mahaifina engineer Bashir Abdullahi,Allah ya Ƙara musu lfy da nisan Ƙwana mai albarka. *Doka⚠️⚠️⚠️:* ban yadda a canzamin labarina ta kowacce irin siga ba,ba tare da an tuntuɓeni ba. Ku kasance da gawurtattu 5 don jin yadda za ta kaya. *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* ----------------------------------- HAJIYA KAKA POV 1🟨2 ... . . .Kana shigowa tunda kan layinmu zaka san cewa ana wani mashahurin biki a layin,gidane kato sosai daga gani ko da ba'a gaya maka ba kasan cewa gida ne na family house farin fenti ne dashi me tsari,a ɓangare kusan sha uku ne agidan. A babban hall ɗin na gidan ake sha'anin kamu,amaryar na hango taci adonta sosai cikin kayan fulani mai ƙyau da kuma tsari,ƴan matan amarya suna gefe suna selfie ana tsokanar amaryar. "Khairat ki yi sauri ki fito,don Kin san ke kaɗai suke ta jira".wacce aka kira da khairat ta jiyo,wow na faɗa don yarinyar irin yarannan ce black beauty,ta juya eyes balls ɗinta da ɗan ƙaramin bakinta cikin shagwaɓa ta ce"to Mama ganinan fitowa". Su Rashida ne suka shigo suna ce wa"don Allah Khairat ki fito kina ƙanwar ango amman kina yi wa mutane delay,ga ƙawayenmu nan duk sun zo mu kaɗai suke jira". tsaki Iman taja sannan ta ce"Allah Rashida kina nema mana raini wajen wannan kucakar yarinyar shiyasa ni bana son haɗa harka da ita ko kaɗan,yanzu muna zuwa wajen wasu ma sai sun tambayemu anya kuwa wannan ba ƴar aiku ba ce?". Wani irin baƙin ciki ne na ji ya tokaremin zuciyata amman babu yadda zanyi don Iman ba sa'a ta bace baya ga haka ma ni ba ma'abociyar yin faɗa bace. Jikina ne duk ya yi sanyi don ganin irin kallon dasu Iman suke min da ƙannenta su Baby,na rasa me yasa suka tsaneni agidan tunda duj ba haka suke yi wa sauran ƙannen na su ba amman ni daga zagi sai hantara,kaf cikinsu mutum biyu ne suke sona daga Rashida sai Amira.Iman babanmu ɗaya dasu amman kuma sunfi kowa ƙyama ta. A haka na zauna a tsararrun kujerun da aka ajje acikin gidan,ina juyawa na hango Hajiya Kaka wato kakarmu tasha gwaggwaronta harda jan baki,dariya na fara yi mata har ta yi gaba kuma sai ta dawo baya ta ce"ke kinji ja irar banza malik ne da Maryam su ki ke yiwa dariya don ni dai na fi ƙarfin uwarki da zaki sakani agaba kina yimin dariya yo me ye laifin wannan ƙwalliyar dana yi da zaki ringa yimin wannan dariya kamar kinga mahaukaciya?yo ko uwarki inyamura da take a uwar ango yau bata isa ta nuna min ƙyau ba,don haka ki shiga idona in rufe,shegiya ƴat baƙa kawai". tana faɗar hakan ta tafi tana taunar goronta tana cigaba da mitarta don Kaka ta tsani ta yi ƙwalliya kace bata yi ƙyau ba. Babu abinda yaban haushi a maganar kaka don daman idan da sabo mahaifiyata ta saba da wannan zagin da kuma toxarcin awajen kaka don ita arayuwarta ta Ƙi jinin mahaifiyata duk don a kasancewarta ba yaransu Ɗaya ba,uwa uba kuma gashi mahaifina ne Ya musuluntar da ita shiyasa gaba ki Ɗaya kaka ta tsani mama na,kullum cikin gori kuma abinda ke Ƙara bani haushi da kaka ko a gaban waye sai ta yi in dai Ƴan faƊan suka zo,yaya Aliyu shine Ɗan farin mama sai yaya Salim sai ni khairat sai auta afrah. "ke kuma Khadija ranar auren na ki kika saka wannan ɗamammun kayan duk jikinki a waje?Ina shi sokon angon na ki ya ke ne?da ya barki kika saka wannan kayan?.Wannan tozarcin da Kaka ke yiwa Khadija a lasifiƙa ta taƙarƙare ta ke faɗa son ranta babu abinda ya shafeta. Gaba ki ɗaya wajen shiru kowa ya yi don jin ƙatoɓarar da kaka ke yi,don yanzu kana magana masifar zata dawo kanka shiyasa ma kowa ya shafawa kansa lafiya don abin na ta sai ita ɗin. Rafi'atu ce ta kalli kaka cikin fushi ta ce"Ke kaka shigar da kika yi a matsayinki na tsohuwa babu wanda ya ce miki komai sai ke ce zaki saka yaya ta a gaba da masifarki". "inye a lallai Farouku ya baku daman cimin mutunci tunda gashi kina zagina a gaban uwarki bata iya magana ba saboda tana tsoronki to ko farouku ubanki bai isa ba,shegiya ƴar tsigi tsila". ƙwashewa akayi sosai da dariyar dramar kaka don idan ka biye mata sai a ƙwana a tsaye. Ana cikin hakan mukaji jiniya ta motoci ƙyawawa sun shigo cikin ƙaton gidanmu,ai kuwa sai Kaka ta fashe da kuka tana ce wa"To yau wai agidannan ni kuma kewa dariya tsabar rashin ta ido,ni dai wannan abin ya isheni ace ranar bikin jikata amman a nemi a kwashemin albarkar auren jikoki na to wallahi bazan yarda bari Soja Bilal ya dawo kowa sai ya ƙwashi kashinsa hannu". Gaba na ne ya yi wani mummunan faɗuwa ganin fitowar Yaya Bilal daga cikin mota ya yi ƙyau sosai cikin suite ɗinsa,ƙyaunsa ya ƙara fitowa sosai kamar ka ɗaukesa ka gudu,ƙyaunsa da nutsuwarsa sun ƙara fitowa sosai.na yi wani tagumi azuciyata ina tuna ranar da zan iya barin tunanin Yaya Bilal a cikin zuciya,Yaya Bilal namiji acikin maza yana da wani ƙwarjini da cikar zati,duk wannan abinda na ke yi Yaya Bilal bai san ina yi ba don tsakani na dashi hantara da kuma kallon banza,donshi aƙwaishi da miskilanci sosai. Cikin takunsa mai ƙyau da haiba ya ƙaraso inda Kaka take ya rungumeta yana cewa"my grand fa dafatan na sameki lafiya".da yake shiba mutum ne mai magana da yawa ba yafi yin magana kaɗan,ai kuwa nan kaka ta zage tana ta basa labarin cin kashin da aka yi mata,ina cikin satar kallonsa sai kuwa naji ta ce"kaga waccen ƴar baƙar ita ce ta fara wulaƙantani a wajen nan har kowa ya samu bakin yimin wulaƙanci,waiwayowa ya yi ya kalleni kallo ɗaya shima by mistake ya juya kansa,yaja hannun kaka suka tafi sashenta,kallonsu na yi cikin tsoro na ce"Rashida na shiga ukuna kinga wanna fitinanniyar tsohuwar zata jazamin ƙazamin duka,kinga wani banxan kallon da ya yi min kuwa?". Dariya Rashida ta yi sannan ta ce"ai ni dai na godewa Allah da ban ma haɗa ido da wannan mugun sojan ba amman wallahi da na yarda na haɗa ido dashi da tabbas naga wulaƙanci don wallahi haɗuwarmu baza ta yi mana ƙyau ba". Ɓata rai na yi na ce"ke kinga Rashida idan bazaki faɗi alkhairi ba to ki yi shiru don Allah don manzon Allah(S.A.W) ya ce ka faɗi alkhairi ko ka yi shiru". dariya sosai Rashida ta yi sannan ta ce"hmm so hana ganin laifi gaskiya Khairat ki rage son da ki kewa Yaya Bilal kada ya haifar miki da wata matsalar,don ni har tausayinki na ke ji kina ganin mutum kullum fuska a ɗaure ki rasa wanda zakice kina so sai shi,kuma ke kinfi kowa sanin baƘwa wani Ɗasawa dashi don
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87