Skip to content

Chapter 29

Chapter 29

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,293 words 0 views Progress saved
Download Book

433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 *YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS* Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: - *Enter your name:* (Cikakken sunanki) *Enter your mail:* (Email ɗinki) *Enter an username* (Sunanki) *Enter your password:* ( misali 12341234) *Confirm password:* (misali 12341234) Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂. *Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye. *Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks. Masu iPhone Zaku iya bibiyar shafinmu https://arewabooks.com [23/09, 16:19] Miss Green🍀: [03/09, 20:31] Ummu Maher(Miss Green): [03/09, 20:19] Ummu Maher(Miss Green): *🥚ABIN CIKIN ƘWAI* NA💋 UMMU MAHER(MISS GREEN) 29🟨30 . . . ."Na tsane ki zulaiha tsana mafi muni arayuwata,kin cutar dani kin cutar da iyali na,akanki na yi faɗa har da mahaifiyata ashe sakayyar da zaki yi min kenan?kin san ƴarki na da ciki amman don mugun hali baki taɓa faɗa min ba?ki ka barni a ƙudundune?to cutar ta yi haka,ayau ba sai gobe ba na ke son ki bar min gida na." yana faɗar hakan ya fita cikin fushi har yana haɗa hanya,hajiya kaka ta ce"haƙiƙa wannan abin ya bani mamaki kuma ya ɗaure min kaina,bana fahimtar komai?wutar kaina baki ɗaya ta ƙone,wallahi ko mutuwar mahaifiyata bata kai wannan abinda na riska acikin jikokina ba,tunda ita dai nasan mutuwa ta yi ba abin kunya ta yi ba,khairat mun nuna miki so da kuma ƙauna amman abinda zaki saka mana dashi kenan?to babu komai kije duniya ce ta ishi bawa riga da wando,ke kuma zulaiha da ki ka ɓoye mana komai kije ke da Allah shine zai yi wa ɗana sakayya". I'tama tana faɗar hakan ta fita tana kuka,jirin da na ke jine naji ya ƙara hawa sosai bibbiyu na ke ganin mutane,tashin hankali da kuma ɗimuwa sun cika doɗaɗɗiyar ƙwaƙwalwa ta wadda ta kasa ɗaukar komai ayau.ni kaina tambayar kaina na ke akan wannan ƙaddarae da ta afkamin balle in amsa tambayar wani?. motsi mai ƙyau mamana ta kasa yi kuka kawai take tana kiran sunan Allah,shekara 30 kenan tunda ta shigo dangin Malik take ganin abubuwa kala kala,na rashin ƙyautawa daga danginsa wai don ita tuba ce. "Hmm daman wannan ranar na ke jira zulaiha,ranar da zanga ƙarshen wayonki da kuma makircinki,wai ke mai sanin miji,mai kuma tattalin miji,wacce miji yafi so,hmm sau gashi tun kafin akai ko ina kin fara ganin sakamakonki,muɗin dai da ki ka gani a gidan dole a tafi a barmu,sha-sha kawai". Mama iklima ke faɗin haka mahaifiyarsu nadiya,ita kuwa anty maman iman ce wa ta yi"hmm ni fa wallahi wannan hukuncin ma baiyi min ba,so na yi ya lakaɗa musu ɗan banzan duka daga ita har ƴar banzar ƴar ta,shegiya me yawon karuwanci,yanzu kinga ai sai asan yadda za'ayi,kin ɓata mana sunan gida yanzu za a dinga kallonmu a wofi". Caraf mama iklima ta amshe"La-la-la ni fa ko ajikina wallahi tunda dai ba ƴata bace cen su ƙarata uwarta ta ɓatawa suna amman ba mu,haka kawai aka ƙalawa ƴaƴanmu sharri a banza yanzu gashinan ai ƴarki har abin kunya ta yi". Asanyaye mahaifiyata ta tashi da addu'ah a bakinta,mahaifiya ta macece mai yadda da ƙaddara ta kallesu kamar babu wani abinda ya dame ta ta ce"Iklima &mariya ku kasance masu faɗin alkhairi akan ƴaƴan wasu,sai kiga kuma naku ƴaƴan sunyi albarka amman ba zagin ƴaƴan wasu ba,matsalar khairat ni ta shafa ba wani ba,kuma mutuwar aure ba ku aka saki ba ni aka saka don haka wannan ba matsalarku ba ce,ku fita daga ɗakin nan". ta faɗi hakan cikin ɗaga murya". Dukkansu sun tsorata da canjin yana yin Zulaiha,donbata taɓa yi musu koda musu bane,amman yau ita ce har da ɗaga musu harshe". "hmm zulaiha kina borin kunya ne dai kawai saboda asirinku ya tonu ke da gantalalliyar ƴarki ƴar daɗi maza,to kodai baki ce mu fita ba yanzu zamu fita daga wannan ɗakin shaiɗaniyar ƴar ta ki don haka mu mun fita kada ma garin tsayawa wata masifar ta shafi namu ƴaƴan don ku ba alkhairi bane acikin al'umma. Da sauri suka fita don sunga yadda mode ɗin mama ya canja sosai kada silar tsayawarsu ta yi musu wani abin. Kulle ƙofar gam mama na ta yi sannan ta matso inda na ke,numfashi na yana fita da ƙer ta kalleni fuskarta sam babu annuri ta ce"khairat kin bani mamaki kuma kin bani kunya,haƙiƙa ban taɓa zaton haka daga gare ki ba,yaushe ki ka lalace?yaushe ki ka zubar da tarbiyyar dana baki?haƙiƙa khairat na ji matuƙar kunyar kaina da kuma mutanen da suka yarda da ke ɗari bisa ɗari". ta juya min baya ta ce"khairat ki faɗa min wanda ya yi miki ciki har ki ka yi ɓari?idan har ki ka ƙi faɗamin to Allah ya i'sa tsakanina da ke,kuma na cire ki daga cikin ƴaƴa na".sai ta juyo tana fuskanta na. Tausayin khairat ya cika zuciyar zulaiha,uwa da ɗa kenan amman a fuskarta rashin imani tsantsana ta nuna wa ƴar ta don ta faɗa mata gaskiyar abinda ya faru. Bakina yana rawa na ce"haƙiƙa mama wannan rana har tafi ranar mutuwa ta zafi,bantaɓa tunanin ko da a mafarki zan tsinci wannan rayuwar ba,ban sani ba ban san kuma me ya faru dani ba?ni dai na tashi na ji ni a baƙon yana yi,ban taɓa zama na minti goma dana miji awaje ɗaya ba,mama kin sani koda saurayin ma na yi to ya zamar min dole in faɗa miki,don ban saba ɓoye miki komai ba,tun yarinta na har zuwa yanzu,wallahi mama ban taɓs kusantar wani ɗa najimi ba?me zan gaya miki yanzu ki tabbatar da hakan?". da sauri mama ta juyo ta ce"khairat tashi in duba ki"?. duk da halin da na ke ciki sai da na shiga ɗimuwa sosai akan hakan,duk da mahaifiya ta ce amman da tsananin kunya,tunda dai yanzu ni ba ƙaramar yarinya ba ce". tsawa ta bugamin da ƙarfi,da sauri na tashi daman rigar bacci ce ajikina na ciresa baki ɗaya. Kallona sosai take da mamaki,babu wata hanya ko kaɗan daya nuna khairat ta taɓa kusantar ɗa namiji,grady a matsayin budurwa taje cikakkiya. Shiru mama Ta yi ta kasa ce wa komai,ta tafi tunanin wani abu daya shuɗe,tabbas jiya taga hajiya iklima na barbaɗa abu a ƙofar ɗakin khairat amman bata san kome ye ba,da sauri ta fita waje kai tsaye ɗakin hajiya iklima ta shiga,zuciyarta har wani bugawa take,lallai hajiya iklima ta taɓo ruwan dafa kanta,don yau za ta nuna mata ko da yaya kurna tafi magarya daɗi. Sosai ta tsorata da ganin zulaiha,tos wani ɗan ƙwalba da ta ɗakko ya fashe,tsoro sosai ya fito daga idanuwan hajiya iklima. Bakinta na rawa ta ce"zu. .zu. .zulaiha ms ki ka shigomin ɗaki"?.bata i'da gamawa ba zulaiha ta shaƙo wuyanta sosai har dai da ta kaita bango tana kakkarin aman wahala,cikin ɓacin rai da baƙin ciki zulaiha ta ce"kina tunanin Allah zai barki da abinda ki ka yiwa jinina?yarinya bata ji ba,bata gani ba

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87