Chapter 82
Chapter 82
ke ranar da khairat ɗin tazo ranar bikin ƴar gidan Baba Hamza ne kuma an tafi dinner shiyasa ba kowa ne ya san zancen ba,Sai Hajiya kaka uwar ƴan kunne duk da ta tsufa tsam kunnenta na nan daram don ko gulmarta ka yi to babu abinda baza taji ba. Babu wanda ya kirani ya ce Bilal bai da lafiya hatta mama na bata faɗamin ba,kullum dai idan na buga mata waya zance ta bani su Haidar muyi waya amman irfan sam bai ko kallon inda wayar take,idan ma aka ce masa mamansa ta bugo sai ya ce waishi ba mamansa ba ce. Ranar dana ji hakan da kunnena ranar na yi kuka sosai,tambayar duniya Shahid ya tambayeni abinda ke faruwa na ce masa babu komai.haka dai ya sakani agaba har na samu naci abinci.sosai Shahid ke kula dani babu abinda na nema na rasa na rayuwa,ko tagumi idan shahid yaga na yi to hankalinsa yanzu zai tashi. Ammi mahaifiyarsa yanzu ita ke yini a sashe na,saboda taga duk yanda na rame naƙi sakin jiki na kamar da,shima Shahid ɗin yanzu idan ya tafi aiki mai makon da baya dawowa sai maghrib amman yanzu la'asar na yi zai dawo. Jikin Bilal ya yi sauƙi yanzu,sai dai kowa ya kallesa yasan yana cikin wani hali,ga yaransa wanda yanzu sun koyi wata ƙiwa indai ba shiba basu fiya yadda da kowa ba.hatta abin yanzu yana san ya shafi aikinsa.don daga wajen aikin ma sun aiko masa da saƙo akan yana wasa da aikinsa,uzuri ya bayar akan ce wa bai da lafiya.ai kuwa ba tare da ya watstsake ba ya koma bakin aikinsa. Sai dai fa ƙwana biyu da komawar tasa jikinsa ya ƙara dawowa,yana daurewa don bai san kowa yasan halin da ya ke ciki,ga ciwo na nuƙurƙusarsa amman yana daurewa. ********* ayanzu mun gama makaranta wacce muka yi shekara fin biyar muna yi,don kowa yasan aikin Lauya yadda ya ke aƙwai cinye shekaru.ya yi dai dai da kasancewa ta shekara ishirin da huɗu a duniya.abin kuɗi sai gashi shahid ya fara cuku cukun nemomin aiki,Allah ya taimake ni aka ɗaukeni a babbar kotu amman bazan fara aiki ba har sai na haihu. Tun safe ciwo ke nuƙur ƙusa ta amman naƙi in bar kowa ya gane halin da na ke ciki,har dai Ammi ta gano ai kuwa sai ga ciwo daga kaɗan ya zama babba,muka garzaya asibiti,A ruɗe Shahid ya taho asibitin hankalinsa tashe. Dai dai wannan lokacinne kuma aka kawo Bilal shima ranga-ranga babu lafiya,kowa hankalinsa atashe sai kuka ake. 07068606171 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨 _*Miss green ce*_🤙🏿 [23/09, 16:31] Miss Green🍀: 1001. . . .1002 tashin hankali sai ya zama guda biyu don nima wannan haihuwar har tafi tasu Ƴan huƊu,don har an fara fitar da rai dani,shi kuwa shahid nema ya ke ya fita daga cikin hayyacinsa,ba don ma ammi ba da ba'asan abinda zai faru ba,har an fara haƊa kayan aiki na sunkutu Ƴa ta mace kyakkyawa me tsananin kama da mahaifinta,kyakkyawa ce sosai har tafi mahaifinta ma kyau. hajiya kaka ma tazo ta yimin barka sai dai fuskarta atamke tsaf,haka ma duk wanda zai zo duba ni sai inga fuskarsa a haƊe sosai na rasa gane kan kowa,kai hatta yaya Aliyu dasu mamana kowa sai inga fuskarsa tamau,abin ya dameni sosai,na rasa wanda zan tambaya gashi nima ban gama warwarewa ba don nasha wuya sosai. Shahid ne ya shigo shima duk jikinsa ya yi sanyi,yana shigowa ya kalleni sannan ya ce"khairat ya jikin"?.sosai maganarsa ta girgizani don bai taƁa kirana da khairat ba sai dai hayatee,na kallesa sosai Na ce"hubby yau kuma sunana ka ke faƊa"?.na faƊi hakan ina me kallonsa kamar ya yimin laifi. sunkuyar da kansa ya yi ya Ƙaraso inda jaririyar take ya saka hannu ya Ɗauketa ya rungume ta a Ƙirjinsa hawaye masu zafi suka zubo masa a kuncinsa,a zuciyarsa ya ce Allah sarko Ƴata ashe bazan rayu da mahaifiyarki ba?ashe bazanyi rayuwa da ita me tsayi ba?yanzu me na aikata haka?shin nima ina tunanin zan iya wani auren idan na rabu da khairat?shin ya rayuwar Ƴarsa yaya za ta kasance alhali babu me kula da ita sai mahaifiyarsa zai Ɗorawa wahala. jin kukan da khairat ta fashe dashi ne ya saka ya juyo da sauri ya ce"khairat lafiya ki ke kuka me aka yi miki?".ya faƊi hakan yana matsowa har ya riƘe hannuna wanda na Ɗora aka ina gunxuma ihu kamar wani ya dake ni. da sauri na yar da hannunsa gefe na ce"haba na gaji wallahi,yaya kuke so inyi ne?kO cikakkiyar awa Ɗaya banyi da haihuwa ba,amman kowa ya shigo sai inga duk hankalinsa atashe kuma ya Ɗauremin fuska?Haba wannan wani irin rashin tausayi ne?ku faƊamin mana idan wani abune ya faru?" da sauri ya koma gefe ya ce"khairat babu komai fa haka dai ke ki ka gani,amman babu komai bari inje wajen Ammi sai mu taho tare taje duba wanine ba shida lafiya".yana faƊar hakan ya fita da mugun saurinsa,tuni naji zuciyata ta tsinke na shiga wani irin kuka wanda na kasa gane kansa,na kalli Ƴata wacce kebta shan hannu alamar tana neman abincinta,da ta gaji da shan hannun sai ta fara kuka sosai,nima uwarta ta kuka nake sosai kamar wacce aka aiko mata iyayenta sun mutu duka. ana cikin wannan halin ne anty hakisa tazo,da sauri ta Ƙaraso cikin Ɗakin tana ce wa"subhanalillahi khairat me ya faru haka?ga yarinya na ta kuka alamar tana neman mama kuka kinƘi bata?".ta saka hannunta cikin gadon babyn ta Ɗakko ta tana Ɗan girgiza ta,ta zauna ta ajjemin ita akan cinya ta tace"khairat yi haƙuri ku bata tasha kinji?koma menene ya faru bai kamata ki yiwa Ƴarki ta cikinki haka ba,ki bata tasha sannan sai muyi magana". Sai shashsheƘar kuka ba ke harda majina ta kalleni kawai,tana jin tausayina har cikin ranta,a hankali na ke shayar da ita jaririyar ta riƘe babban Ɗan yatsana tana kuma kallon cikin idona sosai,ina kallon yarinyar sai naji zuciyata ta fara sanyi tabbas ƳaƳa rahama ne arayuwa,Allah ubangiji ya bawa duk wanda basu haihu ba,ya basu masu albarka wanda za'ayi alfahari dasu aduniya da lahira. sai da tasha ta Ƙoshi sosai sannan anty halisa ta amsheta ta sakata a kafaƊarta har ta yi gyatsa,sannan ta kalleni sosai ta fara yimin nasiha sannan ta ce"khairat yanzu fa daga dubo baban Ƴan huƊu na ke".da sauri na kalleta sannan na ce"me ya same shi kuma?daman ba shida lafiya ne?". Na faƊi hakan zuciyata na bugawa sosai,ganin na shiga wani hali ne yasa ta gane ce wa ban san ba shida lafiya ba ta ce"khairat come down,kinga yanzu kin haihu fa kina
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87