Skip to content

Chapter 45

Chapter 45

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,294 words 0 views Progress saved
Download Book

na gani atsaye ne yasa ni waro idanuwa na waje.. .✍🏿 07068606171 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss green ce*_🤙🏿 [23/09, 16:22] Miss Green🍀: *_🪺ABIN CIKIN ƘWAI🪺_* 📃LITTAFI NA 2 UMMU MAHER(MISS GREEN🍀) Wattpad user name Rabiatu333 Arewabooks rabiattu0444 *Matso kiji👂🏻* Ki dinga tsarki da kanimfari musamman ma idan bayan kin gama al'ada yana cuko da gaban mace sosai sannan ya matseki ciki da kuma wajenki. 49. . . .50 . .. ."Yaya Salim kaine?".Na faɗi hakan ina matsa masa,na gaishesa ya ce"ai ba ni kaɗai bane ma dasu mama ne harda Hajiya kaka".buɗe idanuwa na yi murna ta isheni ƴar damuwata naji ta kau. Na rungume Hajiya kaka ina ce wa"i miss u so much my Hajiya kaka".itama rungumeni ta yi tana tsokana ta,wai tunda na yi aure ko kiranta awaya banyi ba. Sosai mukasha hira ananne ma ake hirar zancen rashin lafiyar Rashida,na ce"Hajiya kaka inason zuwa in duba ta". "A'ah ƴar nan ba'a haka daga aure sai kuma ki fara fita?yanzu ma daga gidan mero muke,itama ta saka min kuka wai sai ta biyoni munzo nan,to shine fa naja mata kunne akan baza ta bini ba,sokon mijinta gashinan gabanki Salim ko kallon ƙurar zancenmu baiyi ba,daga baya ma ya fito waje shine na biyosa na ce sai ya kawoni gidanki,amman gidan Rashida muka fara zuwa tunda yafi kusa da gida." dariya na yi na ce"Allah sarki Mero ai ita ga ta ga gida ma babu nisa tunda bayan gidanmu ne,Amman hajiya kaka ya ki ka jikin Rashidan?". "Ah wallahi jikinta da sauƙi sosai,ai da ya ke ma an sallamota da wuri,ita kuma haka Allah ya tsara mata to ubangiji Allah ya bada na aike".dukkanmu da amin muka amsa aka cigaba da hira,Hajiya kakanta leƙa taga garar da aka kawomin ta ce"ah gara wallahi ta yi,wannan dai idan ba rabawa biyu zaki yi ki bawa waccen figigiyar ba ai har sai ayi shekara ma".ta faɗi haka tana dariya. Har ƙofar sashena na rakosu mama ta ce"to khairat muyi banƙwana gobe insha Allah zan wuce gida,Allah ya bada zaman lafiya".na amsa da amin hawaye na fitowa daga cikin idaniya ta. "Au yay naji ɗan jakar uba,au yanzu don Allah Bilalu kana cikin gidannan?Amman har muka gama zaman daɓaro baka shigo ba?saboda kana wajen wannan ƙwailar matar taka?a to ahir ɗinka idan aka shiga haƙƙin jikata,don ina jiye maka tashi da ƙonannan jiki". Ta faɗi hakan tana harar jidda wacce ko kunyar idon hajiya kaka bai hanata ɗafewa jikin Yaya Bilal ba,shine ma yaji kunya ya ture ta gefe ɗaya ya durƙusa har ƙasa yana gaidasu mama,Hajiya kaka ta ce"ah to ni dai na faɗa maka,ka biyewa mace ka faɗa wuta tsundum wallahi,kuma duk ihunka Ruƙayya da Abdu baza su fito da kai ba".Ta daɗi hakan tana yin gaba abinta. Bayansu Hajiya kaka sun tafi da daddare na yi wanka na mai kyau da sabulun da mama ta haɗomin na gyaran fata,na ɗakko qur'ani ina karantawa sai naji zuciyata kamar an wanke min ita fes. Na ɗakko wayata na buga wayar Rashida naci sa'a ta ɗaga,da sauri ta ce"ah lallai amaryar yayana kin manta dani ko?da tuni yanzu ina barzahu,amman ko kizo ki dubani ko?". Duk alokaci ɗaya ta sakomin waɗannan tambayoyin na ce"ayya Rashida kinfi ƙarfin haka awaje na,nima shekaran jiya da maryam tazo shine take faɗamin abinda ya faru har kuka sai da na yi wallahi". Nan dai muka cigaba da hirarmu ta aminai,ta ce"kin buga number maryam kuwa".? Na bata amsa"eh na buga ita ma akashe shiyasa duk naji kamar na rabu da wani abu mai muhimmanci arayuwata,me ya faru da wayar na ta"?. "Hmm kinsan fa washe garin ranar da aka kaita sukayi faɗa da Khadija shine ta fasa mata wayar,bata tsaya anan ba ta shiga ɓangarenta duk ta rugurguza kayan wuta masu amfani da kayan kitchen ɗinta,Hmm kedai bari khairat jiya dai Khadija agida ta wuni,don yaya Aliyu ce wa yayi ta koma ta gyara tarbiyyarta sannan ta dawo,ina faɗa miki da ya ke yaya Aliyu ɗan duniya ne,kayan daya canjawa khadija na kayan wuta da kuma kayan kitchen su ya ɗiba ya bawa maryam".tana kaiwa nan ta rintsire da dariya. Nima dariyar na ke na ce"hmm Rashida kema fa ki danki da makamanciyar irin wannan matsalar,ki daina dariya". "Hmm a fahimtarki hakanne,amman a fahim tana ba haka bane,da zaki yi ƙwana ɗaya agidana da sai kinci dariya har cikinki ya ƙulle,abinda baki sani ba shine Yaya Aliyu dai da ki ka sani mijina,agaban Nadiya yana nuna kamar yana sonta ne ko kuma tsoronta,amman wallahi ko ɗaya babu haka,ahi dai yana yi ne saboda fita hakkinta,kuma wallahi son da Nadiya ke yimai ya fi nasa yawa nesa ba kusa ba,don haka ki daina zaton ko aƙwai wani abu,in ma asiri zasuyi to ni na fisu har awajen Allah,don ni zuciyata awanke take fes,babu wani abu acikinta kinga kuwa ƙarshe kansu zai koma". Gyaɗa kai na yi kawai don ni a fahimtar tawa ko wani abin suka yiwa Rashida,don tsaf nasan Mama iklima cikinta da wajenta,basu da tsoron Allah ko ɗaya,su dai kansu kawai suka sani da kuma ƴaƴansu. **** Wayar dana ajje ce ta fara ruri,na ɗauka na saka a kunne ba tare dana duba ba,saboda wanke salad ɗin dana ke a kitchen,muryar Zuhra ce ta karaɗe min kunnuwa,ƙawata ce a Bayero university muka haɗu,wajen zamanmu ɗaya da kuma wata Zainab,ganin suma duk masu hankaline yasa na yi ƙawance dasu. "Ah lallai ya yi amarya agidanta,kina more amarci wallahi,kai muma dai Allah ya nuna mana ranar aurenmu,amman kash nasan Dadyna bazai taɓa aurar dani yanzu ba,kin san burinsa akaina wai har sai na cika lauya sannan zai aurar dani,wallahi abin nan yana damuna,gashi kuma ni ina son auren". Ɗan murmushi kawai na yi,tausayin Zuhra duk ya cika ni,Allah sarki ita tana ganin kamar duk wata mace idan ta yi aure shikkenan ba tada wata damuwa?ko kuma kawai morewarta take?ita dai gata nan kamar wata sunduƙi agida,yau sati ɗaya cif amman babu ita babu miji,naji wani abu kamar mashi ya daki ƙirjina,saboda jin tashin motar Yaya Bilal,na ɗan zuge labulen kitchen ɗin ina hangosa,shi da ƴar ganan goshin sane wato Jidda. "Kina jina kuwa amarsu"?. Da sauri na dawo cikin hayyaci na sannan na ce"zuhra abinda ba keso dake,ki ƙara haƙuri komai lokaci ne,haka zali ka shima aure lokaci ne dashi,don haka ki cigaba da addu'ar Allah dai ya baki miji nagari,ba auren ba samun miji nagari ayanzu shine ya yi ƙaranci acikin al'umma." "Ba komai khairat ina jin daɗin shawararki gare ni,Allah ya baku zaman lafiya tare da danƙwan soyayya me ƙarfi musamman ma shi mijin".dariya kawai na yi

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87