Chapter 13
Chapter 13
idanuwansu,don sun san kakarsu aƙwai tonon asiri suka haɗa baki wajen ce wa"hajiya kaka ina wuni".zaro idanu kaka ta yi sannan ta ce"oh ni ina ganin rashin hankali a gidannan ke Nadiya don ubanki sadakar yalla ce ta raɗamin wannan sunan Hajiya?ke kuma imani fulanin daji ce ta raɗamin ko kuwa?".da sauri suka haɗa idanu don mamakin zagin da kaka ta yi musu,ganin mamakin zagin da ta yi musu suke ta ce"to wannan kallon da kuke min munafukai nima ƙwaƙwuleni zakuyi?kamar yadda kuka yi wa ƴar uwarku khairat?to wallahi ahir ɗinku don ni na fi ƙarfin maitarku,kuma bari Malik ɗin ya dawo duk sai an kori masu aikin gidannan ku koma masu yi mana aiki,tunda rashin aikin yi ne yasa kuke saƙule ƴaƴan mutane". *GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE* 1, *MU GANI A ƘASA..🔥* _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚* _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5_ *AUREN WATA TARA👩❤️👨* _Miss Hajo_ Guda ɗaya N300 Guda biyu N500 Guda uku N600 Guda huɗu N700 Guda biyar 1k *ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇* Fatima Rabiu Sunusi 0037219728 StanbicIBTC Bank. Shaidar biya tanan 👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 ...........🥚👩❤️👨💥🌎.... *ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇 +227 84 50 64 76 *MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO* *miss green ce* [23/09, 16:17] Miss Green🍀: _*🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!*_ 📃Littafi na 1 By🪶 *Ummu maher(Miss green)🍏* *GAWURTATTU 5* ----------------------- *Wattpad user name* https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333 ------------------------- *Arewa book user name* https://arewabooks.com/u/rabiattu0444 ---------------------- masu buƙatar talla 2k Ne,zamu dinga Ɗora muku a dukkanin shafukanmu a kowani social media don samun costumer cikin sauƘi. *Sirrinmu* mata mu kasance masu tsafta,ladabi,biyayya,haƙuri,juriya.domin shi namiji ba ta ƙarfi ake samunsa ta lallami da lumana.Allah yasa mu dace amin. ---------------------------------- 15⬜16 . . . .Ina ƙwance duk abin duniya ya isheni tun jiya Yaya Bilal ya i'so gidan amman tsoron fita na ke don bana son abinda zai janyo mana tashin hankali dashi don matuƙar yazo to fa tabbas sai an ɗebi ƴan kallo,shi yasa ma na rufawa kaina asiri na yi zamana a ɗakin,ina jin tafiyar mama ta taho na yi saurin lulluɓa da bargon don bana son ta aikeni gun kaka don yau ita ce da girki. "Khairat!Khairat!! Mama ta fara tashi na, na buɗe idanuwa na gaisheta sannan ta ce"kalli garin mana rana ta fito sosai amman kina cikin ɗaki kina bacci?yanxu Khairat kin lalace da bacci wallahi da tun kafin in tashi zaki shiga kitchen ki girkamin abinci?amman yanzu sai na tashi da kaina na yi sannan kuma ki ƙi tashi da wuri?ni dai gidan miji na ke jiye miki don wannan salon da ki ka ɗauka ba mai ɓullewa ba ne?yanzu ki tashi ki kaiwa kaka abinci don ya zama ready".tana faɗar hakan ta fita nasan halin mama ba ta san jira don haka na tashi da sauri na shiga ba yi na yi brush sannan na wanke fuskata,daman na yi sallah tun asuba gabana yana ta faɗuwa don bana son na haɗu da Yaya B,don nasan ko ban kulasa ba dole ne na yi laifi,don idan na gaishesa ma ba ya amsawa ko kallon inuwa ta bayayi,ni na rasa wannan wacce irin tsana ce haka?. ina fitowa farlon na iske Amira ƙanwar su iman tana homework,da murmushinta ta juyo ta ce"la Anty daman ke na ke jira ki tashi wallahi".murmushi na yi mata sannan na ce"to little sis me kuma ya faru?".shagwaɓe fuska ta yi sannan ta ce"assignment aka bani kuma wallahi na kasa yi guda 3,ne na yi ɗaya sauran ban iya ba,kuma na bawa su Anty iman sunce wai baza su iya ba aikin na da wahala"?. "To Meeraty bari dai yanzu in kaiwa Kaka abinci in dawo sai in yi miki kinji?"da to ta amsamin ni kuma na wuce don kai aiken kaka.inason Amira don kaf cikin ƴan uwanta ta fita zakka ita kaɗai ce take sona acikinsu sauran duk sunbi layin iyayensu mata. Tun daga ne sa na ke jiyo ƙamshin turarensa gabana yana ta faɗuwa na tsaya cak sai da na karanta addu'ar tsoron mutune sannan na yi hanyar. Ƙamewa na yi kawai ina kallonsa yadda ya haɗu cikin wata farar jallabiya farar fatarsa sai shining take kamar ta mata,sak balarabe haka ya fito,shima tun daga nesa ya hango ta yaga ta kafesa da idanuwa azuciyarsa ya ce kai wannan yarinyar kamar mayya take wallahi ƙwata ƙwata ba tada kamun kai irin na mata,shi fa arayuwara na fi son mace mai kamun kai,tun ba yau ba yasan Khairat na sonshi irin son nan na ƙarshe,shi kuma tun daga ranar yaji ya yi wani irin muguwar tsanarta wadda ko ganinta ya yi sai yaji gabansa yana faɗuwa ainun,ga ta wata mummuna da ita don kaf gidan kamar ita Aka ɗorawa muni. Har ya wuce ta kusa dani ban daina kallonsa ba,ya yi tsaki ya wuce shima sashen kaka ɗin ya shiga,cikin faɗuwar gaba nabi bayansa muka shiga atare. Kaka tana sharar ɗakinta ta ce"kai!"cikin tsawa duk sai da muka tsorata ta ce"duk ku tsaya anan shara na ke ko mijina yasan idan ina shara tsayawa ake har sai na gama don bana son ju shigarmin da datti". "to in koma kenan ko?"ya ce wa Hajiya kaka kawai sai na ji ta ce"kai soja ni na i'sa in ce ka koma?jiya ma fa haka ka aikomin da abin arziƙi lodi lodi,yauma ka ga kayan shayin da ka lodomin shi na haɗa da safen nan nasha abina,kafin a kawomin makararren abincin da aka saba kawomin".ta kalli abincin hannuna ta yi wani gyatsine. Shiga ɗakin ya yi ni kuma naja na tsaya har ta gama sharar ta sai kuwa ta ce"to dogariya ke ko kunya ma baki ji ba?ina ta aiki ko ki taya ni?kema kin fara ɗakko hali irin na su Nadiya ko?to kuwa wallahi wahala zakisha,agidan miji don ni har na fara tausayin jikokina da aka haɗasu dasu Nadiya don babu abinda suka iya sai rashin arziƙi". ni dai bance mata ƙala ba na wuce zuwa ɗakin cikin nutsuwa na ajje abincin sannan na gaisheta,na wuce ɗakinta don na tuno duk ranar asabar ni ke mata gyaran kayan cikun sif ɗinta. Ina jin kaka bayan tafiya ta ce"Allah sarki Abin cikin ƙwai yarinya kirki yanzu haka fa gyaran ɗakin za ta yimin abinda kaf jikokina basa yin hakan,Allah ya baki miji nagari yarinya ga haƙuri ga kunya".ta faɗi haka tana buɗe abincin dana kawo mata. Azuciyarsa ya ce lallai bakisan yarinya mai kunya ba abinda idan taga maza kamar za ta cinyeshi take,ita wannan maitar ta ta ma har tafi tasu Nadiya ma.yana cikin wannsn tunanin yaji kaka ta fashe da kuka ta ce"ikon Allah yau kuma abincin inyamurai akayi agidan,ka duba fa ka gani Bilal?wai ruwan shayine da wannan soyayyiyar ayabar,ayabar da tunda na ke ban taɓa cinta ba ko da na yi zaman cikin yare,shine ni za'a kawomin ni wallahi bazan ci ba".ta faɗi hakan tana ajje abincin a gefe. Rarrashin kaka ya dingayi har ta ɗan ɗauki plaintain ɗin ta fara yaga kamar kashi,abinda aka kawo mata cikin flask sai ga
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87